NOTES: DO NOT CHANGE THIS FILE OR PROGRAM COULD BREAK DOWN @Hausa:Unknown Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. This Holy Qur'an was downloaded from the Internet site: http://www.qurandatabase.org/, then (hard)checked and converted into unicode text file, for use within Islam software, by the author of Islam software: Samir Alicehajic, http://www.agnatemoslem.net/ @AL FAATIHAH Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [1.1] Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [1.2] Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu; [1.3] Mai rahama, Mai jin ƙai; [1.4] Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako. [1.5] Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa. [1.6] Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya. [1.7] Hanyar waɗanda Ka yi wa ni´ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba. @AL BAQARAH Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [2.1] A. L̃. M̃. [2.2] Wãncan ne Littãfi, bãbu shakka a cikinsa, shiriya ne ga mãsu taƙawa.(1) [2.3] Waɗanda suke yin ĩmãni game da gaibi, kuma suna tsayar da salla, kuma daga abin da Muka azurta su suna ciyarwa. [2.4] Kuma waɗanda suke yin ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar daga gabãninka, kuma game da Lãhira suna yin yaƙĩni. [2.5] Waɗannan suna kan shiriya, daga Ubangjinsu, kuma waɗannan su ne mãsu cin nasara. [2.6] Lalle ne waɗanda suka kãfirta(1) daidai ne a kansu, shin kã yi musu gargaɗi kõ ba ka yi musu gargaɗi ba, ba zã su yi ĩmãni ba. [2.7] Allah Ya sa hãtimi a kan zukãtansu, da a kan jinsu, kuma a Kan ganin su akwai wata yãna; kuma suna da wata azãba mai girma. [2.8] Kuma akwai daga mutãne wanda(2) yake cewa: "Mun yi imani da Allah kuma da Yinin Lãhira." Alhãli kuwa su ba muminai ba ne. [2.9] Suna yaudarayya da Allah da waɗanda suka yi ĩmãni, alhãli bã su yaudarar kõwa fãce kansu, kuma bã su sakankancħwa! [2.10] A cikin zukãtansu akwai wata cũta. Sai Allah Ya ƙãramusu wata cũta, kuma suna da azãba mai raɗaɗi sabõda abin da suka kasance suna yi na ƙarya. [2.11] Kuma idan aka ce musu: "Kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa," sukan ce: "Mũ mãsu kyautatawa kawai ne!" [2.12] To, lalle ne su, sũne mãsu ɓarna, kuma amma bã su sansancewa. [2.13] Kuma idan aka ce musu: "ku yi ĩmãni kamar yadda mutãne suka yi ĩmãni," sukan ce: "Zã mu yi ĩmãni ne kamar yadda wãwãye suka yi ĩmãni?" To, lalle ne su, sũ ne wãwãye, kuma amma bã su sani. [2.14] Kuma idan sun haɗu da waɗanda suka yi ĩmãni,sukan ce: "Mun yi ĩmãni. "Kuma idan sun wõfinta zuwa ga shaiɗãnunsu,(3) sukan ce: "Lalle ne muna tãre da ku: Mu mãsu izgili, kawai ne." [2.15] Allah Yana yin izgili(4) gare su kuma Yana taimakon su a cikin ɓatarsu, suna ɗimuwa. [2.16] Waɗannan su ne waɗanda suka sayi ɓata da shiriya, sai fataucinsu bai yi rĩba ba, kuma ba su kasance masu shiryuwa ba. [2.17] Misãlinsu(1) shĩ ne kamar misãlin wanda ya hũra wuta, to, a lõkacin da ta haskake abin da yake għfensa (na abin tsõro), Allah Ya tafi da haskensu, kuma Ya bar su a cikin duffai, bã su gani. [2.18] Kurãme, bħbãye, makãfi, sabõda haka bã su kõmõwa. [2.19] Ko kuwa kamar girgije mai zuba(2) daga sama, a cikinsa akwai duffai da tsãwa da walƙiya: suna sanyãwar yãtsunsu a cikin kunnuwansu dãga tsãwarwakin, dõmin tsõron mutuwa. Kuma Allah Mai kħwayewa ne gã kãfirai! [2.20] Walƙiyar tana yin kusa ta fizge gannansu, ko da yaushe ta haskakã musu, sai su yi tafiya a cikinta, kuma idan ta yi duhu a kansu, sai su yi tsaye. Kuma dã Allah Yã so, sai Ya tafi da jinsu da gannansu. Lalle ne Allah a kan dukan kõme Mai ĩkon yi ne. [2.21] Yã ku mutãne! Ku bauta(3) wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku ! [2.22] Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma sama gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Ya fitar da abinci daga ´ya´yan itãce game da shi, sabõda ku. Sabõda haka kada ku sanya wa Allah wasu kĩshiyõyi, alhãli kuwa kuna sane. [2.23] Kuma idan kun kasance a cikin shakka daga abin da Muka sassaukar ga Bãwanmu, to, ku zõ da sũra guda daga misalinsa (Alƙur´ãni). Kuma ku kirãwo shaidunku (4) baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya. [2.24] To, idan ba ku aikata (kãwo sura) ba, to, bã zã ku aikata ba, sabõda haka, ku ji tsoron wuta, wadda makãmashinta mutãne da duwãtsu ne, an yi tattalinta dõmin kãfirai. [2.25] Kuma ka bãyar da bishãra ga waɗanda suka yi ĩmãni. kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, cħwa lallene, suna da gidãjen Aljanna, ƙõramu na gudãna daga ƙarƙashinsu. Ko da yaushe aka azurta su da abinci daga wasu ´ya´yan itãce daga gare su,(1) sai su ce: "Wannan shi ne aka azurta mu da shi daga gabãnin haka," Kuma a je musu da shi yana mai kama da juna, Kuma sunã da, a cikin su, mãtan aure mãsu tsarki, kuma su, cikin su madawwama ne. [2.26] Lalle ne, Allah bã Ya jin kunyar Ya bayyana wani misãli, kõwane iri ne, sauro da abin da yake bisa gare shi. To, amma waɗanda suka yi ĩmãni, sai su san cewa lalle shi ne gaskiya daga Ubangijin su, kuma amma waɗanda suka kãfirta, sai su ce: "Mħne ne Allah Ya yi nufi da wannan(2) ya zama misãli?" na ɓatar da wasu mãsu yawa da shi, kuma Yana shiryar da wasu mãsu yawa da shi, kuma bã Ya ɓatarwa da shi fãce fasiƙai. [2.27] Waɗanda suke warware alƙawarin Allah daga bãyan ƙulla shi, kuma su yanke abin da Allah Ya yi umurni da shi a sãdar, kuma suna ɓarna a cikin ƙasa, waɗannan sũ ne mãsu hasãra. [2.28] Yaya kuke kãfirta da Allah, alhãli kuwa kun kasance matattu sa´an nan Ya rãyar da ku, sa´nnan kuma Ya matar da ku, sa´an nan kuma Ya rãya ku, sa´an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku? [2.29] Shi ne Wanda Ya halitta muku abin da ke a cikin ƙasa gaba ɗaya, sa´an nan kuma Ya daidaita(3) zuwa sama, sa´an nan Ya aikata su sammai bakwai. Kuma Shi ga dukan kõmai Masani ne. [2.30] Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya ce ga malã´iku: "Lalle ne, Ni Mai sanya wani halĩfa ne a cikin ƙasa," suka ce: "Ashe, zã Ka sanya a cikinta, wanda zai yi ɓarna a cikinta, kuma ya zubar da jinainai alhali kuwa mu, muna yi maka tasbihi game da gõde maka, kuma(1) muna tsarkakewa gareka" Ya ce: "Lalle ne, Ni Na san abin da ba ku sani ba." [2.31] Kuma Ya sanar da Ãdam sũnãye dukansu, sa´an nan kuma ya gitta su a kan malã´iku, sa´an nan Ya ce: "Ku gaya mini sũnayen waɗannan, idan kun kasance mãsu gaskiya." [2.32] Suka ce: "Tsarki ya tabbata a gare Ka! Bãbu sani a gare mu, face abin da Ka sanar da mu, lalle ne Kai, Kai ne Masani, Mai hikima." [2.33] Ya ce: "Yã Ãdam! Ka gaya musu sũnãyensu." To, a lokacin da ya gaya musu sũnãyensu, (Allah) Ya ce: "Ashe, ban ce muku(2) ba, lalle Ni, Inã sane da gaibin sammai da ƙasa, kuma (Inã sane da ) abin da kuke bayyanawa da abin da kuka kasance kuna ɓõyewa?" [2.34] Kuma a lõkacin da Muka ce ga malã´iku: "Ku yi sujada ga Ãdam," Sai suka yi sujada, fãce Ibilĩsa ya ƙi, kuma ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kãfirai. [2.35] Kuma muka ce: "Ya Ãdam! Ka zauna kai da matarka a gidan Aljanna, kuma ku ci daga gare ta, bisa wadãta, inda kuke so, kuma kada ku kusanci wannan itãciyar, har ku kasance daga azzãlumai." [2.36] Sai Shaiɗan ya talãlãɓantar da su ga barinta, sai ya fitar da su daga abin da suka kasance a cikinsa. Kuma muka ce: "Sãshenku nã maƙiyi ga sãshe, kuma kuna da a cikin ƙasa matabbata da jin dãɗi zuwa ga wani lõkaci." [2.37] Sai Ãdam ya karɓi wasu kalmõmi daga Ubangjjinsa, sabõda haka ya karɓi tũba a kansa. Lalle ne Shi, Shĩ ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai. [2.38] Muka ce: "Ku sauka daga gare ta gabã ɗaya. To, imma lalle shiriya ta je muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiriya ta to, bãbu tsõro a kansu, kuma bã su yin baƙin ciki." [2.39] "Kuma waɗanda suka kãfirta, kuma suka ƙaryata game da ãyõyinMu, waɗannan sũ ne abõkan Wuta; sũ a cikinta madawwama ne." [2.40] Yã Banĩ Isrã´Ĩla(1) ! Ku tuna ni´imãTa wadda Na ni´imta a kanku, kuma ku cika alƙawariNa, In cika muku da alƙawarinku. kuma Ni, ku ji tsõro Na. [2.41] Kuma, ku yi ĩmãni da abin da na saukar, yana, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku, kuma kada ku kasance farkon kãfiri game da shi. Kuma kada ku sayi ´yan kuɗi kaɗan da ãyõyiNa. Kuma ku ji tsõrõNa, Nĩ kaɗai. [2.42] Kuma kada ku lulluɓe gaskiya da ƙarya, kuma ku ɓõye gaskiya, alhãli kuwa kuna sane. [2.43] Kuma ku tsayar da salla; kuma ku bãyar da zakka; kuma ku yi rukũ´i tãre da mãsu yin rukũ´i. [2.44] Shin, kuna umurnin mutãne da alhħri, kuma ku manta da kanku alhãli kuwa kuna karatun littãfi? Shin, bãzã ku hankalta ba? [2.45] Kuma ku nħmi taimako da yin haƙuri, da salla. Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa, mai girma ce fãce fa a kan mãsu tsõron Allah. [2.46] Waɗanda suka tabbata cħwa lalle ne su mãsu haɗuwa ne da Ubangijinsu, kuma lalle ne sũ zuwa gare Shi mãsu kõmãwa ne. [2.47] Yã banĩ Isrã´ĩla! Ku tuna ni´imaTa, wadda Na ni´imta a kanku, kuma lalle ne Ni, na fĩfĩta ku a kan tãlikai. [2.48] Kuma ku ji tsoron wani yini, (a cikinsa) rai bã ya wadãtar da wani rai da kõme, kuma ba a karɓar cetõ daga gareshi, kuma ba a karɓar fansa daga gare shi, kuma bã su zama ana taimakon su ba. [2.49] Kuma a lõkacin da muka tsĩrar da ku daga mutãnen Fir´auna, su na taya muku muguntar azãba, su na yayyanke ɗiyanku maza su na rãyar da mãtanku. Kuma a cikin wancan akwai jarabawa mai girma daga Ubangijinku. [2.50] Kuma a lõkacin da Muka raba tħku sabõda ku, sai Muka tsĩrar da ku kuma Muka nutsar da mutãnen Fir´auna, alhãli kuwa kũ kuna kallo. [2.51] Kuma a lõkacin da muka yi wa´adi ga Mũsa, dare arba´in, sa´an nan kuma kuka riƙi maraƙi daga bãyansa, alhãli kũ, kuna mãsu zãlunci (da bauta masa). [2.52] Sa´an nan kuma muka yãfe muku daga bãyan wancan, tsammãninku, kuna gõdħwa. [2.53] Kuma a lõkacin da Muka baiwa Mũsa Littãfi da rarrabħwa, tsammãninku, kuna shiryuwa. [2.54] Kuma a lõkacin da Mũsa ya ce ga mutãnensa: "Ya mutãnena! Lalle ne ku, kun zãlunci kanku game da riƙonku maraƙin, sai ku tũba zuwa ga Mahaliccinku, sai ku kashe kãwunanku. Wancan ne mafi alheri a wajen mahaliccinku. Sa´an nan Ya karɓi tuba a kanku. Lalle ne Shi, Shi ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai. [2.55] Kuma a lõkacin da kuka ce: "Ya Musa! Bã zã mu yi ĩmãni ba dõminka, sai munga Allah bayyane," sabada haka tsãwar nan ta kamaku, alhãli kuwa kuna kallo. [2.56] Sa´an nan kuma Muka tãyar da ku daga bãyan mutuwarku, tsammãninku, kuna gõdħwa. [2.57] Kuma Muka sanya girgije ya yi inuwa a kanku, kuma Muka saukar da darɓa da tantabaru a kanku; "Ku ci daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku." kuma ba su zãlunce Mu ba, kuma amma kansu suka kasance suna zãlunta. [2.58] Kuma a lokacin da Muka ce: "Ku shiga wannan alƙarya. Sa´an nan ku ci daga gareta, inda kuka so, bisa wadata, kuma ku shiga ƙofa kuna masu tawalu´i, kuma ku ce; "kãyar da zunubai" Mu gãfarta muku laifukanku, kuma zã mu ƙãra wa mãsu kyautatawa." [2.59] Sai waɗanda suka yi zalunci suka sake magana watar wannan da aka ce musu, saboda haka muka saukar a kan waɗanda suka yi zãlunci da azãba daga sama sabõda abin da suka kasance suna yi na fãsiƙanci. [2.60] Kuma a lokacin da Mũsa ya nemi shãyarwa domin mutãnensa, Muka ce; "Ka dõki dũtsen da sandarka." Sai marmaro gõma sha biyu suka ɓuɓɓuga, haƙĩƙa, kõwaɗanne mutãne sun san wurin shansu. "Ku ci kuma ku sha daga arziƙin Ubangijinku, kuma kada ku yi fasadi, a cikin ƙasa, kuna mãsu ɓarna." [2.61] Kuma a lõkacin da kuka ce: "Yã Mũsã! Bã zã mu yi haƙuri ba a kan abinci guda. Sai ka rõƙa mana Ubangijinka Ya fitar mana daga abin da ƙasa take tsirarwa daga ganyenta, dumanta, da alkamarta da albasarta. Ya ce: "Kuna nħman musanya abin da yake mafi ƙasƙanci da wanda yake mafi alhħri? Ku sauka wani birni (daga cikin birane), domin lalle ne, kuna da abin da kuka rõƙa. "Kuma Muka dõka musu wulãƙanci da talauci. Kuma suka kõma da wani fushi daga Allah. Wancan sabõda lalle su, sun kasance suna kãfirta da ãyõyin Allah, kuma suna kashe Annabãwa, bãda hakki ba. Wancan, sabõda sãɓawarsu ne, kuma sun kasance suna ƙħtarewar haddi. [2.62] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, da waɗanda suka tũba (1) , da Nasãra da Makarkata, wanda ya yi ĩmani da Allah da Yinin Lãhira, kuma ya aikata aikin ƙwarai, to, suna da ijãrarsu a wurin Ubangijinsu, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba. [2.63] Kuma a lõkacin da Muka riƙi alƙawarinku, kuma Muka ɗaukaka dũtse a bisa gareku: "Ku kãma abin da Muka baku da ƙarfi. Kuma ku ambaci abin da yake a cikin sa, tsammãninku ku kãrekanku. [2.64] Sa´an nan kuma kuka jũya daga bayan wancan, to, bã dõmin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa, haƙĩƙa, dã kun kasance daga mãsu hasãra." [2.65] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, kun san waɗanda suka ƙħtare haddi daga gare ku a cikin Asabar, sai muka ce musu: "ku kasance birai ƙasƙantattu." [2.66] Muka sanya ta (mas´alar) azãba, dõmin abin da abin da yake gaba gareta, da yake a bãyanta, kuma wa´azi ga mãsu taƙawa. [2.67] Kuma a lõkacin da Musa yace ga mutanensa: "Lalle ne, Allah Yana umurnin ku da ku yanka wata sãniya." Suka ce: "Shin kana riƙon mu ne da izgili?" Ya ce: "Ina nħman tsari ga Allah da in kasance daga jãhilai." [2.68] Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka, Ya bayyana mana, mecħ ce ita?" Ya ce: "Lalle ne, Shi, Yana cewa: "Lalle ne ita sãniya ce; bã tsõfuwa ba, bã kuma budurwa ba, tsakãtsaki ce a tsakãnin wancan,´ sai ku aikata abin da ake umurninku." [2.69] Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka Ya bayyana mana abin da yake launinta." Ya ce: "Lalle ne, Shi Yana cewa: "Ita wata saniya ce Fatsi, mai tsan-tsan launi, tana faranta ran masu kallo." [2.70] Suka ce: "Ka rõƙa mana Ubangijinka, Ya bayyana mana abin da yake ita, lalle ne shãnu suna yi mana kamã da jũna, kuma mu, idan Allah Yã so, haƙĩƙa, shiryuwa ne." [2.71] Ya ce: "Lalle ne Shi, Yana cħwa: "Ita wata sãniya ce; ba horarra bã tana noman ƙasa, kuma ba ta shayar da shuka, lãfiyayya ce: bãbu wani sõfane a cikinta." Suka ce: "Yanzu kã zo da gaskiya. Sai suka yanka ta, kamar ba zã su aikata ba. [2.72] Kuma a lõkacin da kuka yi kisan kai, kuka dinga tunkuɗa wa jũna laifĩ a cikinsa,(1) kuma Allah Mai fitar da abin da kuka kasance kuna ɓõyħwa ne. [2.73] Sai Muka ce: "Ku dõke shi da wani sãshenta." Kamar wancan ne Allah Yake rãyar da matattu, kuma Ya nũna muku ayõyinSa, tsammãninku kuna hankalta. [2.74] San´nan kuma zukãtanku, suka ƙħƙashe daga bãyan wancan. Sabõda haka suka zama kamar duwatsu. ko mafi tsananin ga ƙeƙashewa. kuma lalle ne daga duwãtsu, haƙĩka, akwai abin da maremari suke ɓuɓɓuga daga gare shi, kuma lalle ne daga gare su, haƙĩƙa, akwai abin da yake tsatstsagewa har ruwa ya fita daga gare shi, kuma lalle ne, haƙĩƙa, daga gare su, haƙĩƙa, akwai da yake fãɗõwa dõmin tsõron Allah, kuma Allah bai zama gãfili ba daga barin abin da kuke aikatãwa. [2.75] Shin fa kuna tsammãnin zã su yi imãni sabõda ku, alhãli kuwa, haƙĩƙa, wata ƙungiya daga gare su sun kasance suna jin maganar Allah, sa´an nan kuma su karkatar da ita daga bãyan sun gãne ta, alhãli sũ, suna sane? [2.76] Kuma idan sun haɗu da waɗanda suka yi ĩmãni sukan ce: "Mun yi ĩmãni," kuma idan sãshensu ya wõfinta zuwa ga sãshe, sukan ce: "Shin, kuna yi musu magana da abin da Allah Ya buɗa muku ne dõmin su yi muku hujja da shi a wurin Ubangijinku?" Shin fa, bã ku hankalta? [2.77] Shin, kuma bã su sanin cħwa lalle ne Allah Yana sanin abin da suke ɓõyħwa da abin da suke bayyanãwa? [2.78] Kuma daga cikinsu akwai ummiyyai, bã su da sanin Littãfi, fãce tãtsuniyoyi, kuma sũ bã kõme suke yi ba fãce suna yin zato. [2.79] To, bone ya tabbata ga waɗanda suke rubũta littãfi da hannuwansu sa´an nan kuma su ce wannan daga wurin Allah yake, dõmin su sayi kuɗi kaɗan da shi, san nan bone ya tabbata a gare su daga abin da hannayensu ke rubũtãwa, kuma bone ya tabbata a gare su daga abin da suke sanã´antãwa. [2.80] Kuma suka ce: "Wuta bã zã ta shãfe mu ba, fãce, ´yan kwãnuka ƙidãyayyu."Ka ce: "Ashe kun riƙi wani alkawari a wurin Allah, sa´an nan Allah ba zai sãɓa wa alkawarinSa ba ko kuwa kuna faɗin abin da ba ku sani ba bisa ga Allah?" [2.81] Na´am! Wanda ya yi tsiwur-wurin mũgun abu, kuma laifinsa ya kħwaye shi, to, waɗannan su ne ´yan Wuta, sũ a cikinta madawwama ne. [2.82] Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, waɗannan, ´yan Aljanna ne, sũ a cikinta madawwama ne. [2.83] Kuma a lõkacin da Muka karɓi alkawarin Bani-Isrã´ĩla(1) : "Kada ku bauta wa kõwa fãce Allah, kuma ga mahaifa ku kyautata, da mai zumunta da marãyu da matalauta, kuma ku faɗi magana mai kyau zuwa ga mutãne, kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka, sa´an nan kuka jũya bãya, fãce kaɗan daga gare ku,alhãli kuwa kuna mãsu bijirħwa. [2.84] Kuma a Lõkacin da Muka riƙi alkawarinku; bã zã ku zubar da jininku ba, kuma bã zã ku fitar da kanku daga gidãjenku ba; sa´an nan kuka tabbatar alhãli kuwa kuna bãyar da shaida (a kanku). [2.85] Sa´an nan kuma, gã ku, yã waɗannan! Kuna kashe kanku, kuma kuna fitar da wani ɓangare daga gare ku daga gidãjensu, kuna taimakon jũna a kansu da zunubi da zãlunci kuma idan kãmammu suka je muku kuna fansarsu alhãli kuwa shĩ fitar da su abin da aka haramta muku ne. Shin fa, kuna ĩmãni da sãshen Littãfin ne, kuma ku kãfirta da sãshe? To, mħne ne sakamakon wanda ke aikata wancan daga gare ku fãce wulãkanci(1) a cikin rãyuwar dũniya? Kuma a Rãnar Ƙiyãma ana mayar da su zuwa ga mafi tsananin azãba. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga barin abin da kuke aikatãwa. [2.86] Waɗannan su ne waɗanda suka sayi rãyuwar dũniya da Lãhira, dõmin haka bã zã a sauƙaƙa azãba ba daga kansu, kuma sũ, bã a taimakonsu. [2.87] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã Littãfi, kuma Mun biyar daga bãyansa da wasu Manzanni, kuma Muka bai wa Ĩsã ɗan Maryama hujjõji bayyanannu, kuma Muka ƙarfafa shi da Rũhi mai tsarki.(2) Shin fa, kõ da yaushe wani manzo ya je muku tãre da abin da rãyukanku bã su so, sai ku kangara, wani ɓangare kun ƙaryata, kuma wani ɓangare kuna kashħwa? [2.88] Kuma suka ce: "Zukatanmu suna cikin rufi." A´a, Allah Yã la´ane su, dõmin kafircinsu kadan kwarai suke yin ĩmãni! [2.89] Kuma a lõkacin da wani Littãfi daga wurin Allah ya je musu, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da su, alhãli kuwa sun kasance daga gabãnin haka suna fãtar taimako(1) da shi a kan waɗanda suka kãfirta. To, a lõkacin da abin da suka sani ya je musu, sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka la´anar Allah ta tabbata a kan kãfirai. [2.90] Tir da abin da suka sayi rãyukansu da shi; watau su kãfirta da abin da Allah Ya saukar sabõda zãlunci;(2) kada Allah Ya saukar da falalarsa a kan wanda Yake so daga bãyinsa. Sai suka kõmo da fushi game da wani fushi. Kuma ga kãfirai akwai azãba mai wulãƙantarwa. [2.91] Kuma idan aka ce musu: "Ku yi ĩmãni da abin da Allah Ya saukar." Sai su ce: "Muna ĩmãni da abin da aka saukar a gare mu," kuma suna kãfircħwa da abin da ke bãyansa, alhãli kuwa, shi ne gaskiyar (da suka sani) mai gaskatawa ga abin da yake tãre da su (na Attaura). Ka ce: "To, don me kuke kashe annabãwan Allah gabãnin wannan, idan kun kasance mãsu bãyar da gaskiya?"(3) [2.92] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mũsã ya zo muku da hujjõji bayyanannu, sa´an nan kuka riƙi maraƙi(4) daga bãyansa, alhãli kuwa kuna mãsu zãlunci. [2.93] Kuma a lõkacin da Muka riƙi(5) alkawarinku kuma Muka ɗaukaka dutse a bisa gare ku, (Muka ce:) "Ku riƙi abin da Muka kãwo muku da ƙarfi kuma ku ji" Suka ce: "Mun ji kuma mun ƙi." Kuma aka zuba son maraƙin a cikin zukatansu sabõda kãfircinsu. Ka ce: "Tir da abin da ĩmãninku yake umurnin ku da shi, har idan kun kasance mãsu ĩmãni!" [2.94] Ka ce: "Idan Gidan(1) Lãhira ya kasance sabõda ku, a wurin Allah keɓe bã da sauran mutãne ba, to, ku yi gũrin mutuwa, idan kun kasance mãsu gaskiya." [2.95] Kuma bã zã su yi gũrinta ba har abada sabõda abin da hannayensu, suka gabãtar. Kuma Allah Masani ne ga azzãlumai. [2.96] Kuma lalle ne, zã ka sãme su mafiya kwaɗayin mutãne a kan rãyuwa, kuma sũ ne mafiya kwaɗayin rãyuwa daga waɗanda suka yi shirka. Ɗayansu yana son dã zã a rãyar da shi shekara dubu, kuma bã ya zama mai nĩsantar da shi daga azãba dõmin an rãyar da shi. Kuma Allah, Mai gani ne ga abin da suke aikatãwa. [2.97] Ka ce: Wanda ya(2) kasance maƙiyi ga Jibirilu, to, lalle ne shi ya saukar da shi a kan zũciyarka da izinin Allah, yana mai gaskatãwa ga abin da yake gaba gare shi, kuma da shiriya da bishãra ga mũminai. [2.98] Wanda ya kasance maƙiyi ga Allah da malã´ikunSa da manzanninSa da Jibirĩla da Mĩkã´ĩla to, lalle ne, Allah Maƙiyi ne ga kãfirai. [2.99] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun saukar, zuwa gare ka, ãyõyi bayyanannu, kuma ba wanda yake kãfirta da su fãce fãsikai(3) . [2.100] Shin, kuma a kõ da yaushe suka ƙulla wani alkawari sai wani ɓangare daga gare su ya yi jĩfa da shi? ôa, mafi yawansu bã su yin ĩmãni. [2.101] Kuma a lõkacin da wani manzo (Muhammadu) daga wurin Allah ya je musu, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da su, sai wani ɓangare daga waɗanda aka bai wa Littãfi, suka yar da Littãfin (Alƙur´ãnin) Allah a bãyan bãyansu, kamar dai sũ ba su sani ba. [2.102] Kuma suka bi abin da shaiɗãnu(1) ke karantawa a kan mulkin Sulaimãnu, kuma Sulaimãnu bai yi kãfirci ba, kuma Shaidãnun, sũ ne suka yi kãfirci, suna karantar da mutãne sihiri. Kuma ba a saukar da shi ba a kan malã´iku biyu a Bãbila, Harũta da Mãrũta. Kuma ba su sanar da kõwa ba balle su ce: "Mũ fitina kawai ne, sabõda haka kada ka kãfirta," balle har su yi ta nħman ilmin abin da suke rarrabħwa tsakãnin mutum da mãtarsa da shi daga gare su. Kuma su (mãsu yin sihirin) ba su zama mãsu cũtar da kõwa da shi ba, fãce da iznin Allah. Kuma suna nħman ilmin abin da yake cũtar da su, kuma bã ya amfaninsu. Kuma lalle ne, haƙiƙa, sun sani, tabbas, wanda ya saye shi, bã ya da wani rabo a cikin Lãhira. Kuma tir da abin da suka sayar da rãyukansu da shi, dã sun kasance suna sani. [2.103] Kuma dã lalle ne sũ, sun yi ĩmani, kuma sun yi taƙawa, haƙiƙa, da sakamako daga wurin Allah shi ne mafi alhħri, dã sun kasance suna sani. [2.104] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmani! Kada ku ce: ´Rã´inã´(2) kuma ku ce: ´Jinkirtã manã´, kuma ku saurara. Kuma kãfirai suna da azãba mai raɗaɗi. [2.105] Waɗanda suka kãfirta daga Ma´abuta Littãfi, bã su son a saukar da wani alhħri a kanku daga Ubangijinku, kuma mushirikai mã bã su so. Kuma Allah Yana keɓance da wanda Yake so da rahamarSa. Kuma Allah Ma´abũcin falala mai girma ne. [2.106] Abin da Muka shãfe(1) daga ãya, ko kuwa Muka jinkirtar da ita, zã Mu zo da mafi alhħri daga gare ta ko kuwa misãlinta. Ashe, ba ka sani ba, cħwa lalle ne, Allah a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne? [2.107] Shin ba ka sani ba, cħwa lalle ne Allah, Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa kuma bã ku da, baicin Allah, wani majiɓinci, kuma bã ku da wani mataimaki? [2.108] Kõ kuna nufin ku tambayi Manzonku, kamar yadda aka tambayi Mũsã a gabãnin haka? Kuma wanda ya musanya kãfirci da ĩmãni, to, lalle ne yã ɓace tsakar hanya. [2.109] Mãsu yawa daga Ma´abuta Littãfi sunã gũrin dã sun mayar da ku, daga bãyan ĩmãninku, kãfirai,sabõda hãsada daga wurin rãyukansu, daga bayãn gaskiya tã bayyana a gare su. To, ku yãfe, kuma ku kau da kai, sai Allah Yã zo da umurninSa. Lalle ne Allah a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne. [2.110] Kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka. Kuma abin da kuka gabãtar dõmin kanku daga alhħri, zã ku sãme shi a wurin Allah. Lalle ne Allah, ga abin da kuke aikatãwa Mai gani ne. [2.111] Kuma suka ce: "Bãbu mai shiga Aljanna fãce waɗanda suka zama Yahũdu ko Nasãra." Waɗancan tãtsũniyõyinsu ne. Ka ce: "Ku kãwo dalilinku idan kun kasance mãsu gaskiya." [2.112] Na´am! Wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yana mai kyautatãwa, to, yana da ijãrarsa, a wurin Ubangijinsa, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba. [2.113] Kuma Yahũdãwa suka ce: "Nasãra ba su zamana a kan kõme ba," kuma Nasãra suka ce: "Yahũdãwa ba su zamana a kan kõmeba,"(1) alhãli kuwa su, suna karãtun Littãfi. Kamar wancan ne waɗanda ba su sani ba suka faɗa, kamar maganarsu sabõda haka Allah ne ke yin hukunci a tsakãninsu a Rãnar Ƙiyãma, a cikin abin da suka kasance suna sãɓawa jũna a cikinsa. [2.114] Kuma wãne ne mafi zãlunci(2) daga wanda ya hana masallãtan Allah, dõmin kada a ambaci sunanSa a cikinsu, sai kuma ya yi aiki ga rushe su? Waɗannan bã ya kasancħwa a gare su su shigħ su fãce suna mãsu tsõro. Suna da, a cikin duniya wani wulãkanci, kuma suna da, a cikin Lãhira, azãba mai girma. [2.115] Kuma Allah ɗai yake da gabas da yamma sabõda haka, inda duk aka jũyar da ku, to, a can fuskar Allah take. Lalle ne, Allah Mawadãci ne, Mai ilmi. [2.116] Kuma suka ce: "Allah Yã riƙi(3) ɗã." Tsarki yã tabbata a gare Shi! A´a, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da ƙasa, dukansu, a gare Shi, mãsu ƙanƙan da kai ne. [2.117] Mai kyautata halittar sammai da ƙasa, kuma idan Ya hukunta wani al´amari, sai kawai Ya ce masa: "Kasance." Sai ya yi ta kasancewa. [2.118] Kuma waɗanda bã su da sani suka ce: "Don me Allah bã Ya yi mana magana, ko wata ãyã ta zo mana?"(4) Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu suka faɗa, kamar maganarsu. zukãtansu sun yi kamã da jũna. Lalle ne, Mun bayyana ãyõyi ga mutãne masu sakankancewa. [2.119] Lalle ne Mun aike ka da gaskiya, kana mai bãyar da bishãra, kuma mai gargaɗi, kuma bã zã a tambaye ka ba, game da abõkan Wuta. [2.120] Kuma Yahũdu bã zã su yarda da kõme daga gare ka ba, kuma Nasãra bã zã su yarda ba, sai kã bi irin aƙidarsu. Ka ce: "Lalle ne, shiriyar Allah ita ce shiriya." Kuma lalle ne idan ka bi son zũciyõyinsu a bãyan abin da ya zo maka na ilmi, bã ka da, daga Allah, wani majiɓinci, kuma bãbu wani mataimaki. [2.121] Waɗanda Muka bai wa Littãfi suna karãtunsa a kan haƙƙin karãtunsa, waɗannan suna ĩmani da shi (Alƙur´ãni). Kuma wanda ya kãfirta da shi, to, waɗannan sũ ne mãsu hasãra. [2.122] Yã Banĩ Isrã´ĩla! Ku(1) tuna ni´imaTa wadda Na ni´imtar da ita a kanku, kuma lalle ne Nĩ, Nã fĩfĩtã ku a kan tãlikai. [2.123] Ku ji tsõron wani yini, (a cikinsa) wani rai bã ya tunkuɗe wa wani rai kõme kuma bã a karɓar fansa daga gare shi, kuma wani cħto bã ya amfanin sa, kuma ba su zama ana taimakon su ba. [2.124] Kuma a lõkacin da Ubangijin Ibrãhim Ya jarrabħ shi da wasu kalmõmi, sai ya cika su. Ya ce: "Lalle ne Nĩ, Mai sanya ka shugaba dõmin mutãne ne." Ya ce: "Kuma daga zũriyata." Ya ce: "AlkawarĩNa bã zai sãmu azzãlumai ba." [2.125] Kuma a lõkacin da Muka sanya Ɗãkin ya zama makõma ga mutãne, da aminci, kuma ku riƙi wurin salla daga Maƙãmi Ibrãhĩm, kuma Muka yi alƙawari zuwa ga Ibrãhĩm, da Ismã´ila da cħwa: "Ku tsarkake ƊãkiNa dõmin mãsu ɗawãfi da mãsu lizimta da mãsu rukũ´i, mãsu sujada." [2.126] Kuma a lõkacin da lbrãhĩm ya ce: "Yã Ubangijĩna! Ka sanya wannan gari amintacce, Ka azurta mutãnensa, daga ´ya´yan itãcen, wanda ya yi ĩmãni, daga gare su, da Allah da Ranar Lãhira." Allah Ya ce: "Wanda ya kãfirta ma Ina jiyar da shi dãɗi kaɗan, sa´an nan kuma Ina tĩlastã shi zuwa ga azãbar Wuta. Kuma makõmar, ta munana." [2.127] Kuma a lõkacin da Ibrãhĩm yake ɗaukaka harsãshin gini ga Ɗãkin, da Ismã´ĩla (suna cħwa:) "Yã Ubangijnmu! Ka karɓa daga gare mu, lalle ne Kai, Kai ne Mai ji, Mai sani. [2.128] "Ya Ubangijnmu! Ka sanyã mu, mu biyu, waɗanda suka sallama (al´amari) gare Ka, kuma daga zuriyarmu (Ka sanya) al´umma mai sallamãwa zuwa gare Ka, Kuma Ka nũna mana wurãren ibãdar hajjinmu, kuma Ka karɓi tũba a kanmu. Lalle ne Kai, Kai ne Mai karɓar tũba, Mai rahama. [2.129] "Ya Ubangijinmu! Ka aiko, a cikinsu, wani manzo(1) daga gare su, yana karanta musu ãyõyinKa, kuma yana karantar da su Littãfin(2) da hikimar, kuma yana tsarkake su. Lalle ne Kai, Kai ne Mabuwãyi Mai hikima." [2.130] Kuma wãne ne yake gudu daga aƙĩdar Ibrãhĩm, fãce wanda ya jãhilta ga ransa? Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe shi, a cikin dũniya, kuma lalle ne shi, a cikin Lãhira, haƙĩƙa, yana daga sãlihai. [2.131] A lõkacin da Ubangijinsa Ya ce masa: "Ka miƙa wuya," ya ce: "Nã miƙa wuya ga Ubangijin tãlikai." [2.132] Kuma lbrãhĩm ya yi wasiyya da ita ga ɗiyansa, kuma Ya´aƙũbu (ya yi wasiyya,suka ce:) "Yã ɗiyãna! Lalle ne, Allah Ya zãɓã muku addini don haka kada ku mutu, lalle, fãce kuna Musulmi." [2.133] Ko kun(3) kasance halarce a lõkacin da mutuwa ta halarci Ya´aƙũbu, a lõkacin da ya ce wa ɗiyansa: "Mħne ne zã ku bauta wa daga bãyãna?" Suka ce: "Muna bauta wa Abin bautawarka kuma Abin bautawar ubanninka lbrãhĩm da lsmã´ĩla da Is´hãƙa, Ubangiji Guda, kuma mu a gare Shi mãsu miƙa wuya ne." [2.134] Waccan, wata al´umma ce, ta riga ta shige, tana da abin da ta sanã´anta kuma kuna da abin da kuka sanã´anta, Kuma bã zã a tambaye ku ba daga abin da suka kasance suna aikatãwa. [2.135] Kuma suka ce: "Ku kasance(1) Yahũdãwa ko Nasãra, kwã shiryu."Ka ce: "A´a aƙidar Ibrãhĩm dai, maikarkata, zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba." [2.136] Ku(2) ce: "Mun yi ĩmãni da Allah, da abin da aka saukar zuwa gare mu, da abin da aka saukar zuwa ga Ibrãhĩm da Ismã´ĩla da Is´hãka da Ya´aƙũbu da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da Ĩsã, da abin da aka bai wa annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu rarrabħwa a tsakãnin kõwa daga gare su, kuma mu, a gare Shi, mãsu miƙa wuya ne." [2.137] To, idan sun yi ĩmãni(3) da misãlin abin da kuka yi ĩmãni da shi, to, lalle ne sun shiryu, kuma idan sun jũya bãya, to, suna a cikin sãɓãni kawai sabõda haka Allah zai isar maka a gare su, kuma Shi ne Mai ji, Masani. [2.138] Rinin Allah! Kuma wãne ne mafi kyau ga rini daga Allah? Kuma mu, a gare Shi, mãsu bautãwa ne. [2.139] Ka ce: Shin kuna jãyayyar hujia ne da mu a cikin al´amarin Allah, alhãli kuwa Shi ne Ubangijinmu kuma Ubangijinku, kuma muna da ayyukanmu, kuma kuna da ayyukanku, kuma mũ, a gare Shi, mãsu tsarkakħwane? [2.140] Ko kuna cħwa: Lalle ne, Ibrãhĩm da Ismã´ĩla da Is´hãƙa da Ya´aƙũbu da Jĩkõki, sun kasance Yahũdãwa kõ kuwa Nasãra? Ka ce: Shin kũ ne kuke mafi sani kõAllah? Kuma wãne ne ya zama mafi zãlunci daga wanda ya bõye shaida a wurinsa daga Allah? Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da kuke aikatãwa! [2.141] Waccan, wata al´umma ce, tã riga ta shige, suna da abin da suka sana´anta kuma kuna da abin da kuka sana´anta kuma bã a tambayar ku daga abin da suka kasance suna aikatãwa. [2.142] Wãwãye daga mutãne zã su ce: Mħne ne ya jũyar da su daga alƙiblarsu wadda suka kasance a kanta? Ka ce: "Allah Ɗai ne Yake da gabas da yamma, Yana shiryar da wanda Yake so zuwa ga hanya madaidaiciya." [2.143] Kuma kamar wancan, Muka sanya ku al´umma matsakaiciya(1) dõmin ku kasance mãsu bãyar da shaida a kan mutãne. Kuma Manzo ya kasance mai shaida a kanku. Kuma ba Mu sanya Alƙibla(2) wadda ka kasance a kanta ba, fãce dõmin Mu san wanda yake biyar Manzo daga wanda yake jũyãwa a kan duga-dugansa. Kuma lalle ne, tã kasance haƙĩƙa, mai girma, sai a kan waɗanda Allah Ya shiryar. Kuma ba ya yiwuwa ga Allah Ya tõzartar da ĩmãninku.(3) Lalle ne, Allah, ga mutãne, haƙĩƙa, Mai tausayi ne, Mai jin ƙai. [2.144] Lalle ne, Muna ganin jujjũyãwar fuskarka a cikin sama. To, lalle ne, Mu jũyar da kai ga Alƙibla wadda kake yardã da ita. Sai ka jũyar da fuskarka wajen Masallãci Tsararre, kuma inda duk kuka kasance, to, ku jũyar da fuskõkinku jiharsa. Kuma lalle ne waɗanda aka bai wa Littãfi, haƙĩƙa su, sunã sanin lalle ne, shĩ ne gaskiya, daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da suke aikatãwa. [2.145] Kuma hakĩka, idan ka je wawaɗanda aka bai wa Littafi da dukan ãyã, bã zã su bi Alƙiblarka ba, kuma kai ba ka zama mai bin Alƙiblarsu ba, kuma sãshensu bã mai bin Alƙiblar(4) sãshe ba ne. Kuma haƙĩƙa, idan ka bi son zũciyõyinsu daga bãyan abin da ya zo maka daga ilmi, lalle ne kai, sa´an nan, haƙiƙa, azzãlumi kake. [2.146] Waɗanda Muka bã su Littãfi, suna saninsa kamar yadda suke sanin ɗiyansu. Kuma lalle ne wani ɓangare daga gare su, haƙiƙa, suna ɓõyewar gaskiya alhãli kuwa sũ, suna sane. [2.147] Gaskiya daga Ubangijinka(1) take sabõda haka, lalle kada ka kasance daga mãsu shakka. [2.148] Kuma kõwane ɓangare yana da alƙibla wadda yake shi mai fuskantar ta ne. Sai ku yi tsħre zuwa ga ayyukan alhħri, inda kuka kasance duka Allah zai zo da ku gabã ɗaya. Lalle ne Allah, a kan kõme, Mai ĩkon yi ne. [2.149] Kuma daga inda ka fita, to, sai ka jũyar da fuskarka a wajen Masallãci Tsararre kuma lalle tabbas, shi ne gaskiya daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da kuke aikatãwa ba. [2.150] Kuma daga inda ka fita, to, ka jũyar da fuskarka a wajen Masallãci Tsararre kuma inda kuke duka, to, ku jũyar da fuskõkinku a wajensa, dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kanku, fãce waɗanda suka yi zãlunci daga gare su. Sabõda haka kada ku ji tsõronsu kuma ku ji tsõrõNa kuma dõmin In cika ni´imaTa a kanku, kuma tsammãninku zã ku shiryu. [2.151] Kamar(2) yadda Muka aika Manzo a cikinku, daga gare ku, yana karanta ãyõyinMu a gare ku kuma yana tsarkake ku, kuma yana sanar da ku Littãfi da hikima, kuma yana sanar da ku abin da ba ku kasance kuna sani ba. [2.152] Sabõda haka, ku tuna Ni, In tunã ku, kuma ku yi gõdiya gare Ni, kuma kada ku butulce Mini. [2.153] Ya ku waɗanda(3) suka yi ĩmãni! Ku nħmi taimako da haƙuri game da salla. Lalle ne, Allah na tãre da mãsu haƙuri. [2.154] Kada ku ce ga waɗanda(1) ake kashħwa a cikin hanyar Allah: "Matattu ne." ôa, rãyayyu ne, kuma amma bã ku sansancħwa. [2.155] Kuma lalle ne, Muna jarrabar ku da wani abu daga tsõro da yunwa da naƙasa daga dũkiya da rãyuka da ´ya´yan itãce. Kuma ka yi bishãra ga mãsu haƙuri. [2.156] Waɗanda suke idan wata masĩfa ta sãme su, sai su ce: "Lalle ne mũ ga Allah muke, kuma lalle ne mũ, zuwa gare Shi, muke kõmãwa." [2.157] Waɗannan akwai albarku a kansu daga Ubangijinsu da wata rahama. Kuma waɗannan sũ ne shiryayyu. [2.158] Lalle ne Safã da Marwa(2) suna daga wurãren ibãdar Allah, to, wanda ya yi hajin Ɗãki kõ kuwa ya yi Umra, to, bãbu laifi a kansa ga ya yi ɗawãfi gare su, su biyu. Kuma wanda ya ƙãra yin wani aikin alhħri to, lalle ne Allah Mai gõdiya ne, Masani. [2.159] Lalle ne waɗanda suke ɓõyħwar abin da Allah Ya saukar da ga hujjõji bayyanannu, da shiriya, daga bãyan Mun bayyana shi ga mutãne, a cikin Littãfi (Alƙur´ãni), waɗannan Allah Yana la´anar su, kuma mãsu la´ana suna la´anar su. [2.160] Sai waɗanda suka tũba,kuma suka gyãra, kuma suka bayyana, to waɗannan Ina karɓar tũba a kansu kuma Nĩ ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai. [2.161] Lalle ne, waɗanda suka kãfirta kuma suka mutu alhãli kuwa suna kãfirai, waɗannan akwai, a kansu, la´anar Allah da Malã´iku da mutãne gabã ɗaya. [2.162] Suna madawwama a cikinta, bã a sauƙaƙa azãba daga barinsu, kuma ba su zama ana jinkirta musu ba. [2.163] Kuma Ubangijinku Ubangiji(3) Guda ne. Bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Mai rahama, Mai jin ƙai. [2.164] Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa, da sãɓãwar dare da yini, da jirãge wadaɗnda suke gudana a cikin tħku (ɗauke) da abin da yake amfãnin mutãne, da abin da Allah Ya saukar daga sama daga ruwa, sai Ya rãyar da ƙasa da shi a bãyan mutuwarta, kuma Ya wãtsa, a cikinta, daga dukan dabba, kuma da jũyãwar iskõki da girgije hõrarre a tsakãnin sama da ƙasa; haƙĩƙa, akwaiãyõyi ga mutãne mãsu yin hankali. [2.165] Kuma akwai daga mutãne wanda yake riƙon kinãye, baicin Allah, suna son su, kamar son Allah, kuma waɗanda suka yi ĩmãni ne mafiya tsananin so(1) ga Allah. Kuma dã waɗanda(2) suka yi zãlunci, suna ganin lõkacin da zã su ga azãba, da cewa lalle ne ƙarfi ga Allah yake duka, da cħwa lalle neAllah Mai tsananin azãba ne. [2.166] A lõkacin da waɗanda aka bi suka barranta daga waɗanda suka bi, kuma suka ga azãba, kuma sabubba suka yanke da su. [2.167] Kuma waɗanda suka bi, suka ce: "Dã lalle ne muna da wata kõmãwa (dũniya) sai mu barranta daga gare su kamar yadda suka barranta daga gare mu (dã ba su riƙi kinãyen ba)." Kamar wancan ne Allah ke nũna musu ayyukansu, suna da nadãmõmi a kansu, kuma ba su zama mãsu fita daga wutar ba. [2.168] Yã ku mutãne!(3) Ku ci daga abin da yake a cikin ƙasa, wanda yake halal, mai dãɗi. Kuma kada ku bi zambiyõyin(4) Shaiɗan. Lalle ne shi, gare ku, maƙiyi ne bayyananne. [2.169] Yana umurnin ku ne kawai da mugun aiki da alfãsha, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba ga Allah. [2.170] Kuma idan aka ce musu: "Ku bi abin da Allah Ya saukar," sai su ce: ôa, muna bin abin da muka iske ubanninmu a kansa." Shin, kuma kõ dã ubanninsu bã su hankaltar kõme, kuma bã su shiryuwa? [2.171] Kuma misãlin (mai kiran) waɗanda suka kãfirta kamar misãlin wanda ke yin me! me! ga abin da ba ya ji ne, fãce kira da ƙãra, kurãme, bħbãye, makafi, sabõda haka bã su hankalta. [2.172] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku ci ku sha daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku. Kuma ku gõde wa Allah, idan kun kasance Shi kuke bauta wa. [2.173] Kawai abin da Ya haramta a kanku, mũshe da Jini da nãman alade da abin da aka kurũrũta game da shi ga wanin Allah. To, wanda aka matsã, wanin ɗan tãwãye, kuma banda mai zãlunci, to bãbu laifi a kansa. Lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [2.174] Lalle ne waɗannan da suke ɓõye abin da Allah Ya saukar daga Littãfi, kuma suna sayen kuɗi kaɗan da shi; waɗannan bã su cin kome a cikin cikkunansu fãce wuta, kuma Allah bã zai yi musu magana ba a Rãnar Ƙiyãma, kuma bã zai tsarkake su ba, kuma suna da azãba mai raɗaɗi. [2.175] Waɗannan su ne waɗanda suka sayi ɓata da shiriya, kuma azãba da gãfara. To, me ya yi haƙurinsu a kan Wuta! [2.176] Wancan dõmin lalle ne Allah Ya saukar da Littafi da gaskiya, kuma lalle ne waɗanda suka sãɓã a cikin Littãfin, haƙĩƙa, suna a cikin sãɓãni mai nĩsa. [2.177] Bai zama addini(1) ba dõmin kun jũyar da fuskõkinku wajen gabas da yamma, kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira da malã´iku da Littattafan sama da Annabãwa, kuma ya bãyar da dũkiya, akan yana son ta, ga mai zumunta da marãyu da matalauta da ɗan hanya da mãsu rõƙo, kuma a cikin fansar wuya, kuma ya tsayar da salla, kuma ya bãyar da zakka, da mãsu cika alkawari idan sun ƙulla alkawarin da mãsu haƙuri a cikin tsanani da cũta da lõkacin yãƙi. Waɗannan su ne suka yi gaskiya. Kuma waɗannan su ne mãsu taƙawa. [2.178] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! An wajabta, a kanku, yin ƙisãsi(2) a cikin kasassu. ɗa da ɗa kuma bãwa da bãwa, kuma mace da mace, to, wanda aka yi rangwamen wani abu gare shi daga ɗan´uwansa to a bi da alhħri da biya zuwa gare, shi da kyautatãwa. Wancan sauƙaƙewa ne daga Ubangijinku, kuma rahama ce. To, wanda ya yi zãlunci a bãyan wancan, to, yana da azãba mai raɗaɗi. [2.179] Kuma kuna da rãyuwa a cikin ƙisãsi, yã ma´abuta hankula; tsammãninku, zã ku yi taƙawa. [2.180] Kuma an wajabta,(3) a kanku idan mutuwa ta halarci ɗayanku, idan ya bar wata dũkiya, wasiyya dõmin mahaifa da dangi bisa ga abin da aka sani; wajabce a kan mãsu taƙawa. [2.181] To, wanda ya musanya masa a bãyan ya ji shi, to, kawai laifinsa yana a kan waɗanda suke musanya shi. Lalle ne, Allah Mai ji ne, Masani. [2.182] To, wanda ya ji tsõron karkata ko kuwa wani zunubi daga mai wasiyyar, sai ya yi sulhi a tsakãninsu to bãbu laifi a kansa. Lalle ne Allah, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [2.183] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! An wajabta(1) azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku, zã ku yi taƙawa, [2.184] Kwanuka ƙidãyayyu. To, wanda ya kasance daga gare ku majinyaci ko kuwa yana a kan tafiya, sai (ya biya) adadi daga wasu kwanuka na dabam. Kuma a kan waɗanda suke yin sa da wahala akwai fansa; ciyar da matalauci, sai dai wanda ya ƙãra alhħri to, shi ne mafi alhħri a gare shi. Kuma ku yi azumi (da wahalar) ne mafi alhħri a gare ku idan kun kasance kuna sani. [2.185] Watan Ramalãna ne wanda aka saukar da Alƙur´ãni a cikinsa yana shiriya ga mutãne da hujjõji bayyanannu daga shiriya da rarrabħwa. To, wanda ya halarta daga gare ku a watan, sai ya azumce shi, kuma wanda ya kasance majinyaci ko kuwa a kan tafiya, sai ya biya adadi daga wasu kwanuka na dabam. Allah Yana nufin sauƙi gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani gare ku, kuma dõmin ku cika adadin, kuma dõmin ku girmama Allah a kan Yã shiryar da ku, kuma tsammãninku, zã ku gõde. [2.186] Kuma idan bãyiNa suka tambaye ka daga gare Ni, to, lalle Ni Makusanci ne. Ina karɓa kiran mai kira idan ya kirã Ni.(2) Sabõda haka su nħmi karɓawaTa, kuma su yi ĩmãni da Ni: tsammãninsu, su shiryu. [2.187] An halatta a gare ku, a daren azumi, yin jima´i(1) zuwa ga matanku, sũ tufa ne a gare ku, kuma kũ tufa ne a gare su, Allah Yã sani lalle ne ku kun kasance kuna yaudarar kanku. Sabõda haka Yã karɓi tũbarku, kuma Yã yãfe muku. To, yanzu ku rungume su kuma ku nħmi abin da Allah yã rubũta muku. Kuma ku ci kuma ku sha har sĩlĩli fari ya bayyana a gare ku daga sĩlĩli baƙi daga alfijiri, sa´an nan kuma ku cika azumi zuwa ga dare. Kuma kada ku rungume su alhãli kuna mãsu itikãfi a cikin masallãtai. Waɗancan iyãkokin Allah ne: don haka kada ku kusancesu, kamar haka ne Allah Yake bayyana ãyõyinSa ga mutãne: tsammãninsu, zã su yi taƙawa. [2.188] Kada ku ci dukiyõyinku(2) a tsakãninku da ƙarya, kuma ku sãdu da ita zuwa ga mahukunta dõmin ku ci wani yanki daga dũkiyõyin mutãne da zunubi alhãli kuwa kũ, kuna sane. [2.189] Kuma suna tambayar ka(3) daga jirajiran wata. Ka ce: "Su lõkatai ne dõmin mutãne da haji, kuma bã addini ba ne ku je wa gidãje daga bãyansu: kuma amma abin da yake addini shi ne wanda ya yi taƙawa. Kuma ku je wa gidãje daga ƙõfõfinsu, kuma ku bi Allah da taƙawa: tsammãninku, ku ci nasara. [2.190] Kuma ku yãƙi waɗanda(4) suke yãƙinku, a cikin hanyar Allah, kuma kada ku yi tsõkana, lalle ne Allah bã Ya son mãsu tsõkana. [2.191] Kuma ku yãƙe su inda kuka sãme su, kuma ku fitar da su daga inda suka fitar da ku. Kuma fitina ita ce mafi tsanani daga kisa. Kuma kada ku yãƙe su a wurin Masallãci Tsararre (Hurumin Makka) fãce fa idan sun yãƙe ku a cikinsa. To, idan sun yãƙe ku, sai ku yãƙe su. Kamar wancan ne sakamakon kãfirai yake. [2.192] Sa´an nan idan sun hanu, to, lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [2.193] Kuma ku yãƙe(1) su har ya zama wata fitina bã zã ta kasance ba, kuma addini ya zama na Allah. Sa´an nan idan sun hanu to bãbu tsõkana fãce a kan azzãlumai. [2.194] Watan alfarma da wani watan alfarma alfarmõmi mãsu dũkar jũna ne. Sabõda haka wanda ya yi tsõkana a kanku, sai ku yi tsokana a kansa da misãlin abin da ya yi tsõkana a kanku. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cħwa lalle ne, Allah Yana tãre da mãsu taƙawa. [2.195] Kuma ku ciyar(2) a cikin hanyar Allah. Kuma kada ku jefa kanku da hannayenku, zuwa ga halaka. Kuma ku kyautata; lalle ne, Allah Yana son mãsu kyautatãwa. [2.196] Kuma ku cika(3) hajji da umra dõmin Allah. To idan an kange ku, to, ku bãyar da abin da ya sauƙaƙa na hadaya. Kuma kada ku aske kãwunanku, sai hadaya ta kai wurinta. To, wanda ya kasance majinyaci daga cikinku, kõ kuwa akwai wata cũta daga kansa (ya yi aski) sai fansa (fidiya) daga azumi ko kuwa sadaka ko kuwa yanka. To, idan kuna cikin aminci to, wanda ya ji dãdi da umra zuwa haji, sai ya biya abin da ya sauƙaƙa daga hadaya, sa´an nan wanda bai sãmu ba, sai azumin yini uku a cikin haji da bakwai idan kun kõma, waɗancan gõma ne cikakku. Wancan yana ga wanda iyãlinsa ba su kasance mazaunan Masallãci Tsararre ba. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cewa Allah Mai tsananin uƙũba ne. [2.197] Hajji watanni ne sanannu. To, wanda ya yi niyyar hajji(1) a cikinsu to bãbu jimã´i kuma bãbu fãsiƙanci, kuma bãbu jãyayya a cikin hajji. Kuma abin da kuka aikata daga alhħri, Allah Ya san shi. Kuma ku yi guzuri. To, mafi alhħrin guzuri yin taƙawa. Kuma ku bi Ni da taƙawa, ya ma´abuta hankula. [2.198] Bãbu laifi a kanku ga ku nħmi falala daga Ubangijinku. Sa´an nan idan kun malãlo daga Arafãt, sai ku yi ta ambatar Allah a wurin Mash´aril Harãmi kuma ku tuna Shi kamar shiriyar da Ya yi muku kuma lalle ne kun kasance a gabãninsa, haƙĩƙa, daga ɓatattu. [2.199] Sa´an nan kuma ku malãlo daga inda mutãne suke malalowa. Kuma ku nemi gafara ga Allah. Lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [2.200] To, idan kun ƙãre ayyukan hajji, sai ku ambaci Allah kamar ambatarku ga ubanninku, kõ kuwa mafi tsanani ga ambato. To, daga cikin mutãne akwai wanda yake cħwa: "Ya Ubangjinmu! Ka bã mu a cikin dũniya! Kuma bã ya da wani rabo a cikin Lãhira. [2.201] Kuma daga gare su akwai wanda yake cħwa: "Yã Ubangijinmu! Ka bã mu mai kyau a cikin dũniya da mai kyau a cikin Lãhira, kuma Ka tsare mana azãbar Wuta!" [2.202] Waɗannan suna da rabo daga abin da suka sanã´anta; kuma Allah Mai gaggãwar sakamako da yawa ne. [2.203] Kuma ku ambaci Allah a cikin kwanuka ƙidayayyu.(1) To, wanda ya yi gaggawa a cikin kwana biyu, to, bãbu laifi a kansa, kuma wanda ya jinkirta, to, bãbu laifi a kansa, ga wanda ya yi taƙawa. Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma ku sani cewa lalle ne kũ, zuwa gare Shi ake tãrã ku. [2.204] Kuma akwai daga mutãne(2) wanda maganarsa tana bã ka sha´awa a cikin rãyuwar dũniya, alhãli yanã shaidar da Allah a kan abin da yake cikin zuciyarsa, kuma shi mai tsananin husũma ne. [2.205] Kuma idan ya jũya sai ya yi gaggawa a cikin ƙasa dõmin ya yi ɓarna a cikinta, kuma ya halaka shũka da ´ya´yan dabbõbi. Kuma Allah bã Ya son ɓarna. [2.206] Kuma idan an ce masa: "Ka ji tsõron Allah," sai girman kai da yin zunubi ya ɗauke shi. To abin da yake mai isarsa Jahannama ce. Kuma haƙĩƙa, shimfiɗa tã munana. [2.207] Kuma akwai daga mutãne(3) wanda yake sayar da ransa, dõmin nħman yardar Allah: Kuma Allah Mai tausayi ga bãyi ne. [2.208] Yã ku waɗanda suka yi ĩmani! Ku shiga cikin Musulunci gabã ɗaya; kuma kada ku bi zambiyõyin Shaiɗan; lalle ne shĩ a gare ku maƙiyine, bayyananne. [2.209] To, idan kun karkace daga bayan hujjõji bayyanannu sun zo muku to ku sani cħwa lalle ne Allah, Mabuwãyi ne, Mai hikima. [2.210] Shin suna jira, fãce dai Allah Ya je musu a cikin wasu inuwõyi na girgije, da malã´iku, kuma an hukunta al´amarin? Kuma zuwa ga Allah al´amurra ake mayar da su. [2.211] Ka tambayi Banĩ Isrã´ila, da yawa Muka bã su daga ãyõyi bayyanannu. Kuma wanda ya musanya ni´imar Allah daga bãyan tã je masa, to, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne. [2.212] An ƙawata rãyuwar dũniya ga waɗanda suka kãfirta, kuma suna izgili daga waɗanda suka yi ĩmãni, alhãli waɗanda suka yi taƙawa suna bisa gare su, a Rãnar Ƙiyãma. Kuma Allah Yana azurta wanda Yake so, bã da lissãfi ba. [2.213] Mutãne sun kasance al´umma guda. Sai Allah Ya aiki annabãwa suna mãsu bãyar da bishãra kuma mãsu gargaɗi; kuma Ya saukar da Littãfi da gaskiya tãre da su dõmin (Littãfin) ya yi hukunci a tsakãnin mutãnen a cikin abin da suka sãɓã wa jũna a cikinsa. kuma bãbu wanda ya sãɓã, a cikinsa, fãce waɗanda aka bai wa shi daga bãyan hujjõji bayyanannu sun je musu dõmin zãlunci a tsakãninsu. Sai Allah Ya shiryar da waɗanda suka yi ĩmani ga abin da suka sãɓã a cikinsa daga gaskiya da izninSa. Kuma Allah Yana shiryar da wanda Yake so, zuwa ga hanya madaidaiciya. [2.214] Ko kuna zaton ku shiga Aljanna kuma tun misãlin waɗanda suka shige daga gabãninku bai zo muku ba? Wahalõli da cũta sun shãfe su, kuma aka tsõratar da su har manzonsu da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi su ce: "Yaushe taimakon Allah zai zo?" To! Lalle ne, taimakon Allah yana kusa! [2.215] Suna tambayar ka mħne ne zã su ciyar. Ka ce: Abin da kuka ciyar daga alhħri sai ga mahaifa(1) da mafi kusantar dangantaka da marãyu da matalauta da ɗan hanya. Kuma abin da kuka aikata daga alhħri, to, lalle ne, Allah gare shi Masani ne. [2.216] An wajabta(1) yãƙi a kanku, alhãli kuwa shi abin ƙi ne a gare ku, akwai fãtar cħwa ku ƙi wani abu, alhãli shi ne mafi alhħri a gare ku, kuma akwai fãtar cħwa kuna son wani abu alhãli kuwa shi ne mafi sharri a gare ku. Kuma Allah ne Yake sani, kuma kũ ba ku sani ba. [2.217] Suna tambayar ka game da Watan Alfarma: yin yãki a cikinsa. Ka ce: "Yin yãƙi a cikinsa babban zunubi ne, kuma hani daga hanyar Allah, da kuma kãfirci da Shi, da kuma da Masallaci Tsararre, da Kuma fitar da mutãnensa daga gare shi, shi ne mafi girman zunubi a wurin Allah." Kuma fitina ita ce mafi girma daga kisa. Kuma bã su gushħwa suna yãƙinku har su mayar da ku daga barin addininku idan za su iya. Kuma wanda ya yi ridda daga gare ku ga barin addininsa har ya mutu alhãli kuwa yana kãfiri, to, waɗannan ayyukansu sun ɓãci a cikin dũniya da Lãhira. Kuma waɗannan abõkan Wuta ne, sũ a cikinta madawwama ne. [2.218] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, da waɗanda suka yi hijira kuma suka yi jihãdi a cikin hanyar Allah waɗannan suna fãtar (sãmun) rahamar Allah kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [2.219] Suna tambayar ka game da giya da cãcã.(2) Ka ce: "A cikinsu akwai zunubi mai girma da wasu amfãnõni ga mutãne, kuma zunubinsu ne mafi girma daga amfaninsu." Kuma suna tambayar ka mħne ne zã su ciyar; ka ce: "Abin da ya rage."(3) Kamar wancan ne Allah Yake bayyanawar ãyõyi a gare ku; tsammãninku, kuna tunãni. [2.220] A cikin dũniya da Lãhira. Kuma suna tambayar ka game da marãyu.(1) Ka ce: "Kyautatãwa gare su ne mafi alhħri, kuma idan kun haɗa da su (wajen abinci), to, ´yan´uwanku ne; kuma Allah Yana sanin mai ɓãtãwa daga mai kyautatãwa. Kuma dã Allah Yã so, dã Ya tsananta muku. Lalle ne Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima. [2.221] Kuma kada ku auri mãtã(2) mushirikai sai sun yi ĩmãni: Kuma lalle ne baiwa mũmina ita ce mafi alhħri daga ɗiya kãfira, kuma kõ da tã bã ku sha´awa. Kuma kada ku aurar wa maza mushirikai sai sun yi ĩmãni, kuma lalle ne bãwa mũmini shi ne mafi alhħri daga da mushiriki, kuma kõ da yã bã ku sha´awa, waɗannan suna kira ne zuwa ga wuta kuma Allah Yana kira zuwa ga Aljanna da gãfara da izninsa. Kuma Yana bayyana ãyõyinsa ga mutãne; tsammãninsu suna tunãwa. [2.222] Kuma suna tambayar ka game da haila(3) Ka ce: Shi cũta ne. Sabõda haka ku nĩsanci mãta a cikin wurin haila kuma kada ku kusance su sai sun yi tsarki. To, idan sun yi wanka sai ku je musu daga inda Allah Ya umurce ku. Lalle ne Allah Yana son mãsu tũba kuma Yana son mãsu tsarkakħwa. [2.223] Mãtanku gõnaki ne a gare ku,(4) sabõda haka ku je wa gõnakinku yadda kuka so. Kuma ku gabãtar (da alheri) sabõda kanku, ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cħwa lalle ne kũ mãsu haɗuwa da Shi ne. Kuma ka bãyar da bishãra ga mũminai. [2.224] Kuma kada ku sanya(5) Allah kambu ga rantsuwõyinku dõmin kada ku yi wani alhħri, kuma ku yi taƙawa, kuma ku yi wani gyara tsakãnin mutãne, kuma Allah Mai jĩ ne, Masani. [2.225] Allah ba Ya kãmã ku da laifi sabõda yãsasshiya a cikin rantsuwõyinku. Kuma amma Yana kama ku sabõda abin da zukãtanku(1) suka sanã´anta. Kuma Allah Mai gãfara ne, Mai haƙuri. [2.226] Ga waɗanda suke yin rantsuwa(2) daga matansu akwai jinkirin watã huɗu. To, idan sun kõma, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [2.227] Kuma idan sun yi niyyar saki, to, lalle ne, Allah Mai ji ne, Masani. [2.228] Kuma mãtã waɗanda(3) aka saki aurensu, suna jinkiri da kansu tsarki uku. Kuma bã ya halatta a gare su, su ɓõye abin da Allah Ya halitta a cikin mahaifunsu, idan sun kasance suna yin ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Kuma mazan aurensu su ne mafiya haƙƙi ga mayar da su a cikin wancan, idan sun yi nufin gyãrawa. Kuma sũ mãtan suna da kamar abin da yake a kansu, yadda aka sani. Kuma maza suna da wata daraja a kansu (su mãtan). Kuma Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima. [2.229] Saki sau biyu(4) yake, sai a riƙa da alh ħri, ko kuwa a sallama bisa kyautatãwa. Kuma ba ya halatta a gare ku (maza) ku karɓe wani abu daga abin da kuka bã su, fãce fa idan su (ma´auran) na tsõron bã zã su tsayar da iyãkõkin Allah ba. Idan kun (danginsu) ji tsõron bã zã su tsayar da iyãkõkin Allah ba, to, bãbu laifi a kansu a cikin abin da ta yi fansa da shi. Waɗancan iyãkõkin Allah ne sabõda haka kada ku kħtare su. Kuma wanda ya ƙħtare iyãkõkin Allah, to waɗannan su ne azzãlumai. [2.230] Sa´an nan idan ya sake ta (na uku), to, bã ta halatta a gare shi, daga bãya, sai tã yi jima´i da wani miji waninsa. Sa´an nan idan (sãbon mijin, watau na biyu) ya sake ta, to, bãbu laifi a kansu ga su kõma wa (auren) jũna,idan sun (mijin farko da matar) yi zaton cħwa zã su tsayar da iyãkõkin Allah, kuma waɗancan dõkõkin Allah ne Yana bayyana su ga mutãne waɗanda suke sani. [2.231] Kuma idan kun saki mãta, sa´an nan suka isa ga ajalinsu (iddarsu), sai ku riƙe su da alhħri ko ku sallame su da alhħri, kuma kada ku riƙe su a kan cũtarwa dõmin ta tsawaita idda. Kuma wanda ya aikata wancan, to, haƙĩƙa, yã zãlunci kansa. Kuma kada ku riƙi ãyõyin Allah da izgili. Kuma ku tuna ni´imar Allah da abin da Ya saukar a kanku na Littãfi da hikima. Yana yi muku wa´azi da shi. Kuma ku bi Allah da takawa kuma ku sani cewa lalle ne Allah ga dukan kõme Masani ne. [2.232] Kuma idan kuka saki mãta, har suka isa ga ajalinsu (iddarsu), to, kada ku (waliyyansu) hana su, su auri mazansu (da suka sake su) idan sun yarda da jũna a tsakãninsu (tsõhon miji da tsõhuwar mãta) da alhħri. Wancan ana yin wa´azi da shi ga wanda ya kasance daga gare ku yana ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Wancan ne mafi mutunci a gare ku, kuma mafi tsarki. Kuma Allah Yana sani, kuma kũ ba ku sani ba. [2.233] Kuma mãsu haifuwa (sakakku)(1) suna shãyar da abin haifuwarsu shħkara biyu cikakku ga wanda ya yi nufin ya cika shãyarwa. Kuma ciyar da su da tufãtar da su yana a kan wanda aka haifar masa da alhħri. Bã a kallafa wa rai fãce iyãwarsa. Bã a cũtar da uwa game da ɗanta, kuma bã a cũtar da uba game da ɗansa, kuma a kan magãji akwai misãlin wancan. To, idan suka yi nufin yãye, a kan yardatayya daga gare su, da shãwartar jũna, to bãbu laifi a kansu. Kuma idan kun yi nufin ku bãyar da ɗiyanku shãyarwa, to, bãbu laifi a kanku idan kun mĩƙa abin da kuka zo da shi bisa al´ãda. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cħwa lalle ne Allah, ga abin da kuke aikatawa, Mai gani ne. [2.234] Kuma waɗanda suke mutuwa(1) daga gare ku suna barin mãtan aure, mãtan suna jinkiri da kansu wata huɗu da kwãna goma. To, idan sun isa ga ajalinsu, to, bãbu laifi a kanku a cikin abin da suka aikata game da kansu ga al´ãda. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne. [2.235] Kuma bãbu laifi a kanku a cikin abin da kuka gitta(2) da shi daga nħman auren mãtã ko kuwa kuka ɓõye a cikin zukatanku. Allah Ya san cħwa lalle ne ku za ku ambata musu (shi). Kuma amma kada ku yi wa jũna alkawari da shi a ɓõye, fãce dai ku faɗi magana sananniya. Kuma kada ku ƙulla niyyar daurin auren sai littãfin (idda) ya kai ga ajalinsa. Kuma ku sani cħwa lalle ne Allah Yana sanin abin da yake cikin zukatanku, sabõda haka ku ji tsõronsa. Kuma ku sani cewa Allah Mai gãfara ne, Mai haƙuri. [2.236] Kuma bãbu laifi(3) a kanku idan kun saki mãtã matuƙar ba ku shãfe su ba, kuma ba ku yanka musu sadãki ba. Kuma ku bã su kyautar dãɗaɗãwa, a kan mawadãci gwargwadonsa, kuma a kan maƙuntaci gwargwadonsa; dõmin dãɗaɗrwa, da alhħri, wãjibi ne a kan mãsu kyautatãwa. [2.237] Kuma idan kuka sake su daga gabãnin ku shãfe su, alhãli kuwa(4) kun yanka musu sadãki, to, rabin abin da kuka yanka fãce idan sun yãfe, kõ wanda ɗaurin auren yake ga hannunsa ya yãfe. Kuma ku yãfe ɗin ne mafi kusa da taƙawa. Kuma kada ku manta da falala a tsakãninku. Lalle ne Allah ga abin da kuke aikatãwa Mai gani ne. [2.238] Ku tsare(1) lõkatai a kan sallõli da salla mafificiya. Kuma ku tsayu kuna mãsu ƙanƙan da kai ga Allah. [2.239] To, idan kun ji tsõro, to (ku dai yi salla gwargwadon hali) da tafiya ƙasa kõ kuwa a kan dabbobi. Sa´an nan idan kun amince sai ku ambaci Allah, kamar yadda Ya nũna muku abin da ba ku kasance kuna sani ba. [2.240] Kuma waɗanda suke mutuwa(2) daga gare ku, alhãli suna barin mãtan aure, wasiyya ga mãtan aurensu da dãɗaɗãwa zuwa ga shekara guda bãbu fitarwa, to, idan sun fita to bãbu laifi a kanku a cikin abin da suka aikata game da kansu daga abin da aka sani, kuma Allah Mabuwayi ne, Mai hikima. [2.241] Kuma waɗanda aka saki suna da dãɗaɗãwa gwargwadon hãli, wajabce a kan mãsu taƙawa(3) . [2.242] Kamar wancan ne Allah Yake bayyana muku ãyõyinSa; tsammãninku, kuna hankalta. [2.243] Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suka fita(4) daga gidãjensu, alhãli kuwa sũ dubbai ne, dõmin tsõron mutuwa? Sai Allah Ya ce musu: "Ku mutu." Sa´an nan kuma Ya rãyar da su, lalle ne Allah, haƙĩƙa Ma´abũcin falala a kan mutãne ne, kuma amma mafi yawan mutãne bã su gõdħwa. [2.244] Kuma ku yi yãƙi a cikin hanyar Allah, kuma ku sani cħwa lalle ne, Allah Mai jĩ ne, Masani. [2.245] Wãne ne wanda(5) zai bai wa Allah rance, rance mai kyau, dõmin Ya riɓanya masa, riɓanyãwa mai yawa? Kuma Allah Shi ne ke damƙewa, kuma yana shimfiɗawa, kuma zuwa a gare Shi ake mayar da ku. [2.246] Shin, ba ka gani ba zuwa ga wasu mashãwarta(1) daga Bani Isrã´ĩla daga bãyan Mũsã, a lõkacin da suka ce ga wani annabi nãsu: "Naɗã mana sarki, mu yi yãƙi a cikin hanyar Allah." Ya ce: "Ashe, akwai tsammãninku idan an wajabta yãƙi a kanku cħwa bã zã ku yi yãƙin ba?" Suka ce: "Kuma mħne ne a gare mu, ba zã mu yi yãƙi ba, a cikin hanyar Allah, alhãli kuwa, haƙiƙa, an fitar da mu daga gidãjenmu da ɗiyanmu?" To, a lõkacin da aka wajabta yãƙin a kansu, suka jũya, sai kaɗan daga gare su. Kuma Allah Masani ne ga azzãlumai. [2.247] Kuma annabinsu(2) ya ce musu: "Lalle ne, Allah ya naɗa muku Ɗãlũta(3) ya zama sarki." Suka ce: "Yãya ne sarauta zã ta kasance a gare shi, a kanmu, alhãli kuwa mũ ne mafi cancanta da sarauta daga gare shi, kuma ba a bã shi wata wadata ba daga dũkiya?" Ya ce: "Lalle ne, Allah Yã zãɓe shi a kanku, kuma Ya ƙãra masa yalwa a cikin ilmi da jiki. Kuma Allah Yana bãyar da mulkinSa ga wanda Yake so, kuma Allah Mawadaci ne, Masani. [2.248] Kuma annabinsu ya ce musu: "Lalle ne alãmar mulkinSa ita ce akwatin(4) nan ya zo muku, a cikinsa akwai natsuwa daga Ubangijinku da sauran kaya daga abin da Gidan Mũsã da Gidan Hãrũna suka bari malã´iku suna ɗaukarsa. Lalle ne a cikin wancan akwai alãma a gare ku (ta naɗin Ɗãlũta daga Allah ne) idan kun kasance mãsu ĩmãni." [2.249] A lõkacin da Ɗãlũta ya fita(1) da rundunõnin, ya ce: "Lalle ne Allah Mai jarrabarku ne da wani kõgi. To, wanda ya sha daga gare shi, to, ba shi daga gare ni, kuma wanda bai ɗanɗane shi ba to lalle ne shi, yana daga gare ni, fãce, wanda ya kamfata, kamfata guda da hannunsa." Sai suka sha daga gare shi, fãce kaɗan daga gare su. To, a lõkacin da (Ɗãlũta) ya ƙħtare shi, shi da waɗanda suka yi ĩmani tãre da shi, (sai waɗanda suka sha) suka ce: "Babu ĩko a gare mu yau game da Jãlũta da rundunõninsa."Waɗanda suka tabbata cħwa lalle sũ mãsu gamuwa ne da Allah, suka ce: "Da yawa ƙungiya kaɗan ta rinjayi wata ƙungiya mai yawa da iznin Allah, kuma Allah Yana tãre da mãsu haƙuri." [2.250] Kuma a lõkacin da suka(2) bayyana ga Jãlũta da rundunoninsa, suka ce: "Yã Ubangijinmu! Ka zuba haƙuri a kanmu kuma Ka tabbatar da sãwayenmu, kuma Ka taimake mu a kan mutãnen nan kãfirai." [2.251] Sai suka karya su da iznin Allah. Kuma Dãwudu ya kashe Jãlũta, kuma Allah Ya bã shi mulki da hikima kuma Ya sanar da shi daga abin da Yake so. Kuma bã dõmin tunkuɗħwar Allah ga mutãne sãshensu da sãshe ba lalle ne dã ƙasa tã ɓãci; kuma amma Allah Ma´abũcin falala ne a kan tãlikai. [2.252] Waɗancan ayõyin Allah ne: Muna karanta su a kanka da gaskiya: Kuma lalle ne kai, hakĩka, kana daga manzanni. [2.253] Waɗancan manzannin(1) Mun fĩfĩta sãshensu a kan sãshe: Daga cikinsu akwai wanda Allah Ya yi masa magana; kuma Ya ɗaukaka sãshensu da darajõji; kuma Muka bai wa Ĩsã dan Maryama hujjõji bayyanannu, kuma Muka ƙarfafã shi da Rũhi mai tsarki. Kuma dã Allah Yã so dã waɗanda suke daga bãyansu, bã zã su yi yãƙi ba, daga bãyan hujjõji bayyanannu sun je musu. Kuma amma sun sãɓa wa jũna, sabõda haka daga cikinsu akwai wanda ya yi ĩmãni, kuma daga cikin su akwai wanda ya kãfirta. Kuma dã Allah Yã so dã bã zã su yãƙi jũna ba, kuma amma Allah Yana aikata abin da Yake nufi. [2.254] Ya ku waɗanda(2) suka yi ĩmãni! Ku ciyar daga abin da Muka arzuta ku daga gabãnin wani yini ya zo bãbu ciniki a cikinsa kuma bãbu abũta, kuma bãbu cħto, kuma kãfirai sũ ne azzãlumai. [2.255] Allah, bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Rãyayye, Mai tsayuwa da kõme, gyangyaɗi bã ya kãma Shi, kuma barci bã ya kãma Shi, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa. Wane ne wanda yake yin cħto a wurinSa, fãce da izninSa? Yana sanin abin da yake a gaba gare su da abin da yake a bãyansu. Kuma bã su kħwayħwa da kõme daga ilminSa, fãce da abin da Ya so. KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa. Kuma tsare su bã ya nauyayarSa. Kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma. [2.256] Bãbu tĩlastãwa(3) a cikin addini, haƙĩƙa shiriya tã bayyana daga ɓata; Sabõda haka wanda ya kãfirta da Ɗãgũta kuma ya yi ĩmãni da Allah, to, haƙĩƙa, yã yi riƙo ga igiya amintacciya, bãbu yankħwa agare ta. Kuma Allah Mai ji ne, Masani. [2.257] Allah Shi ne Masõyin waɗanda suka yi ĩmãni; Yana fitar da su daga duffai zuwa ga haske, kuma waɗanda suka kãfirta, masõyansu Ɗãgũtu ne; suna fitar da su daga haske zuwa ga duffai. Waɗannan abokan Wuta ne, sũ a cikinta madawwama ne. [2.258] Shin, ba ka gani(1) ba zuwa ga wanda ya yi hujjatayya da Ibrãhĩm a cikin (al´amarin) Ubangijinsa dõmin Allah Yã bã shi mulki, a lõkacin da Ibrãhĩm ya ce: "Ubangijina Shi ne Wanda Yake rãyawa kuma Yana matarwa." Ya ce: "Nĩ ina rãyarwa kuma ina matarwa." Ibrãhĩm ya ce: "To, lalle ne Allah Yana zuwa da rana daga gabas: To, ka zo da ita daga yamma." Sai aka ɗimautar da wanda ya kãfirta. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne azzãlumai. [2.259] Kõ kuwa(2) wanda ya shũɗe a kan wata alƙarya, alhãli kuwa tana wõfintacciya a kan gadãjen rħsunanta. Ya ce: "Yaya Allah zai rãyar da wannan a bãyan mutuwarta." Sai Allah Ya matar da shi, shħkara ɗari; sa´an nan kuma ya tãyar da shi. Ya ce: "Nawa ka zauna?" Ya ce: "Na zauna yini ɗaya ko kuwa rabin yini." Ya ce: "A´a kã zauna shħkara ɗari." To, ka dũba zuwa ga abincinka, da abin shanka, (kõwanensu) bai sãke ba, kuma ka dũba zuwa ga jãkinka, kuma dõmin Mu sanya ka wata ãyã ga mutãne. Kuma ka duba zuwa ga ƙasũsuwa yadda Muke mõtsarda su sa´an nan kuma Mu tufãtar da su, da nãma", To, a lõkacin da (abin) ya bayyana a gare shi, ya ce: "Ina sanin cħwa lalle Allah a kan dukan kõme Mai ĩkõn yi ne." [2.260] Kuma a lõkacin da Ibrãhĩm ya ce: "Ya Ubangijina! Ka nũna mini yadda Kake rãyar da matattu." Ya ce: "Shin, kuma ba ka yi ĩmãni ba?" Ya ce: "Na´am! Kuma amma dõmin zũciyãta, ta natsu." Ya ce: "To ka riƙi huɗu daga tsuntsãye, ka karkatar da su zuwa gare ka, ka yanka su, sa´an nan kuma ka sanya juzu´i daga gare su a kan kõwane dũtse, sa´an nan kuma ka kira su zã su zo maka gudãne. Kuma ka sani cħwa lalle Allah Mabuwãyi ne, Masani." [2.261] Sifar waɗanda suke ciyar da dũkiyõyinsu a cikin hanyar Allah, kamar sifar ƙwãyã ce wadda ta tsirar da zangarniya bakwai, a cikin kõwace zangarniya akwai ƙwãya ɗari. Kuma Allah Yana riɓinyawa ga wanda Ya so. Kuma Allah Mawadãci ne, Masani. [2.262] Waɗanda suke ciyar da dũkiyõyinsu a cikin hanyar Allah, sa´an nan kuma bã su biyar wa abin da suka ciyar ɗin da gõri, ko cũta, suna da sakamakonsu a wurin ubangijinsu, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba. [2.263] Magana mai kyau da gãfartawa su ne mafi alhħri daga sadaka wadda wata cũtarwa take biyar ta. Kuma Allah Wadatacce ne, Mai haƙuri. [2.264] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku ɓãta sadakõkinku da gõri da cũtarwa, kamar wanda yake ciyar da dũkiyarsa dõmin nũna wa mutãne, kuma bã ya yin ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. To, abin da yake misãlinsa, kamar falalen dũtse ne, a kansa akwai turɓãya, sai wãbilin hadari(1) ya sãme shi, sai ya bar shi ƙanƙara. Bã su iya amfani da kõme daga abin da suka sanã´anta. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne kãfirai. [2.265] Kuma sifar waɗanda suke ciyar da dũkiyarsu dõmin nħman yardõjin Allah, kuma da tabbatarwa daga kansu, kamar misãlin lambu ne a jigãwa wadda wãbilin hadari ya sãmu, sai ta bãyar da amfãninta ninki biyu To, idan wãbili bai sãme ta ba, sai yayyafi (ya ishe ta). Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Mai gani ne. [2.266] Shin ɗayanku nã son cħwa wani lambu ya kasance a gare shi daga dabĩnai da inabõbi´ marħmari suna gudãna daga ƙarƙashinsa, yana da, a cikinsa daga kõwane ´ya´yan itãce, kuma tsũfa ya sãme shi, alhãli kuwa yana da zũriyya masu rauni sai gũguwa wadda take a cikinta akwai wuta, ta sãme shi, har ta ƙõne? Kamar wancan ne Allah Yana bayyanãwar ãyõyi a gare ku, tsammãninku kuna tunãni. [2.267] Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku ciyar daga mai kyaun abin da kuka sanã´anta, kuma daga abin da Muka fitar sabõda ku daga ƙasa, kuma kada ku yi nufin mummuna ya zama daga gare shi ne kuke ciyarwa, alhãli kuwa ba ku zama mãsu karɓarsa ba fãce kun runtse ido a cikinsa. Kuma ku sani cħwa lalle ne, Allah Mawadãci ne, Gõdadde. [2.268] Shaiɗan yana yi muku alƙawarin talauci, kuma yana umurnin ku da alfasha,(1) kuma Allah Yana yi muku alƙawarin gãfara daga gare shi da ƙãri, kuma Allah Mawadãci ne, Masani. [2.269] Yana bãyar da hikima (ga fahimtar gaskiyar abubuwa) ga wanda Yake so. Kuma wanda aka bai wa hikima to lalle ne an bã shi alhħri mai yawa. Kuma bãbu mai tunãni fãce ma´abuta hankula. [2.270] Kuma abin da kuka ciyar daga ciyarwa, kõ kuka cika alwãshi daga wani bãkance, to, lalle ne, Allah Yana sanin sa. Kuma azzãlumai bã su da wasu mataimaka. [2.271] Idan kun nũna sadakõki to, yana da kyau ƙwarai kuma idan kuka ɓõye su kuma kuka je da su ga matalauta, to shi ne mafi alhħri a gareku, kuma Yana kankarħwa, daga barinku, daga miyãgun ayyukanku. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne. [2.272] Shiryar da su bã ya a kanka, kuma amma Allah Shi ne Yake shiryar da wanda Yake so, kuma abin da kuka ciyar daga alhħri, to, dõmin kanku ne, kuma bã ku ciyarwa, fãce dõmin nħman yardar Allah, kuma abin da kuke ciyarwa daga alhħri zã a cika lãdarsa zuwa gare ku, alhãli kuwa kũ bã a zãluntarku. [2.273] (Ciyarwar a yĩ ta) ga matalautan(1) nan waɗanda aka tsare a cikin hanyar Allah, ba su iya tafiyar fatauci a cikin ƙasa, jãhilin hãlinsu yana zaton su wadãtattu sabõda kãmun kai kana sanin su da alãmarsu, ba su rõƙon mutãne da nãcħwa. Kuma abin da kuka ciyar daga alhħri, to, lalle Allah gare shi Masani ne. [2.274] Waɗanda suke ciyar da dukiyõyinsu, a dare da yini, ɓõye da bayyane, to suna da sakamakonsu a wurin Ubangijinsu. Kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba. [2.275] Wadanda suke cin ribã(1) ba su tashi, fãce kamar yadda wanda da Shaiɗan yake ɗimautarwa daga shafa yake tashi. Wancan, dõmin lalle ne sun ce: "Ciniki kamar riba yake."Kuma Allah Ya halatta ciniki kuma Ya haramta riba. To, wanda wa´azi daga Ubangijinsa, ya je masa, sa´an nan ya hanu, to yana da abin da ya shige, kuma al´amarinsa (ana wakkala shi) zuwa ga Allah. Kuma wanda ya kõma, to, waɗannan sũ ne abõkan Wuta, sũ a cikinta madawwama ne. [2.276] Allah Yana shãfe albarkar riba, kuma Yana ƙãra sadakõki. Kuma Allah bã Ya son dukan mai yawan kãfirci, mai zunubi. [2.277] Lalle ne, waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka tsayar da salla, kuma suka bãyar da zakka, suna da sakamakonsu a wurin Ubangijinsu, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba. [2.278] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa kuma ku bar abin da ya rage daga riba, idan kun kasance mãsu ĩmãni. [2.279] To, idan ba ku aikata ba to, ku sani fa da akwai yãƙi daga Allah da ManzonSa. Kuma idan kun tũba to kuna da asalin dũkiyõyinku, bã ku zãlunta, kuma bã a zãluntar ku. [2.280] Kuma idan ma´abucin wahala ya kasance (mawahalci) to, jinkirtãwa ake yi zuwa ga sauƙin al´amarinsa, kuma dã kun yi sadaka, shi ne mafi alhħri a gare ku, idan kun kasance kuna sani. [2.281] Kuma ku ji tsõron wani yini wanda ake mayar da ku a cikinsa zuwa ga Allah, sa´an nan kuma a cika wa kõwane rai abin da ya sanã´anta, kuma sũ bã a zãluntar su. [2.282] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi mu´ãmalar bãyar da bãshi zuwa ga wani ajali ambatacce, sai ku rubũta shi. Kuma wani marubuci ya yi rubũtu a tsakaninku da ãdalci. Kuma kada marubũci ya ki rubũtãwa, kamar yadda Allah Ya sanar da shi, sai ya rubũta. Kuma wanda bãshin yake a kansa sai ya yi shibta, kuma ya ji tsõron Allah, Ubangijinsa, da taƙawa, kuma kada ya rage wani abu daga gare shi. To, idan wanda bãshin yake a kansa yã kasance wãwã ne kõ kuwa rarrauna, kõ kuwa shi bã ya iya shibta, to, sai waliyyinsa ya yi shibtar da ãdalci. Kuma ku shaidar da shaidu biyu daga mazanku, to, idan ba su zama maza biyu ba, to, namiji guda da mãtã biyu, daga waɗanda kuke yarda da su daga shaidun dõmin mantuwar ɗayansu, sai gudarsu ta mazãkũtar(1) da ɗayar. Kuma kada shaidun su ƙi, idan an kira su. Kuma kada ku ƙõsa ga rubũta shi, ƙarami ya kasance kõ babba, zuwa ajalinsa. Wancan ne mafi ãdalci a wurin Allah kuma mafi tsayuwa ga shaida, kuma mafi kusa ga rashin shakkarku. Sai idan ya kasance fatauci ne halartacce wanda kuke għwayarwa da shi hannu da hannu a tsakãninku to bãbu laifi a kanku, ya zama ba ku rubũta shi ba. Kuma ku shaidar idan kun yi sayayya. Kuma kada a wahalarda marubuci, kuma kada a wahalar da shaidu kuma idan kun aikata to, lalle ne, shi fãsiƙanci ne game da ku. Kuma ku bi Allah da takƙawa, kuma Allah Ya sanar da ku. Kuma Allah ga dukan kõme Masani ne. [2.283] Kuma idan kun kasance a kan tafiya, kuma ba ku sami marubũci ba, to, a bãyar da jingina karɓaɓɓiya (ga hannu). To, idan sãshenku ya amince wa sãshe, to, wanda aka amincħ wan nan sai ya bãyar da amãnarsa, kuma ya bi Allah, Ubangijinsa, da taƙawa. Kuma kada ku ɓõye shaida, kuma wanda ya ɓõye ta, to, shi mai zunubin zũciyarsa ne. Kuma Allah ga abin da kuke aikatãwa Masani ne. [2.284] Allah ne, da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, kuma idan kun bayyana abin da yake a cikin zukatanku (na shaida), ko kuka ɓõye shi, Allah zai bincike ku da shi, sa´an nan Ya yi gãfara ga wanda Yake so, kuma Ya azabta wanda Yake so. Kuma Allah a kan dukan kõme Mai ĩkon yi ne.(1) [2.285] Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala´ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabħwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã´a; (Muna nħman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take(2) " [2.286] Allah ba Ya kallafa wa rai fãce ikon yinsa, yana da lãdar abin da ya tsirfanta, kuma a kansa akwai zunubin abin da ya yi ta aikatãwa: "Yã Ubangijinmu! Kada Ka kãmã mu, idan mun yi mantuwa, ko kuma mun yi kuskure. Yã Ubangijinmu! Kuma kada Ka aza nauyi a kanmu, kamar yadda Ka aza shi a kan waɗanda suke a gabãninmu. Yã Ubangijinmu! Kada Ka sanya mu ɗaukar abin da bãbu ĩko gare mu da shi. Kuma Ka yãfe daga gare mu, kuma Ka gãfarta mana, kuma Ka yi jin ƙai gare mu. Kai ne Majibincinmu, sabõda haka Ka taimake mu a kan mutãnen nan kãfirai." @ALI 'IMRAN Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [3.1] A. L̃.M̃. [3.2] Allah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye Mai tsayuwa da kõme. [3.3] Yã sassaukar da Littãfi a gare ka da gaskiya, yana mai gaskatãwa ga abin da ke gaba gare shi, kuma Allah Yã saukar da Attaura da Linjĩlã. [3.4] A gabãni, suna shiryar da mutãne, kuma Ya saukar da littattafai mãsu rarrabħwa. Lalle ne waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Allah, suna da azãba mai tsanani. Kuma Allah Mabuwayi ne, Ma´abucin azãbar rãmuwa. [3.5] Lalle ne, Allah bãbu wani abin da ke ɓõyuwa gare Shi a cikin ƙasa, kuma bãbu a cikin sama. [3.6] Shi ne wanda Yake suranta ku a cikin mahaifu yadda Yake so. Bãbu abin bautãwa fãce Shi Mabuwãyi, Mai hikima. [3.7] Shi ne wanda ya saukar da Littãfi a gare ka, daga cikinsa akwai ãyõyi bayyanannu, su ne mafi yawan Littãfin, da wasu mãsu kamã da jũna. To, amma waɗanda yake a cikin zukãtansu akwai karkata sai suna bin abin da yake da kamã da jũna daga gare shi, dõmin nħman yin fitina da tãwĩlinsa. Kuma bãbu wanda ya san tãwĩlinsa fãce Allah. Kuma matabbata a cikin ilmi sunã cħwa: "Mun yi ĩmãni da Shi; dukkansa daga wurin Ubangijinmu yake." Kuma bãbu mai tunãni fãce ma´abũta hankula. [3.8] Yã Ubangijinmu! Kada Ka karkatar da zukãtanmu bãyan har Kã shiryar da mu, kuma Ka bã mu rahama daga gunKa. Lalle ne, Kai, Kai ne Mai yawan kyauta. [3.9] "Yã Ubangijimu! Lalle ne Kai, Mai tãra mutãne ne dõmin wani yini wanda bãbu shakka a gare shi, Lalle ne Allah bã Ya sãɓãwar lõkacin alkawari." [3.10] Lalle ne waɗanda suka kãfirta, dũkiyõyinsu bã su tunkuɗe musu kõme daga Allah, kuma ´ya´yansu bã su tunkuɗħwa, kuma waɗannan, sũ ne makãmashin wuta. [3.11] Kamar ɗabi´ar mutãnen Fir´auna da waɗanda ke a gabãninsu, sun ƙaryata ãyõyinMu, sai Allah Ya kãmã su sabõda zunubansu, kuma Allah Mai tsananin uƙũba ne. [3.12] Ka ce wa waɗanda suka kãfirta: "Za a rinjãye ku, kuma a tãraku zuwa Jahannama, kuma shimfiɗar tã mũnana! [3.13] "Lalle ne wata ãyã tã kasance a gare ku a cikin ƙungiyõyi biyu da suka haɗu; ƙungiya guda tana yãƙi a cikin hanyar Allah, da wata kãfira, suna ganin su ninki biyu nãsu, a ganin ido. Kuma Allah Yana ƙarfafa wanda Yake so da taimakonSa. Lalle ne a cikin wannan, hakĩƙa, akwai abin kula ga maabũta basĩra. [3.14] An ƙawata wa mutãne son sha´awõyi daga mãtã da ɗiya da dũkiyõyi abũbuwan tãrãwa daga zinariya da azurfa, da dawãki kiwãtattu da dabbõbin ci da hatsi. Wannan shi ne dãɗin rãyuwar dũniya. Kuma Allah a wurinsa kyakkyãwar makõma take. [3.15] Ka ce: Shin kuma, in gaya muku mafi alhħri daga wannan? Akwai gidãjen Aljanna a wurin Ubangiji sabõda waɗanda suka bi Shi da taƙawa, kõguna suna gudãna daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu, da mãtan aure tsarkakakku, da yarda daga Allah. Kuma Allah Mai gani ne ga bãyinSa. [3.16] Waɗanda suke cħwa: "Ya Ubangijinmu! Lalle ne mu, mun yi ĩmãni, sai Ka gãfarta mana zunubanmu kuma Ka tsare mu daga azãbar wuta." [3.17] Mãsu haƙuri, da mãsu gaskiya, da mãsu ƙanƙan da kai, da mãsu ciyarwa da mãsu istingifari a lõkutan asuba. [3.18] Allah Ya shaida cħwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma´abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima. [3.19] Lalle ne, addini a wurin Allah, Shi ne Musulunci. Kuma waɗanda aka bai wa Littafi ba su sãɓã ba, fãce a bãyan ilmi ya je musu, bisa zãlunci a tsakãninsu. Kuma wanda ya kãfirta da ãyõyin Allah, to, lalle ne Allah Mai gaugãwar sakamako ne. [3.20] To, idan sun yi musu da kai, sai ka ce: "Nã sallama fuskata ga Allah, kuma wanda ya bi ni (haka)." Kuma ka ce wa waɗanda aka bai wa littãfi da Ummiyyai:(1) "Shin kun sallama?" To, idan sun sallama, haƙĩƙa, sun shiryu kuma idan sun jũya, to, kawai abinda ke kanka, shi ne iyarwa. Kuma Allah Mai gani ne ga bãyinSa. [3.21] Lalle ne waɗanda suke kãfirta da ãyõyin Allah, kuma suna kashe Annabãwa bã da wani hakki ba, kuma suna kashe waɗanda ke umurni da yin ãdalci daga mutãne, to, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi. [3.22] Waɗannan ne waɗanda ayyukansu suka ɓãci a cikin dũniya da Lãhira, kuma bã su da wasu mataimaka. [3.23] Shin, ba ka ga waɗanda aka bai wa rabo daga littãfi ba ana kiran su zuwa ga Littãfin Allah dõmin ya yi hukunci a tsakãninsu sa´an nan wata ƙungiya daga cikinsu ta jũya bãya, kuma sunã mãsu bijirħwa? [3.24] Wannan kuwa, dõmin lalle ne su sun ce: "Wutã bã zã ta shãfe mu ba, fãce a ´yan kwãnaki ƙidãyayyu." Kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa na ƙarya ya rũɗħ su a cikin addininsu. [3.25] To, yãya idan Mun tãra su a yini wanda bãbu shakka a cikinsa, kuma aka cikã wa kõwane rai sakamakon abin da ya tsirfanta, alhãli kuwa, sũ bã zã a zãlunce su ba? [3.26] Ka ce:(1) "Yã Allah Mamallakin mulki, Kanã bayar da mulki ga wanda Kake so, Kanã zãre mulki daga wanda Kake so, kuma Kanã buwãyar da wanda Kake so, kuma Kanã ƙasƙantar da wanda Kake so, ga hannunKa alhħri yake. Lalle ne Kai, a kan kõwane abu, Mai ĩkon yi ne." [3.27] "Kanã shigar da dare a cikin yini, kuma Kanã shigar da yini a cikin dare, kuma Kana fitar da mai rai daga mamaci, kuma Kanã fitar da mamaci daga mai rai, kuma Kanã azurta wanda Kake so bã da lissafi ba.". [3.28] Kada mũminai su riƙi kãfirai masõya, baicin mũminai. Kuma wanda ya yi wannan, to, bai zama a cikin kõme ba daga Allah, fãce fa dõmin ku yi tsaro daga gare su da ´yar kãriya. Kuma Allah yana tsõratar da ku kanSa. Kuma zuwa ga Allah makõma take. [3.29] Ka ce: "Idan kun ɓõye abin da ke a cikin ƙirãzanku, kõ kuwa kun bayyana shi, Allah Yana sanin sa. Kuma Yana sanin abin da ke a cikin sammai da ƙasa. Kuma Allah a kan kõwane abu Mai ĩkon yi ne." [3.30] A Rãnar da kõwane rai yake sãmun abin da ya aikata daga alhħri, a halarce, da kuma abin da ya aikata daga sharri, alhãli yana gũrin, dã dai lalle a ce akwai fage mai nĩsa a tsakãninsa da abin daya aikata na sharrin! Kuma Allah Yanã tsõratar da kũ kanSa. Kuma Allah Mai tausayi ne ga bãyinSa. [3.31] Ka ce: "Idan kun kasance kunã son Allah to, ku bĩ ni, Allah Ya sõ ku, kuma Ya gãfarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai." [3.32] Ka ce: "Ku yi ɗã´a ga Allah da Manzo." To, amma idan sun jũya bãya, to, lalle ne Allah bã Ya son kãfirai. [3.33] Lalle ne Allah Yã zãɓi Ãdama da Nũhu da Gidan Ibrãhĩma da Gidan Imrãna a kan tãlikai. [3.34] Zuriyya ce sãshensu(1) daga sãshe, kuma Allah Mai ji ne, Masani. [3.35] A lõkacin da mãtar Imrãna(2) ta ce: "Ya Ubangijina! Lalle ni, nã yi bãkancen abin da ke cikin cikĩna gare Ka; ya zama ´yantacce, sai Ka karɓa daga gare ni. Lalle ne Kai, Kai ne Mai ji, Masani." [3.36] To, a lõkacin da ta haife ta sai ta ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne nĩ, nã haife ta mace!"Kuma Allah ne Mafi sanin abin da ta haifa." Kuma namiji bai zama kamar mace ba. Kuma nĩ nã yi mata suna Maryamu(3) kuma lalle ne ni, ina nħma mata tsari gare Ka, ita da zũriyarta daga Shaiɗan jħfaffe." [3.37] Sai Ubangijinta Ya karɓe ta karɓa mai kyau. Kuma Ya yabanyartar da ita yabanyartarwa mai kyau, kuma Ya sanya rħnonta ga Zakariyya. Ko da yaushe Zakariyya ya shiga masallãci, a gare ta, sai ya sãmi abinci a wurinta. (Sai kuwa) ya ce: "Yã Maryamu! Daga ina wannan yake gare ki?" (Sai) ta ce: "Daga wurin Allah yake. Lalle ne Allah yana azurta wanda Ya so ba da lissafi ba." [3.38] A can ne Zakariyya ya rõki Ubangijinsa, ya ce: "Ya Ubangijina! Ka bã ni zuriyya mai kyau daga gunKa. Lalle ne Kai Mai jin addu´a Kake." [3.39] Sai malã´iku suka kirãye shi, alhãli kuwa shĩ yanã tsaye yana salla a cikin masallãci. (Suka ce), "Lalle ne Allah yana bã ka bushãra da Yahaya, alhãli yana mai gaskatãwar wata kalma daga Allah, kuma shugaba, kuma tsarkakke kuma annabi daga sãlihai." [3.40] Ya ce: "Yã Ubangijina! Yãya yãro zai sãmu a gare ni, alhãli kuwa, lalle tsũfa ya sãme ni,kuma mãtãta bakarãriya ce?" Allah ya ce, "Kamar hakan ne, Allah yana aikata abin da Yake so." [3.41] Ya ce: "Yã Ubangijinã! Ka sanya mini wata alãma!" (Allah) Ya ce "Alãmarka ita ce ba zã ka iya yi wa mutãne magana ba har yini uku face da ishãra. Sai ka ambaci Ubangijinka da yawa. Kuma ka yi tasbĩhi da marece da sãfe." [3.42] Kuma a lõkacin da malã´iku suka ce: "Ya Maryamu! Lalle ne, Allah Ya zãɓe ki, kuma Ya tsarkake ki, kuma Ya zaɓe ki a kan mãtan tãlikai." [3.43] "Yã Maryamu! Ki yi ƙanƙan da kai ga Ubangijinki, kuma ki yi sujada, kuma ki yi rukũ´i tãre(1) da mãsu rukũ´i." [3.44] Wannan yana daga lãbarun(2) gaibi, Munã yin wahayinsa zuwa gare ka (Muhammadu). Ba ka kasance ba a wurinsu a lõkacin da suke jħfa alƙalumansu (domin ƙuri´a) wãne ne zai yi rħnon Maryam. Kuma ba ka kasance a wurinsu ba a lõkacin da suke ta yin husũma(3) . [3.45] A lõkacin da malã´iku suka ce "Yã Maryamu! Lalle ne Allah Yana bã ki bushãra da wata kalma daga gare Shi; sũnansa Masĩhu ĩsa ɗan Maryama, yana mai daraja a dũniya da Lãhira kuma daga Makusanta. [3.46] "Kuma yana yi wa mutãne magana a cikin shimfiɗar jariri, da kuma lõkacin da yana dattijo, kuma yana daga sãlihai." [3.47] Ta ce: "Yã Ubangijina! Yãya yãro zai kasance a gare ni, alhãli kuwa wani mutum bai shãfe ni ba?" (Allah) Ya ce: "Kamar wannan ne, Allah yana halittar abin da Yake so. Idan Ya hukunta wani al´amari, sai ya ce masa, "Ka kasance!, Sai yana kasancħwa." [3.48] Kuma Ya sanar da shi rubũtu da hikima da Taurata da injĩla. [3.49] Kuma (Ya sanya shi) manzo zuwa ga Bani Isrãila´ĩla (da sãko, cħwa), Lalle ne, ni haƙĩƙa nã zõ muku da wata ãyã daga Ubangijinku. Lalle ne ni ina halitta muku daga lãka, kamar siffar tsuntsu sa´an nan in hũra a cikinsa, sai ya kasance tsuntsu, da izinin Allah. Kuma ina warkar da wanda aka haifa makãho da kuturu, kuma ina rãyar da matattu, da izinin Allah. Kuma ina gayã muku abin da kuke ci da abin da kuke ajiyħwa acikin gidãjenku. Lalle ne, a cikin wannan akwai ãyã a gare ku, idan kun kasance mãsu yin ĩmãni. [3.50] "Kuma inã mai gaskatãwa ga abin da yake a gabãnina daga Taurata. Kuma (nãzo) dõmin in halatta muku sãshen abin da aka haramta muku. Kuma nã tafo muku da wata ãyã daga Ubangijinku. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã´ã. [3.51] "Lalle Allah shi ne Ubangijina, kuma Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Wannan ce hanya madaidaiciya." [3.52] To, a lõkacin da Ĩsa ya gane kãfirci daga gare su, sai ya ce: "Su wãne ne mataimakãna zuwa ga Allah?" Hawãriyãwa suka ce: "Mu ne mataimakan Allah. Mun yi ĩmani da Allah. Kuma ka shaida cħwa lalle ne mu, mãsu sallamãwa ne. [3.53] "Yã Ubangijinmu! Mun yi imãni da abin da Ka saukar, kuma mun bi ManzonKa, sai Ka rubũta mu tãre da mãsu shaida.(1) . [3.54] Kuma (Kãfirai) suka yi mãkirci, Allah kuma Ya yi musu (sakamakon) makircin, kuma Allah ne Mafi alhħrin mãsu sãka wa mãkirci. [3.55] A lõkacin da Ubangiji Ya ce: "Ya Ĩsa! Lalle NĨ Mai karɓar ranka ne, kuma Mai ɗauke ka ne zuwa gare Ni, kuma Mai tsarkake ka daga waɗanda suka kãfirta, kuma Mai sanya waɗanda suka bĩ ka a bisa waɗanda suka kãfirta har Rãnar Ƙiyãma. Sa´an nan kuma zuwa gare Ni makõmarku take, sa´an nan in yi hukunci a tsakãninku, a cikin abin da kuka kasance kuna sãɓã wa jũna. [3.56] "To, amma waɗanda suka kãfirta sai In azabta su da azãba mai tsanani, a cikin dũniya da Lãhira, kuma bã su da wasu mãsu taimako. [3.57] Kuma amma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sai (Allah) Ya cikã musu ijãrõrinsu. Kuma Allah bã Ya son azzãlumai. [3.58] "Wannan Muna karanta shi a gare ka (Muhammad) daga ãyõyi, da Tunatarwa mai hikima (Alƙur´ãni)." [3.59] Lalle ne misãlin Ĩsã a wurin Allah kamar misãlin Ãdama ne, (Allah) Yã halitta shi daga turɓãya, sa´an nan kuma Ya ce masa: "Ka kasance: "Sai yana kasancewa. [3.60] Gaskiya daga Ubangijinka take sabõda haka kada ka kasance daga mãsu shakka. [3.61] To, wanda ya yi musu(2) da kai a cikinsa, a bãyan abin da ya zo maka daga ilmi, to ka ce: "Ku zo mu kirãyi, ´yã´yanmu da ´yã´yanku da mãtanmu da mãtanku da kanmu da kanku sa´an nan kuma mu ƙanƙantar da kai sa´an nan kuma mu sanya la´anar Allah a kan maƙaryata." [3.62] Lalle ne wannan, haƙĩƙa, shi ne lãbãri tabbatacce, kuma bãbu wani abin bautawa fãce Allah, kuma lalle ne, Allah, haƙĩƙa,Shi ne Mabuwãyi Mai hikima. [3.63] To, idan sun jũya bãya, to, lalle Allah Masani ne ga maɓannata. [3.64] Ka ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi!(1) Ku tafo zuwa ga kalma mai daidaitãwa(2) a tsakãninmu da ku; kada mu bauta wa kõwa fã ce Allah. Kuma kada mu haɗa kõme da Shi, kuma kada sãshenmu ya riƙi sãshe Ubangiji, baicin Allah." To, idan sun jũya bãya sai ku ce: "ku yi shaida cħwa, lalle ne mu masu sallamã wa ne." [3.65] Yã Mutãnen Littãfi! Don me kuke hujjacħwa a cikin sha´anin lbrãhĩma, alhãli kuwa ba a saukar da Attaura da injĩla ba fãce daga bãyansa? Shin bã ku hankalta? [3.66] Gã ku yã waɗannan! Kun yi hujjacħwa a cikin abin da yake kunã da wani ilmi game da shi, to, don me kuma kuke yin hujjacħwa a cikin abin da bã ku da wani ilmi game da shi? Allah yana sani, kuma kũ, ba ku sani ba! [3.67] Ibrãhĩma bai kasance Bayahũde ba, kuma bai kasance Banasãre ba, amma yã kasance mai karkata zuwa ga gaskiya, mai sallamãwa, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba. [3.68] Lalle ne mafi hakkin mutãne da Ibrãhĩma haƙĩƙa, sũ ne waɗanda suka bi shi a (zamaninsa) da wannan Annabi (Muhammadu) da waɗanda suka yi ĩmãni. Kuma Allah ne Majiɓincin mũminai. [3.69] Wata ƙungiya daga Mutãnen Littãfi sun yi gũrin su ɓatar da ku, to, ba su ɓatar da kõwa ba fãce kansu, kuma bã su sansancewa! [3.70] Yã Mutãnen Littãfi! Don me kuka kãfirta da ãyõyin Allah, alhãli kuwa kũ, kuna shaida (cħwa sũ gaskiya ne)? [3.71] Yã Mutãnen Littãfi! Don me kuke lulluɓe gaskiya da ƙarya, kuma kuke ɓõye gaskiya, alhãli kuwa kuna sane? [3.72] Kuma wata ƙungiya daga Mutãnen Littãfi ta ce: "Ku yi ĩmãni da abin da aka saukar a kan waɗanda suka yi ĩmãni (da Muhammadu) a farkon yini, kuma ku kãfirta a ƙarshensa; tsammãninsu, zã su kõmõ." [3.73] "Kada ku yi ĩmãni fãce(1) da wanda ya bi addininku." Ka ce: "Lalle ne, shiriya ita ce shiriyar Allah. (Kuma kada ku yi ĩmãni) cħwa an bai wa wani irin abin da aka bã ku, kõ kuwa su yi musu da ku a wurin Ubangijinku." Ka ce: "Lalle ne falala ga hannun Allah take, yana bãyar da ita ga wanda Yake so, kuma Allah Mawadãci ne, Masani." [3.74] Yanã keɓance wanda Ya so da rahamarSa, kuma Allah Ma´abucin falala ne, Mai girma. [3.75] Kuma daga Mutãnen Littãfi akwai wanda yake idan ka bã shi amãnar kinɗãri(2) , zai bãyar da shi gare ka, kuma daga gare su akwai wanda idan ka bã shi amãnar dĩnari, bã zai bãyar da shi gare ka ba, fãce idan kã dawwama a kansa kanã tsaye. Wannan kuwa, dõmin lalle ne sũ sun ce, "Bãbu laifi a kanmu a cikin Ummiyyai."(3) Suna faɗar ƙarya ga Allah, alhãli kuwa suna sane. [3.76] Na´am! Wanda ya cika alkawarinsa, kuma ya yi taƙawa, to, lalle ne Allah yana son mãsu taƙawa. [3.77] Lalle ne waɗanda suke sayen ´yan tamani kaɗan da alkawarin Allah da rantsuwõyinsu, waɗannan bãbu wani rabo a gare su a Lãhira, Kuma Allah bã Ya yin magana da su, kuma bã Ya dũbi zuwa gare su, a Rãnar Ƙiyãma, kuma bã Ya tsarkake su, kuma sunã da azãba mai raɗaɗi. [3.78] Kuma lalle ne, daga gare su akwai wata ƙungiya suna karkatar da harsunansu da Littãfi dõmin ku yi zaton sa daga Littãfin, alhãli kuwa bã shi daga Littãfin. Kuma suna cħwa: "Shi daga wurin Allah yake." Alhãli kuwa shi, bã daga wurin Allah yake ba. Sunã faɗar ƙarya ga Allah, alhãli kuwa sunã sane. [3.79] Ba ya yiwuwa ga wani mutum, Allah Ya bã shi Littãfi da hukunci da Annabci, sa´an nan kuma ya ce wa mutãne: "Ku kasance bãyi gare ni, baicin Allah." Amma (zai ce): "Ku kasance mãsu aikin ibãda da abin da kuka kasance kuna karantar da Littãfin, kuma da abin da kuka kasance kuna karantãwa(1) ." [3.80] Kuma ba ya umurnin ku da ku riƙi malã´iku da annabãwa lyãyengiji. Shin, zai umurce ku da kãfirci ne a bãyan kun riga kun zama mãsu sallamãwa (Musulmi)? [3.81] Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabãwa: "Lalle ne ban bã ku wani abu ba daga Littãfi da hikima, sa´an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku; lalle ne zã ku gaskata Shi, kuma lalle ne zã ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawarĩNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Nĩ a tãre da ku Inã daga mãsu shaida." [3.82] To, waɗanda kuma suka jũya bãya a bãyan wannan, to, waɗannan sũ ne fãsiƙai. [3.83] Shin wanin Addinin Allah suke nħma, alhãli kuwa a gare Shi ne waɗanda ke cikin sama da ƙasa suka sallama wa, a kan sõ da ƙĩ, kuma zuwa gare Shi ake mayar da su? [3.84] Ka ce: "Mun yi ĩmãni da Allah kuma da abin da aka saukar mana da abin da aka saukar wa Ibrãhĩma da Isma´ĩla da Is´hãƙa da Yãƙũba da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da ĩsã da annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu bambantãwa a tsakãnin kõwa daga gare su. Kuma mũ, zuwa gare Shi mãsu sallamãwa ne." [3.85] Kuma wanda ya nħmi wanin Musulunci ya zama addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra. [3.86] Yãya Allah zai shiryar da mutãne waɗanda suka kãfirta a bãyan ĩmãninsu, kuma sun yi shaidar cħwa, lalle Manzo gaskiya ne, kuma hujjõji bayyanannu sun je musu? Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai. [3.87] Waɗannan, sakamakonsu shi ne, lalle a kansu akwai la´anar Allah da mãla´iku da mutãne gabã ɗaya. [3.88] Sunã mãsu dawwama a cikinta, bã a sauƙaƙa azãbar gare su, kuma ba su zama ana yi musu jinkiri ba. [3.89] Fãce waɗanda suka tũba daga bãyan wannan, kuma suka yi gyãra, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne Mai jin ƙai. [3.90] Lalle ne waɗanda suka kãfirta a bãyan ĩmãninsu, sa´an nan kuma suka ƙãra kãfirci bã zã a karɓi tũbarsu ba. Kuma waɗannan sũ ne ɓatattu. [3.91] Lalle ne wanɗanda suka kãfirta, kuma suka mutu alhãli kuwa suna kãfirai to bã zã a karɓi cike da ƙasa na zinãri daga ɗayansu ba, kõ dã ya yi fansa da shi, waɗannan sunã da azãba mai raɗaɗi, kuma bã su da wasu mataimaka. [3.92] Bã zã ku sãmi kyautatãwa ba, sai kun ciyar daga abin da kuke so. Kuma abin da kuka ciyar, kõ mħne ne, to, lalle ne Allah, gare shi, Masani ne. [3.93] Dukan abinci yã kasance halal ne ga Bani lsrã´ĩla, fãce abinda Isrã´ĩla ya haramta wa kansa daga gabãnin saukar da Attaura. Ka ce: "To, ku zo da Attaura sa´an nan ku karantã ta, idan kun kasance mãsu gaskiya ne. [3.94] "To, wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah daga bãyan wannan, to, waɗannan sũ ne azzãlumai." [3.95] Ka ce: "Allah Ya yi gaskiya, sabõda haka ku bi aƙĩdar Ibrãhĩma mai karkata zuwa ga gaskiya; kuma bai kasance daga mãsu shirki ba." [3.96] Kuma lalle ne, Ɗaki na farko(1) da aka aza dõmin mutãne, haƙĩƙa, shi ne wanda ke Bakka(2) mai albarka kuma shiriya ga tãlikai. [3.97] A cikinsa akwai ãyõyi bayyanannu; (ga misãli) matsayin Ibrãhĩma. Kuma wanda ya shige shi yã kasance amintacce. Kuma akwai hajjin Ɗãkin dõmin Allah a kan mutãne, ga wanda ya sãmi ĩkon zuwa gare shi, kuma wanda ya kafirta to lalle Allah Mawadãci ne daga barin tãlikai. [3.98] Ka ce: "Ya kũ Mutãnen Littãfi! Don me kuke kãfirta da ãyõyin Allah, alhãli kuwa Allah Mai shaida ne a kan abin da kuke aikatãwa?" [3.99] Ka ce: "Ya ku Mutãnen Littãfi! Don me kuke taushe wanda ya yi ĩmani, daga hanyar Allah, kuma kunã nħman ta zama karkatacciya, alhãli kuwa kunã mãsu shaida? Kuma Allah bai gushe daga abin da kuke aikatãwa ba yana Masani." [3.100] Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi ɗã´aga wani ɓangare daga waɗanda aka bai wa Littãfi, zã su mayar da ku kãfirai a bãyan ĩmãninku! [3.101] Kuma yãyã kuke kãfircħwa alhãli kuwa anã karanta ãyõyin Allah a gare ku, kuma a cikinku akwai manzonSa? Kuma wanda ya nħmi tsari da Allah, to, an shiryar da shi zuwa ga hanya miƙaƙƙiya. [3.102] Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, a kan hakkin binsa da taƙawa, kuma kada ku mutu fãce kuna mãsu sallamawa (Musulmi). [3.103] Kuma ku yi daidami da igiyar Allah gabã ɗaya, kuma kada ku rarraba. Kuma ku tuna ni´imar Allah a kanku a lõkacin da kuka kasance maƙiya sai Ya sanya sõyayya a tsakãnin zukãtanku sabõda haka kuka wãyi gari, da ni´imarSa, ´yan´uwa. Kuma kun kasance a kan gãɓar rãmi na wutã sai Ya tsãmar da ku daga gare ta. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ayõyinSa, tsammãninku, zã ku shiryu. [3.104] Kuma wata jama´a daga cikinku, su kasance suna kira zuwa ga alhħri, kuma suna umurni da alhħri, kuma suna hani daga abin da ake ƙi. Kuma waɗannan, sũ ne mãsu cin nasara. [3.105] Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka rarrabu kuma suka sãɓã wa jũna, bãyan hujjõji bayyanannu sun je musu kuma waɗannan sunã da azãba mai girma. [3.106] A rãnar da wasu fuskõki suke yin fari kuma wasu fuskõki suke yin baƙi (zã a ce wa waɗanda fuskokinsu suke yin baƙin): "Shin kun kãfirta a bayan ĩmãninku? Don haka sai ku ɗanɗani azãba sabõda abin da kuka kasance kuna yi na kãfirci." [3.107] Kuma amma waɗanda fuskõkinsu suka yi fari, to sũ suna cikin rahamar Allah kuma, su a cikinta, madawwama, ne. [3.108] Waɗannan ãyõyin Allah ne, muna karanta su a gare ka da gaskiya, kuma Allah bã Ya nufin wani zãlunci ga tãlikai. [3.109] Kuma abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa na Allah ne, kuma zuwa gare Shi ake mayar da al´amurra. [3.110] Kun kasance mafi alhħrin al´umma wadda aka fitar ga mutãne kuna umurni da alhħri kuma kunã hani daga abin da ake ƙi, kuma kunã ĩmãni da Allah. Kuma dã Mutãnen Littãfi sun yi ĩmãni, lalle ne, dã (haka) yã kasance mafi alhħri a gare su. Daga cikinsu akwai mũminai, kuma mafi yawan su fãsiƙai ne. [3.111] Bã zã su cũce ku ba, fãce dai tsangwama. Kuma idan sun yãƙe ku zã su jũya muku bãya, sa´an nan kuma bã zã a taimake su ba. [3.112] An dõka ƙasƙanci a kansu a inda duk aka sãme su fãce da wani alkawari daga Allah, da alkawari daga mutãne. Kuma sun kõma da fushi daga Allah, kuma aka dõka talauci a kansu. Wannan kuwa dõmin sũ, lalle sun kasance suna kãfirta da ãyõyin Allah, kuma suna kashe annabãwa, bã da wani haƙƙi ba. Wannan kuwa dõmin sãɓãwar da suka yi ne, kuma sun kasance suna yin ta´adi. [3.113] Ba su zama daidai ba; daga Mutãnen Littafi akwai wata al´umma wadda take tsaye, suna karãtun ayõyin Allah a cikin sã´õ´in dare, alhãli kuwa sunã yin sujada. [3.114] Suna ĩmãni da Allah da Yinin Lãhira, kuma suna umurni da abin da aka sani kuma suna hani daga abin da ba a sani ba, kuma sunã gaugãwa a cikin alhħrai. Kuma waɗannan suna cikin sãlihai. [3.115] Kuma abin da suka aikata daga alhħri, to, bã zã a yi musu musunsa ba. Kuma Allah Masani ne ga mãsu taƙawa. [3.116] Lalle ne waɗanda suka kãfirta, dũkiyõyinsu kõ ɗiyansu bã zã su wadatar musu da kõme ba daga Allah kuma waɗannan abõkan wuta ne, sũ, a cikinta, madawwama ne. [3.117] Misãlin abin da suke ciyarwa, a cikin wannan rãyuwar dũniya, kamar misãlin iska ce (wadda) a cikinta akwai tsananin sanyi, ta sãmi shukar wasu mutãne waɗanda suka zãlunci kansu, sai ta halakar da ita. Allah bai zãlunce su ba, amma kansu suka kasance sunã zãlunta. [3.118] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi abõkan asĩri daga waninku, ba su taƙaita muku ɓarna. Kuma sun yi gũrin abin da zã ku cũtu da shi. Haƙĩka, ƙiyayya tã bayyana daga bãkunansu, kuma abin da zukãtansu ke ɓõyħwa ne mafi girma. Kuma lalle ne, Mun bayyana muku ãyõyi, idan kun kasance kunã hankalta. [3.119] Gã ku yã waɗannan! Kunã son su bã su son ku, kuma kuna ĩmãni da Littãfi dukansa. Kuma idan sun haɗu da ku sukan ce "Mun yi ĩmani". Kuma idan sun kaɗaita sai su ciji yãtsu a kanku don takaici. Ka ce "Ku mutu da takaicinku. Lalle ne, Allah Masani ne ga abin da ke cikin ƙirãza." [3.120] Idan wani alhħri ya shãfe ku sai ya baƙanta musu rai, kuma idan wata cũtar ta shãfe ku sai su yi farin ciki da ita. Kuma idan kun yi haƙuri kuma kuka yi taƙawa, ƙullinsu bã ya cũtar ku da kõme. Lalle ne, Allah ga abin da suke aikatãwa Mai kħwayħwa ne. [3.121] Kuma a lõkacin(1) da ka yi sauko daga iyãlanka kana zaunar da mũminai a wurãren zama dõmin yãƙi, kuma Allah Mai ji ne, Masani. [3.122] A lõkacin da ƙungiyõyi(1) biyu daga gare ku suka yi niyyar su karye, kuma Allah ne Majiɓincinsu, don haka, ga Allah mũminai sai su dogara. [3.123] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Allah Yã taimake ku a Badar, alhãli kuwa kunã mafiya rauni, sabõda haka ku bi Allah da taƙawa tsammãninku, kuna gõdħwa. [3.124] A lõkacin da kake cħwa ga mũminai, "Shin bai ishe ku ba, Ubangijinku Ya taimake ku da dubu uku daga malã´iku saukakku?" [3.125] "Na´am! Idan kuka yi haƙuri, kuma kuka yi taƙawa, kuma suka zo muku da gaugawarsu, irin wannan, Ubangijinku zai ƙãre ku da dubu biyar daga malãiku mãsu alãma." [3.126] Kuma Allah bai sanya shi(2) ba, fãce dõmin bushãra a gare ku, kuma dõmin zukãtanku su natsu da shi. Taimako bai kasance ba fãce daga wurin Allah, Mabuwãyi, Mai hikima. [3.127] Dõmin Ya katse wani għfe daga waɗanda suka kãfirta ko kuma Ya ƙasƙantã su, har su jũya, suna mãsu ruɓushi. [3.128] Bãbu kõme a gare ka game da al´amarin (shiryar da su banda iyar da manzanci). Ko Allah Ya karɓi tũbarsu, kõ kuwa Ya yi musu azãba, to lalle ne sũ, mãsu zãlunci ne. [3.129] Allah ne da mulkin abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, yana gãfarta wa wanda Yake so, kuma yana azabta wanda Yake so, kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [3.130] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku ci riba ninkininki, riɓanye, kuma ku bi Allah da taƙawa, tsammãninku zã ku ci nasara. [3.131] Kuma ku ji tsõron wutã wadda aka yi tattali dõmin kãfirai. [3.132] Kuma ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, tsammaninku a yi muku rahama. [3.133] Kuma ku yi gaugawa zuwa ga nħman gãfara daga Ubangijinku da wata Aljanna wadda fãɗinta (dai dai da) sammai da ƙasa ne, an yi tattalinta dõmin mãsu taƙawa. [3.134] Waɗanda suke ciyarwa a cikin sauƙi da tsanani kuma suke mãsu haɗiyħwar fushi, kuma mãsu yãfe wa mutãne laifi. Kuma Allah Yana son mãsu kyautatãwa. [3.135] Kuma waɗanda suke idan suka aikata wata alfãsha ko suka zãlunci kansu sai su tunã da Allah, sabõda su nħmi gãfarar zunubansu ga Allah. Kuma wãne ne ke gãfara ga zunubai, fãce Allah? Kuma ba su dõge a kan abin da suka aikata ba, alhãli kuwa suna sane. [3.136] Waɗannan sakamakonsu gãfara ce daga Ubangijinsu, da Gidajen Aljanna (waɗanda) ƙõramu na gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu. Kuma mãdalla da ijãrar mãsu aiki. [3.137] Lalle ne misãlai sun shũɗe a gabãninku, sai ku yi tafiya a cikin ƙasa sa´an nan ku dũba, yãyã ãƙibar mãsu ƙaryatãwa ta kasance. [3.138] Wannan bayãni ne ga mutãne, kuma shiryuwa ce da wa´azi ga mãsu taƙawa. [3.139] Kuma kada ku yi rauni, kuma kada ku yi baƙin ciki, alhãli kuwa kũ ne mafiya ɗaukaka, idan kun kasance mãsu ĩmãni. [3.140] Idan wani mĩki ya shãfe ku, to, lalle ne, wani mĩki kamarsa ya shãfi mutãnen, kuma waɗancan kwãnaki Muna sarrafa su a tsakãnin mutãne dõmin Allah Ya san waɗanda suka yi ĩmãni kuma Ya sãmi mãsu shahãda daga gare ku. Kuma Allah ba Ya son azzãlumai. [3.141] Kuma dõmin Allah Ya ɗauraye waɗanda suka yi ĩmãni,kuma Ya ƙõƙe kãfirai. [3.142] Ko kun yi zaton ku shiga Aljanna alhãli kuwa Allah bai wãda sanin waɗanda suka yĩ jihãdi daga gare ku ba, kuma Ya san mãsu haƙuri? [3.143] Kuma lalle ne, haƙĩƙa kun kasance kuna gũrin mutuwa tun a gabãnin ku haɗu da ita, to lalle ne kun gan ta,(1) alhãli kuwa kuna kallo. [3.144] Kuma Muhammadu bai zama ba face manzo lalle ne manzanni sun shũɗe a gabãninsa. Ashe idan ya mutu ko kuwa aka kashe shi, zã ku jũya a kan dugaduganku? To, wanda ya jũya a kan dugadugansa, bã zai cũci Allah da kõme ba. Kuma Allah zai sãka wa mãsu gõdiya. [3.145] Kuma bã ya yiwuwa ga wani rai ya mutu fãce da iznin Allah, wa´adi ne mai ƙayyadadden ajali. Kuma wanda yake nufin sakamakon dũniya Muna bã shi daga gare ta. Kuma wanda ke nufin samakon Lãhira Muna bã shi daga gare ta. Kuma zã Mu sãka wa mãsu godiya. [3.146] Kuma da yawa wani Annabi wanda ya yi yãƙi, akwai jama´a mãsu yawa tãre da shi, sa´an nan ba su yi laushi ba ga abin da ya same su a cikin hanyar Allah, kuma ba su yi rauni ba kuma ba su sad da kai ba. Kuma Allah yana son mãsu haƙuri. [3.147] Kuma bãbu abin da ya kasance maganarsu fãce faɗarsu cħwa: "Ya Ubangijinmu! Ka gãfarta mana zunubanmu da ɓarnarmu a cikin al´amarinmu, kuma Ka tabbatar da dugaduganmu, kuma Ka taimake mu a kan mutãnen nan kãfirai." [3.148] Allah Yã sãka musu da sakamakon dũniya da kuma kyakkyawan sakamakon Lãhira. Kuma Allah yana son mãsu kyautatãwa. [3.149] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi ɗa´aga waɗanda suka kãfirta zã su mayar da ku a kan dugãduganku, har ku jũya kunã mãsu hasãra. [3.150] ôa, Allah ne Majiɓincinku kuma ShĨ ne Mafi alhħrin mataimaka. [3.151] Zã Mu jħfa tsõro a cikin zukãtan waɗanda suka kãfirta sabõda shirkin da suka yi da Allah gãme da abin da bai saukar da wani dalili ba game da shi. Kuma makõmarsu wuta ce, kuma tir da mazaunin azzãlumai! [3.152] Kuma lalle ne haƙĩƙa Allah Yã yi muku gaskiya ga wa´adinSa, a lokacin da kuke kashe su da izninSa har zuwa lõkacin da kuka kãsa(1) , kuma kuka yi jãyayya a cikin al´amarin, kuma kuka sãɓã a bãyan (Allah) Ya nũna muku abin da kuke so. Daga cikinku akwai wanda yake nufin duniya kuma daga cikinku akwai wanda ke nufin Lãhĩra. Sa´an nan kuma Ya jũyar da ku daga gare su, dõmin Ya jarrabe ku. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Ya yãfe muku laifinku. Kuma Allah Ma´abucin falala ne ga mũminai. [3.153] A lõkacin da kuke hawan dũtse, gudãne. Kuma ba ku karkata a kan kõwa ba, alhãli kuwa Manzon Allah nã kiran ku a cikin na ƙarshenku.(2) Sa´an nan (Allah) Ya sãkã muku da baƙin ciki a tãre da wani baƙin ciki. Domin kada ku yi baƙin ciki a kan abin da ya kuɓuce muku, kuma kada ku yi baƙin cikin a kan abin da ya sãme ku. Kuma Allah Masani ne ga abin da kuke aikatãwa. [3.154] Sa´an nan kuma (Allah) Ya saukar da wani aminci a gare ku daga bãyan baƙin cikin; gyangyaɗi yanã rufe wata ƙungiya daga gare ku, kuma wata ƙungiya, lalle ne, rãyukansu sun shagaltar da su, suna zaton abin da bã shi ne gaskiya ba, a game da Allah, irin zaton jahiliyya, suna cħwa: "Ko akwai wani abu a gare mu dai daga al´amarin?" Ka ce, "Lalle ne al´amari dukansa na Allah ne." Suna ɓõyħwa a cikin zukatansu, abin da bã su bayyana shi a gare ka. Suna cħwa: "Da munã da wani abu daga al´amarin dã ba a kashe mu ba a nan."Ka ce: "Kõ dã kun kasance a cikin gidãjenku, dã waɗanda aka rubũta musu kisa sun fita zuwa ga wurãren kwanciyarsu;" kuma (wannan abu yã auku ne) dõmin Allah Ya jarrabi abin da ke cikin ƙirãzanku. Kuma dõmin Ya tsarkake abin da ke cikin zukãtanku. Allah Masani ne ga abin da ke cikin ƙirãza. [3.155] Lalle ne waɗanda suka jũya daga gare ku a ranar haɗuwar jama´a biyu, shaiɗan kawai ne ya talãlãɓantar da su, sabõda sãshen abin da suka tsirfanta. Kuma lalle ne haƙĩƙa, Allah Ya yãfe laifi daga gare su. Lalle Allah ne Mai gãfara Mai haƙuri. [3.156] Yã ku waɗanda suka yi ĩmani! Kada ku kasance kamar waɗanda suka kãfirta kuma suka ce wa ´yan´uwansu idan sun yi tafiya a cikin ƙasa kõ kuwa suka kasance a wurin yãƙi: "Dã sun kasance a wurinmu dã ba su Mutu ba, kuma dã ba a kashe su ba." (Wannan kuwa) Dõmin Allah Ya sanya waccan magana ta zama nadãma a cikin zukãtansu. Kuma Allah ne Yake rãyarwa kuma Yake matarwa. Kuma Allah, ga abin da kuke aikatãwa, Mai gani ne. [3.157] Kuma lalle ne idan aka kashe ku a cikin hanyar Allah, ko kuwa kuka mutu, haƙĩƙa, gãfara daga Allah da rahama ne mafi alhħri daga abin da suke tãrãwa. [3.158] Kuma lalle ne idan kun mutu ko kuwa aka kashe ku, haƙĩƙa, zuwa ga Allah ake tãra ku. [3.159] Sabõda wata rahama ce daga Allah ka yi sanyin hali a gare su. Kuma dã kã kasance mai hushi mai kaurin zuciya, dã sun wãtse daga għfenka. Sai ka yãfe musu laifinsu, kuma ka nħma musu gãfara, kuma ka yi shãwara(1) da su a cikin al´amarin. Sa´an nan kuma idan ka yi niyyar zartarwa, to, ka dõgara ga Allah, lalle ne, Allah Yana son mãsu tawakkali. [3.160] Idan Allah Ya taimake ku, to, bãbu marinjayi a gare ku. Kuma idan Ya yarɓe ku, to, wãnħ ne wanda yake taimakon ku bãyanSa? Kuma ga Allah sai mũminai su dõgara. [3.161] Kuma bã ya yiwuwa ga wani annabi ya ci gulũlu.(2) Wanda ya ci gulũlu zai je da abin da ya ci na gulũlun, a Rãnar Ƙiyama. Sa´an nan a cika wa kõwane rai sakamakon abin da ya tsirfanta. Kuma sũ, bã zã a zãlunce su ba. [3.162] Shin fa, wanda ya bĩbiyi yardar Allah, yana zama kamar wanda ya kõma da fushi daga Allah kuma makomarsa Jahannama ce? Kuma tir da makõma ita! [3.163] Sũ, darajõji(3) ne a wurin Allah, kuma Allah Mai gani ne ga abin da suke aikatawa. [3.164] Lalle ne haƙĩƙa Allah Yã yi babbar falala(4) a kan mũminai, dõmin Yã aika a cikinsu, Manzo daga ainihinsu yana karanta ãyõyinSa a gare su, kuma yana tsarkake su, kuma yana karantar da su Littãfi da hikima, kuma lalle, sun kasance daga gabãni, haƙĩƙa suna cikin ɓata bayyananniya. [3.165] Shin kuma a lõkacin(5) da wata masĩfa, haƙĩƙa, ta sãme ku alhãli kuwa kun sãmar da biyunta, kun ce: "Daga ina wannan yake?" Ka ce: "Daga wurin rãyukanku(6) yake." Lalle ne, Allah, a kan dukan kõme, Mai ĩkon yi ne. [3.166] Kuma abin da ya sãme ku a rãnar haɗuwar jama´a biyu, to, da izinin Allah ne, kuma dõmin (Allah) Ya san mũminai (na gaskiya). [3.167] Kuma dõmin Ya san waɗanda suka yi munãfunci, kuma an ce musu: "Ku zo ku yi yãƙi a cikin hanyar Allah, kõ kuwa ku tunkuɗe."(1) Suka ce: "Dã mun san (yadda ake) yãƙi dã mun bĩ ku." Sũ zuwa ga kãfirci a rãnar nan, sun fi kusa daga gare su zuwa ga ĩmãni. Sunã cħwa da bãkunansu abin da bã shi ne a cikin zukãtansu ba. Allah ne Mafi sani ga abin da suke ɓõyewa. [3.168] Waɗanda suka ce wa ´yan´uwansu kuma suka zauna abinsu: "Dã sun yi mana ɗã´a, dã ba a kashe su ba." Ka ce: "To, ku tunkuɗe mutuwa daga rãyukanku, idan kun kasance mãsu gaskiya." [3.169] Kada ka yi zaton waɗanda aka kashe a cikin hanyar Allah matattu ne. A´a, rãyayyu ne su, a wurin bangijinsu.(2) Ana ciyar da su. [3.170] Suna mãsu farin ciki sabõda abin da Allah Ya bã su daga falalarSa, kuma suna yin bushãra ga waɗanda ba su risku da su ba, daga bayansu; "Bãbu tsõro a kansu kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba." [3.171] Suna yin bushãra sabõda wata ni´ima daga Allah da wata falala. Kuma lalle ne, Allah bã Ya tozartar da ijãrar mũminai. [3.172] Waɗanda suka karɓa(3) kira zuwa ga Allah da ManzonSa, daga bãyan mĩki ya sãme su. Akwai wata lãda mai girma ga waɗanda suka kyautata(4) yi daga gare su, kuma suka yi taƙawa. [3.173] Waɗanda mutãne(5) suka ce musu: "Lalle ne, mutãne sun tãra (rundunõni) sabõda ku, don haka ku ji tsõrnsu. Sai (wannan magana) ta ƙara musu ĩmãni, kuma suka ce: "Mai isarmu Allah ne kuma mãdalla da wakili Shĩ." [3.174] Sa´an nan suka jũya da wata ni´ima daga Allah da wata falala, wata cũta ba ta shãfe su ba, kuma suka bi yardar Allah. Kuma Allah ne Ma´abucin falala Mai girma. [3.175] Wancan, Shaiɗan ne kawai yake tsõratar da, ku masõyansa. To, kada ku ji tsõronsu, ku ji tsõro Na idãn kun kasance mãsu ĩmãni. [3.176] Kuma waɗannan da suke gaugãwa a cikin kãfirci kada su ɓãta maka rai. Lalle ne su, bã zã su cũci Allah da kõme ba. Allah yanã nufin cħwa, bã zai sanya musu wani rabo ba a cikin Lãhira kuma suna da wata azãba mai girma. [3.177] Lalle ne, waɗanda suka sayi kãfirci da ĩmani, ba zã su cũci Allah da kõme ba. Kuma sunã da azãba mai raɗaɗi. [3.178] Kuma kada waɗanda suka kãfirta su yi zaton cħwa, lalle ne jinkirin da Muke yi musu alhħri ne ga rãyukansu. Munã yi musu jinkirin ne dõmin su ƙãra laifi kawai kuma suna da azãba mai wulãƙantarwa. [3.179] Allah bai kasance yana barin mũminai a kan abin da kuke kansa ba, sai(1) Ya rarrabe mummũna daga mai kyau. Kuma Allah bai kasance Yanã sanar da ku gaibi ba.(2) Kuma amma Allah Yana zãɓen wanda Ya so daga manzanninSa.(3) Sabõda haka ku yi ĩmãni da Allah da manzanninSa Kuma idan kun yi ĩmãni kuma kuka yi taƙawa, to, kunã da lãdã mai girma. [3.180] Kuma kada waɗannan da suke yin rõwa da abin da Allah Ya bã su daga falalarSa su yi zaton shĩ ne mafi alhħri a gare su. A´a, shĩ mafi sharri ne a gare su. Zã a yi musu saƙandami da abin da suka yi rõwa da Shi a Rãnar Ƙiyãma. Kuma ga Allah gãdon sammai da ƙasa yake, kuma Allah, ga abin da kuke aikatãwa, Masani ne. [3.181] Lalle ne, haƙĩƙa Allah Yã ji maganar waɗanda suka ce: "Lalle ne, Allah faƙĩri ne, mũ ne wadãtattu." za mu rubũta abin da suka faɗa, da kisan da suka yi wa Annabãwa bã da wani haƙƙi ba kuma Mu ce: "Ku ɗanɗani azãbar gõbara! [3.182] "Wannan (azãbar) kuwa sabõda abin da hannuwanku suka gabãtar ne. Kuma lalle ne Allah bai zama mai zãlunci ga bãyinsa ba." [3.183] Waɗanda suka ce: "Lalle ne Allah Yã yi alkawari zuwa gare mu, kada mu yi ĩmãni sabõda wani Manzo sai yã zo mana da Baiko wadda wuta za ta ci." Ka ce: "Lalle ne wasu manzanni sun je muku, a gabãnĩna, da hujjõji bayyanannu, kuma da abin da kuka faɗa, to, don me kuka kashe su, idan kun kasance mãsu gaskiya?" [3.184] To, idan sun ƙaryata ka, to lalle ne, an ƙaryata wasu manzanni a gabãninka, sun je musu da hujjõji bayyanannu da littattafai, da kuma Littafi mai haske. [3.185] Kõwane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne. Kuma ana cika muku ijãrõrinku kawai ne a Rãnar Ƙiyãma. To, wanda aka nĩsantar daga barin wuta, kuma aka shigar da shi Aljanna, to, lalle ne yã tsĩra. Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba fãce jin dãɗin rũɗi. [3.186] Lalle ne zã a jarraba(1) ku a cikin dũkiyarku da rãyukanku, kuma lalle ne kuna jin cũtarwa mai yawa daga waɗanda aka bai wa Littãfi a gabãninku da kuma waɗanda suka yi shirki. Kuma idan kun yi haƙuri, kuma kuka yi taƙawa, to lalle ne, wannan yana daga manyan al´amurra. [3.187] Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin waɗanda aka bai wa(1) Littãfi, "Lalle ne kuna bayyana shi ga mutãne, kuma bã zã ku ɓõye shi ba." Sai suka jħfar da shi a bãyan bãyansu, kuma suka sayi ´yan kuɗi kaɗan da shi. To, tir da abin da suke saye! [3.188] Kada lalle ka yi zaton waɗanda suke yin farin ciki da abin da suka bãyar, kuma suna son a yabe su da abin da ba su aikatã ba. To, kada lalle ka yi zaton su da tsĩra daga azãba. Kuma suna da azãba mai raɗadi. [3.189] Kuma ga Allah mulkin sammai da ƙasa yake. Kuma Allah, a kan kõme, Mai ĩkon yi ne. [3.190] Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa da sãɓãwar dare da yini akwai ãyõyi ga ma´abũta hankali. [3.191] Waɗanda suke ambatar Allah a tsaye da zaune da a kan sãsanninsu, kuma suna tunãni a kan halittar sammai da ƙasa: "Yã Ubangijinmu! Ba Ka halitta wannan a kan banza ba. TsarkinKa! Sabõda haka Ka tsare mu daga azãbar wuta. [3.192] "Ya Ubangijinmu! Lalle ne Kai, wanda Ka shigar a cikin wuta to, haƙĩƙa, Ka tozarta shi kuma bãbu wasu mataimaka ga azzãlumai. [3.193] "Yã Ubangijinmu! Lalle ne mũ mun ji Mai kira yanã kira zuwa ga ĩmãni cħwa, ´Ku yi ĩmãni da Ubangijinku.´ Sai muka yi ĩmãni. Yã Ubangijinmu! Sabõda haka Ka gãfarta mana zunubanmu, kuma Ka kankare miyãgun ayyukanmu daga gare mu. Kuma Ka karɓi rãyukanmu tãre da mutãnen kirki. [3.194] "Yã Ubangijinmu! Ka bã mu abin da Ka yi mana wa´adi (alkawari) a kan manzanninKa, kuma kada Ka tozarta mu a Rãnar Ƙiyãma. Lalle ne Kai, bã Ka sãɓãwar alkawari." [3.195] Sabõda haka Ubangijinsu Ya karɓa musu cħwa, "Lalle ne Nĩ bã zan tozartar da aikin wani mai aiki ba daga gare ku, namiji ne ko kuwa mace, sãshenku daga sãshe. To, waɗanda suka yi hijira kuma aka fitar da su daga gidãjensu, kuma aka cũtar da su a cikin hanyaTa, kuma suka yi yãƙi, kuma aka kashe su, lalle ne zan kankare musu miyagun ayyukansu, kuma lalle ne zan shigar da su gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙoramu ke gudãna daga ƙarƙashinsu, a kan sakamako daga wurin Allah. Kuma a wurinSa akwai kyakkyawan sakamako. [3.196] Kada jujjuyawar waɗanda suka kãfirta a cikin garũruwa ta rũɗe ka. [3.197] Jin dãɗi ne kaɗan sa´an nan makõmarsu Jahannama ce, kuma tir da shimfiɗa ita! [3.198] Amma waɗanda suka bi Ubangijinsu da taƙawa sunã da Gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙoramu ke gudãna a ƙarƙashinsu suna madawwama a cikinsu, a kan liyãfa daga wurin Allah, kuma abin da ke wurin Allah ne mafi alhħri ga barrantattu. [3.199] Kuma lalle ne daga Mutãnen Littãfi(1) haƙĩƙa akwai wanda yake yin ĩmãnĩ da Allah da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar zuwa gare su, sunã mãsu tawãlu´i ga Allah, bã su sayen tamani kaɗan da ãyõyin Allah. Waɗannan suna da ijãrarsu a wurin Ubangijinsu. Lalle ne Allah Mai gaugãwar sakamako da yawa ne. [3.200] Yã ku waɗanda suka yi ĩmani! Ku yi haƙuri kuma ku yi dauriya, kuma ku yi zaman dãko, kuma ku yi taƙawa, tsammãninku zã ku ci nasara.(2) @AN NISAA' Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [4.1] Ya ku mutãne! Ku bi Ubangijinku da taƙawa Wanda Ya halitta ku daga rai guda, kuma Ya halitta, daga gare shi, ma´auransa, kuma Ya watsa daga gare su maza mãsu yawa da mãtã. Kuma ku bi Allah da taƙawa Wanda kuke rõƙon jũna da (sũnan), shi, da kuma zumunta(1) . Lalle ne Allah Ya kasance, a kanku, Mai tsaro ne. [4.2] Kuma ku bai wa marãyu dũkiyõyinsu, kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau. Kuma kada ku ci dũkiyõyinsu zuwa ga dũkiyõyinku. Lalle shi, yã kasance zunubi ne mai girma. [4.3] Kuma idan kun ji tsõron bã zã ku yi ãdalci ba a cikin marãyu,(2) to, (akwai yadda zã a yi) ku auri abin da ya yi muku dãɗi daga mãtã; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu. Sa´an nan idan kun ji tsõron bã zã ku yi ãdalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa abin da hannayenku na dama suka mallaka. Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku wuce haddi ba. [4.4] Kuma ku bai wa mãtã sadãkõkĩnsu da sauƙin bãyarwa. Sa´an nan idan suka yãfe muku wani abu daga gare shi, da dãɗin rai, to, ku ci shi da jin dãɗi da sauƙin haɗiya. [4.5] Kada ku bai wa wãwãye(3) dũkiyarku, wadda Allah Ya sanya ta a gare ku, kunã mãsu tsayuwa (ga gyãranta). Kuma ku ciyar da su a cikinta, kuma ku tufãtar da su, kuma ku gaya musu magana sananniya ta alhħri. [4.6] Kuma ku jarraba marãyu, har a lõkacin da suka isa aure. To, idan kun lura da shiriya daga gare su, to, ku mĩƙa musu dũkiyõyinsu. Kada ku cĩ ta da ɓarna, kuma da gaggawa kãfin su girma. Kuma wanda yake wadãtacce, to, ya kãma kãnsa, kuma wanda yake faƙĩri, to, ya ci, gwargwadon yadda ya kamata. To, idan kun mĩƙa musu dũkiyõyinsu, sai ku shaidar a kansu. Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai bincike. [4.7] Maza suna da rabo(1) daga abin da iyãye biyu da mafi kusantar dangi suka bari, kuma mãtã suna da rabo daga abin da iyãye biyu da mafi kusantar dangi suka bari, daga abin da ya ƙaranta daga gare shi kõ kuwa ya yi yawa, rabo yankakke. [4.8] Kuma idan ma´abũta zumunta da marãyu da matalauta suka halarci rabon, to, ku azurta su daga gare shi, kuma ku faɗa musu magana sananniya ta alhħri. [4.9] Kuma waɗanda suke dã sun bar(2) zuriyya mãsu rauni a bãyansu, zã su ji tsõro a kansu, su yi sauna, sa´an nan su bi Allah da taƙawa, kuma su faɗi magana madaidaiciya. [4.10] Lalle ne, waɗanda suke cĩn dũkiyar marãyu da zãlunci, to, wuta kawai suke ci a cikin cikkunansu, kuma za su shiga cikin wata wuta mai tsanani. [4.11] Allah Yanã yi muku wasiyya a cikin ´ya´yanku; namiji yanã da rabon mãtã biyu. Idan sun kasance mãtã ne fiye da biyu kuwa, to, suna da biyu daga kashi uku ɗin abin da ya bari, kuma idan ta zama guda ce (kawai) to, tana da rabi. Kuma iyãyensa biyu kõwane ɗaya daga cikinsu yanã da ɗaya daga kashi shida ɗin abin da ya bari idan wani rħshe ya kasance gare shi, to, idan rħshe bai kasance gare shi ba, kuma iyãyensa ne (kawai) suka gãje shi, to, uwa tanã da sulusi (ɗaya daga cikin kashi uku). Sa´an nan idan ´yan´uwa sun kasance gare shi, to, uwarsa tana da sudusi (ɗaya daga cikin kashi shida) daga bayan wasiyya wadda ya yi kõ kuwa bãshi. Ubanninku da ´yã´yan ku, ba ku sani ba, wannensu ne mafi kusantar amfani, a gare ku. Yankawa daga Allah. Lalle ne, Allah Yã kasance Masani Mai hikima. [4.12] Kuma kunã da rabin abin da mãtanku na aure suka bari idan rħshe bai kasance gare su ba. Sa´an nan idan rħshe ya kasance gare su, to, kunã da rubu´i (ɗaya daga cikin kashi huɗu) daga abin da suka barin, daga bãyan wasiyya wadda suka yi kõ kuma bãshi. (Sũ) kuma suna da rubu´i daga abin da kuka bari idan rħshe bai kasance ba gare ku, idan kuwa rħshe ya kasance gare ku, to, sunã da sumuni (ɗaya daga cikin kashi takwas) daga abin da kuka bari, daga bãyan wasiyya wadda kuka yi kõ kuwa bãshi. Idan wani namiji ya kasance ana gãdon sa bisa kalãla, ko kuwa wata mace alhãli kuwa yana da ɗan´uwa kõ ´yar´uwa(1) to, kõwane ɗaya daga cikinsu yana da sudusi (ɗaya daga cikin kashi shida), sai idan sun kasance mafi yawa daga wannan, to, sũ abõkan tãrayya ne a cikinsulusi (ɗaya bisa uku), daga bãyan wasiyya wadda aka yi kõ kuma bãshi. Bã da yana mai cũtarwa ba, ga wasiyya, daga Allah. Kuma Allah Masani ne Mai haƙuri. [4.13] Waɗancan iyãkõkin Allah ne. Wanda ya yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, (Allah) zai shigar da shi gidãjen Aljanna (waɗanda) ɗõramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu, kuma wannan shi ne rabo babba. [4.14] Kuma wanda ya sãɓã wa Allah da ManzonSa, kuma ya ƙħtare iyãkõkinSa, zai shigarda shi wuta, yana madawwami a cikinta, kuma yana da wata azãba mai walãkantarwa. [4.15] Kuma waɗanda suka je wa alfãsha daga mãtanku, to, ku nħmi Shaidar mutãne huɗu daga gare ku a kansu. To, idan sun yi shaida, sai ku tsare su a cikin gidãje har mutuwa ta karɓi rãyukansu, ko kuwa Allah Ya sanya wata hanya a gare su.(1) [4.16] Kuma waɗanda (mazã biyu) suka je mata(2) daga ku, to, ku cũtar da su, sa´an nan idan sun tũba kuma suka kyautata hãlãyensu, sai ku kau da kai da ga barinsu. Lalle ne Allah Yã kasance Mai kaɓar tũba ne, Mai jin ƙai [4.17] Abar da take tũba kawai ga Allah, ita ce ga waɗanda suke aikatãwar mugun aiki da jãhilci sa´an nan su tũba nan kusa(3) to, waɗannan Allah Yanã karɓar tũ barsu kuma Allah Yã kasance Masani ne, Mai hikima. [4.18] Bã tũba ba ce ga waɗanda suke aikatãwar mũnanan ayyuka har idan mutuwa ta halarci ɗayansu ya ce: "Lalle ne ni, na tũba yanzu," kuma bã tũba ba ce ga waɗanda suke mutuwa alhãli kuwa sunã kãfi rai Waɗannan mun yi musu tattalin wata azãba mai raɗaɗi [4.19] Ku waɗanda suka yi ĩmãni! Bã ya halatta a gare ku, ku gãji mãtã a kan tĩlas kuma kadaku hana su aure dõmin ku tafi da sãshen abin da kuka ba su, fãce idan suka zo da wata alfãsha(4) bayya nanniya kuma ku yi zamantakħwa da su da alhħri sa´an nan idan kun ƙĩ su, to akwai tsammãnin ku ƙi wani abu alhãli kuwa Allah Ya sanya wani alhħri mai yawaa cikinsa. [4.20] Kuma idan kun yi nufin musanya mãta a matsayin wata mãta, alhãli kuwa kun bai wa ɗayarsu ƙinɗari(1) to kada ku karɓi kõme daga gare, shi, shin, zã ku karɓe shi da ƙarya da zunubi bãyyananne? [4.21] Kuma yãyã zã ku karɓe shi alhãli kuwa, haƙĩƙa, sãshenkuyã sãdu zuwa ga sãshe, kuma sun riƙi alkawari(2) mai kauri daga gare ku? [4.22] Kuma kada ku auri abin da ubanninku suka aura daga mãtã, fãce abin da ya shige. Lalle ne shi, ya kasance alfãsha da abin ƙyãma. Kuma ya mũnana ya zama hanya. [4.23] An haramta muku uwãyenku, da ´yã´yanku, da ´yan´uwanku mãtã, da goggonninku, da innoninku, da ´yã´yan ɗan´uwa, da ´ya´yan ´yar´uwa, da uwãyenku waɗanan da suka shãyar da ku mãma, da ´yan´uwanku mãtã na shan mãma, da uwãyen mãtanku, da agõlolinku waɗanda suke cikin ɗãkunanku daga mãtanku, waɗanda kuka yi duhũli da su, kuma idan ba ku yi duhũli da sũ ba, to, bãbu laifi(3) a kanku, da mãtan ´yã´yanku waɗanda, suke daga tsatsonku, kuma kada ku haɗa tsakanin ´yan´uwa biyu mãtã, fãce abin da ya shige. Lalle ne, Allah Yã kasance Mai gãfara ne Mai jin ƙai. [4.24] Da tsararrun auren(1) wasu maza, fãce dai abin da hannuwanku suka mallaka. (Ku tsare) Littãfin Allah a kanku. Kuma an halatta muku abin da yake bayan wancan. Ku nħma da dukiyõyinku, kunã mãsu yin aure, bã mãsu yin zina ba. sa´an nan abin da kuka ji daɗi da shi daga gare su, to, ku bã su ijãrõrinsu bisa farillar sadãki. Bãbu laifia gare ku ga abin da kuka yi yardatayya(2) da shi a bãyan farillar sadãki. Lalle ne Allah Yã kasance Masani ne, Mai hikima. [4.25] Kuma wanda(3) bai sãmi wadãta ba daga cikinku bisa ga ya auri ´ya´ya mũminai, to, (ya aura)daga abin da hannuwanku na dãma suka mallaka, daga kuyanginku mũminai. Kuma Allah ne Mafi sani ga ĩmãninku, sãshenku daga(4) sãshe. Sai ku aurħ su da izinin mutãnensu. Kuma ku bã su ijãrõrinsu bisa ga abin da aka sani, suna mãsu kamun kai bã mãsu zina ba, kuma bã mãsu riƙon abõkai ba. To, idan aka aure su, sai kuma suka zo da wata alfãsha, to, akwai a kansu rabin abin da ko a kan, ´ya´ya daga azãba. wancan (auren kuyanga) ga wanda ya ji tsõron wahala ne daga gare ku. Kuma ku yi haƙuri shi ne mafi alhħri a gare ku. Kuma Allah Mai gãfara ne Mai jin ƙai. [4.26] Allah Yanã nufin Ya bayyana muku, kuma Ya shiryar da ku hanyõyin waɗanda suke a gabãninku kuma Ya karɓi tũbarku. Kuma Allah Masani ne Mai hikima. [4.27] Kuma Allah Yanã nufin Ya karɓi tũbarku. Kuma waɗanda suke bin sha´awõyi suna nufin ku karkata, karkata mai girma. [4.28] Allah Yana nufin Ya yi muku sauƙi, kuma an halitta mutum yana mai rauni. [4.29] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku ci dũkiyõyinku a tsakãninku da yaudara,(1) fãce idan ya kasance daga fatauci ne, bisa yardatayya daga gare ku. Kuma kada ku kashe kãnku. Lalle ne Allah Yã kasance, game da ku, Mai jin ƙai ne. [4.30] Wanda ya aikata wancan bisa ta´adi da zãlunci, to, zã Mu ƙõne shi da Wuta. Kuma wannan yã kasance ga Allah (abu ne) mai sauƙi. [4.31] Idan kuka nĩsanci manyan abubuwan da ake hana ku aikatãwa, to, zã Mu kankare mũnanan ayyukanku daga gare ku, kuma Mu shigar da ku mashiga ta karimci. [4.32] Kuma kada ku yi gurin abin da Allah Ya fifita sãshenku da shi a kan sãshe; maza suna da rabo daga abin da suka tsirfanta, kuma mãtã suna da rabo daga abin da suka tsirfanta. Ku rõƙi Allah daga falalarSa. Lalle ne Allah Yã kasance ga dukkan kõme, Masani. [4.33] Kuma ga kõwa, Mun sanya magada daga abin da mahaifa da mafiya kusancin zumunta suka bari. Kuma waɗanda rantsuwõyinku suka ƙulla(2) ku bã su rabonsu. Lalle ne, Allah Yã kasance, a kan dukkan kõme, Mahalarci. [4.34] Maza mãsu tsayuwa ne(1) a kan mãtã, sabõda abin da Allah Ya fifita sãshensu da shi a kan sãshe kuma sabõda abin da suka ciyar daga dũkiyõyinsu. To, sãlihan mãtã mãsu ɗã´a ne, mãsu tsarħwa ga gaibi sabõda abin da Allah Ya tsare. Kuma waɗanda kuke tsõron bijirewarsu, to, ku yi musu gargaɗi, kuma ku ƙaurace musu a cikin wurãren kwanciya, kuma ku dõke su. Sa´an nan kuma, idan sun yi muku ɗa´a, to, kada ku nħmi wata hanya a kansu. Lalle ne Allah Yã kasance Maɗaukaki, Mai girma. [4.35] Kuma idan kun ji tsõron sãɓãwar tsakãninsu to ku aika da wani mai sulhu daga mutãnensa da wani mai sulhu daga mutãnenta.(2) Idan sun yi nufin gyãrãwa, Allah zai daidaita tsakãninsu (ma´auran). Lalle ne Allah Yã kasance Masani Mai jarrabãwa. [4.36] Kuma ku bauta wa(3) Allah kuma kada ku haɗa wani da Shi, kuma ga mahaifa ku yi kyautatãwa, kuma ga ma´abũcin zumunta da marãyu da matalauta, da maƙwabci ma´abũcin kusanta, da maƙwabci manĩsanci, da abõki a għfe da ɗan hanya, da abin da hannuwanku na dãma suka mallaka. Lalle ne Allah bã Ya son wanda ya kasance mai tãƙama, mai yawan alfahari. [4.37] Waɗanda suke yin rõwa, kuma sunã umurnin mutãne da yin rõwa, kuma suna ɓõyewar abin da Allah Ya bã su na falalarSa. Kuma Mun yi tattali, sabõda kãfirai, azãba mai walãkantarwa. [4.38] Kuma waɗanda suke ciyar da dũkiyõyinsu dõmin nũna wa mutãne, kuma bã su yin ĩmãni da Allah, kuma bã su yin ĩmãnida Rãnar Lãhira, kuma wanda Shaiɗan ya kasance abõkin haɗi a gare shi, to, yã mũnana ga abõkin haɗi. [4.39] Kuma mħne ne a kansu, idan sun yi ĩmãni da Allah, kuma da Rãnar Lãhira, kuma sun ciyar da abin da Allah Yã azurtã su, kuma Allah Ya kasance, gare su, Masani? [4.40] Lalle ne, Allah bã Ya zãluncin gwargwadon nauyin zarra, idan ta kasance alhħri ce, zai riɓanya ta, kuma Ya kãwo daga gunsa ijãra mai girma. [4.41] To, yãyã, idan Mun zo da shaidu daga dukkan al´umma, kuma Muka zo da kai a kan waɗannan, kana mai shaida! [4.42] A rãnar nan, waɗanda suka kãfirta kuma suka sãɓã wa Manzo, sunã gũrin dã an baje ƙasa dasu, kuma bã su ɓõye wa Allah wani labãri. [4.43] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku kusanci salla alhãli kuwa kuna mãsu mãye,(1) sai kun san abin da kuke faɗa kuma haka idan kuna mãsu janaba, fãce mai ƙħtare hanya, har ku yi wanka. Kuma idan kun kasance majinyata, ko kuwa a kan tafiya ko kuwa wani daga cikinku, idan ya zo daga gayaɗi, kõ kuwa kun shãfi mãtã ba ku sãmi ruwa ba, to ku nufi, fuskar ƙasa mai kyau, ku yi shãfa ga fuskokinku da hannuwanku(2) . Lalle ne Allah Yã kasance Mai yãfħwa Mai gãfara. [4.44] Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda aka bai wa rabo daga Littafi, suna sayen ɓata, kuma suna nħman ku ɓace daga hanya? [4.45] Kuma Allah ne Mafi sani ga maƙiyanku, kuma Allah Yã isa Ya zama Majibinci, kuma Yã isa Ya zama Mataimaki. [4.46] Daga waɗanda suka tũba (Yahũdu), akwai wasu sunã karkatar da magana daga wurãrenta suna cħwa: "Mun jiya(1) kuma mun ƙiya, kuma ka jiya a wani wurin jiyãwa, kuma rã´ina (da ma´anar ´ruɓaɓɓe´), ka tsare mu," dõmin karkatarwa da harsunansu, kuma dõmin sũkã a cikin addini. Kuma dã lalle sũ, sun ce: "Mun jiya kuma mun yi ɗa´a, kuma ka saurãra kuma ka dãkata mana," haƙĩƙa, dã ya kasance mafi alhħri a gare su, kuma mafi daidaita; amma Allah Yã la´anħ su, sabõda kãfircinsu don haka bã zã su yi ĩmãni ba, sai kaɗan. [4.47] Yã kũ waɗanda aka bai wa Littãfi! Ku yi ĩmãni da abinda Muka saukar, yana mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku, tun gabanin Mu shãfe wasu fuskõki, sa´an nan Mu mayar da su a kan bãyayyakinsu, ko Mu la´ane su kamar yadda Muka la´ani masu Asabar. Kuma umurnin Allah ya kasance abin aikatãwa. [4.48] Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki game da Shi, kuma Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan ga wanda Yake so, kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ƙirƙiri zunubi mai girma. [4.49] Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suke tsarkake kansu? ôa, Allah ne Yake tsarkake wanda Yake so. Kuma ba za a zalunce su da zaren gurtsun dabĩno ba. [4.50] Ka dũba yadda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah! Kuma shi ya isa ga zama zunubi bayyananne. [4.51] Shin, ba ka gani ba zuwa ga waɗanda aka bai wa rabõ da ga Littafi suna ĩmãni da gunki da Shaiɗan(2) kuma suna cħwa ga waɗanda suka kãfirta: "Waɗannan ne mafiya shiriya daga waɗanda suka yi ĩmãni ga hanya"? [4.52] Waɗannan ne waɗanda Allah Ya la´ane su, kuma wanda Allah Ya la´ana to bã zã ka sãmi mataimaki a gare shi ba. [4.53] Ko suna da rabõ ne daga mulki? To, a sa´an nan bã zã su iya bai wa mutãne hancin gurtsun dabino ba. [4.54] Ko suna hãsadar mutãne(1) ne a kan abin da Allah Ya bã su daga falalarSa? To, lalle ne, Mun bai wa gidan Ibrãhĩm Littãfi da hikima kuma Mun bã su mulki mai girma. [4.55] To, daga cikinsu akwai wanda ya yi ĩmãni da shi, kuma daga cikinsu akwai wanda ya kange daga gare shi. Kuma yã isa Jahannama ta hũru da shi. [4.56] Lalle ne waɗanda suka kãfirta da ayõyinMu za Mu ƙõne su da wuta, kõ da yaushe fãtunsu suka nuna, sai Mu musanya musu wasu fãtun, dõmin su ɗanɗani azãba. Lalle ne Allah Yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima. [4.57] Kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, zã Mu shigar da su gidãjen Aljanna, (waɗanda) ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã dawwamammu a cikinsu har abada suna da, a cikinsu, mãtan aure mãsu tsarki, Kuma Munã shigar da su a wata inuwa matabbaciyar lumshi. [4.58] Lalle ne Allah Yanã umurnin ku ku bãyar da amãnõni zuwa ga mãsu sũ.(2) Kuma idan kun yi hukunci a tsakãnin mutãne, ku yi hukunci da ãdalci. Lalle ne Allah mãdalla da abin da Yake yi muku wa´azi da shi. Lalle ne Allah Yã kasance Mai ji ne, Mai gani. [4.59] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ɗã´a ga Allah, kuma ku yi ɗã´a ga ManzonSa, da ma´abũta al´amari daga cikinku.(3) Idan kun yi jãyayya a cikin wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da ManzonSa idan kun kasance kunã ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Wannan ne mafi alhħri, kuma mafi kyau ga fassara. [4.60] Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suke riyãwar cħwa sunã ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare ka da abin da aka saukar daga gabãninka, sunã nufin su kai ƙãra zuwa ga Ɗãgũtu(1) alhãli kuwa, lalle ne, an umurce su da su kãfirta da shi, kuma Shaiɗan yanã nħman ya ɓatar da su, ɓatarwa mai nĩsa. [4.61] Kuma idan aka ce musu: "Ku zo zuwa ga abin da Allah Ya saukar, kuma zuwa ga Manzo" zã ka ga munãfukai(2) sunã kange mutãne daga gare ka, kangħwa. [4.62] To, yaya, idan wata masĩfa ta sãme su, sabõda abin da hannuwansu suka gabãtar sa´an nan kuma su je maka sunã rantsuwa da Allah cħwa, "Ba mu yi nufin kõme ba sai kyautatawa da daidaitãwa."? [4.63] Waɗannan ne waɗanda Allah Ya san abin da ke cikin zukãtansu. Sabõda haka ka kau da kai daga gare su, kuma ka yi musu gargaɗi, kuma ka gaya musu, a cikin sha´anin kansu, magana mai nauyi da fasãha. [4.64] Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba fãce dõmin a yi masa ɗã´a da izinin Allah. Kuma dã dai lalle sũ a lõkacin da suka zãlunci kansu,(3) sun zo maka sa´an nan suka nħmi gãfarar Allah kuma Manzo ya nħma musu gãfara, haƙĩƙa, dã sun sãmi Allah Mai karɓar tũba Mai jin ƙai. [4.65] To, a´aha! Ina rantsuwa da Ubangijinka, ba za su yi ĩmãni ba, sai sun yarda da hukuncinka ga abin da ya sãɓa a tsakãninsu, sa´an nan kuma ba su sãmi wani ƙunci a cikin zukãtansu ba, daga abin da ka hukunta, kuma su sallama sallamãwa. [4.66] Kuma dã dai lalle Mũ, Mun wajabta musu cħwa, "Ku kashe kanku, ko kuwa ku fita daga gidãjenku," dã ba su aikata shi ba, fãce kaɗan daga gare su. Kuma dã dai lalle sũ sun aikata abin da ake yi musu gargaɗi da shi, haƙĩƙa, dã yã kasance mafi alhħri daga gare su, kuma mafi tsanani ga tabbatarwa. [4.67] Kuma a sa´an nan, haƙĩƙa, dã Mun bã su, lãda mai girma, daga gunMu. [4.68] Kuma lalle ne, dã Mun shiryar da su hanya madaidaiciya. [4.69] Kuma waɗannan da suka yi ɗã´a ga Allah da Mazonsa, to, waɗannan sunã tãre da waɗanda Allah Ya yi ni´ima a kansu, daga annabãwa da mãsu yawan gaskatãwa, da masu shahãda(1) da sãlihai. Kuma waɗannan sun kyautatu ga zama abõkan tafiya. [4.70] Waccan falalar daga Allah take, kuma Allah Yã isa zama Masani. [4.71] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku riƙi shirinku(2) sa´an nan ku fitar da hari jama´a jama´a ko ku fitar da yaƙi gaba ɗaya. [4.72] Kuma lalle ne daga cikinku akwai mai fãsarwa(3) . To idan wata masĩfa ta sãme ku, sai ya ce: "Lalle ne, Allah Ya yi mini ni´ima dõmin ban kasance mahalarci tãre da su ba." [4.73] Kuma lalle ne idan wata falala daga Allah ta sãme ku haƙĩƙa, tabbas, yanã cħwa, kamar wata sõyayya ba ta kasance a tsakãninku da shi ba: "Yã kaitona! Dã na zama tãre da su dai, dõmin in rabonta da rabõ mai girma!" [4.74] Sai waɗanda suke sayar da rayuwar dũniya su karɓi ta Lãhira su yi yãƙi, a cikin hanyar Allah. Kuma wanda ya yi yãki a cikin hanyar Allah to a kashe shi ko kuwa ya rinjãya, sa´an nan zã Mu ba shi ijãra mai girma. [4.75] Kuma mħne ne ya sãme ku, bã ku yin yãƙi a cikin hanyar Allah, da waɗanda aka raunanar daga maza da mata da yãra sunã cewa: "Yã Ubangijinmu! Ka fitar da mu daga wannan alƙarya wadda mutãnenta suke da zãlunci, kuma Ka sanya mana majiɓinci daga gunKa, kuma Ka sanya mana mataimaki daga gunKa."? [4.76] Waɗanda suka yi ĩmãni, sunã yãki a cikin hanyar Allah, kuma waɗanda suka kãfirta sunã yãƙi a cikin hanyar Ɗãgũtu (Shaiɗan). To, ku yãƙi majiɓintan Shaiɗan. Lalle ne kaidin Shaiɗan yã kasance mai rauni. [4.77] Shin, ba ka gani ba zuwa ga waɗanda aka ce musu: "Ku kange hannuwanku, kuma ku tsayar da salla, kuma ku bãyar da zakka."? To a lõkacin da aka wajabta musu yãƙi sai ga wani ɓangare daga cikinsu sunã tsõron mutãne kamar tsõron Allah kõ kuwa mafi tsanani ga tsõron, kuma suka ce: "Ya Ubangijinmu! Don me Ka wajabta yãƙi a kanmu? Me ya hana Ka jinkirta mana zuwa ga wani ajali na kusa?"Ka ce: "Jin dãɗin dũniya kaɗan ne, kuma Lãhira ce mafi alhħri ga wanda ya yi taƙawa. Kuma bã a zãluntar ku da sĩlĩlin hancin gurtsun dabĩno! [4.78] "Inda duk kuka kasance, mutuwa zã ta riske ku, kuma kõ da kun kasance ne a cikin gãnuwõyi ingãtattu!"Kuma idan wani alhħri ya sãme su sai su ce: "Wannan daga wurin Allah ne," kuma idan wata cũta ta sãme su, sai su ce: "Wannan daga gare ka ne."Ka ce: "Dukkansu daga Allah ne." To, me ya sãmi waɗannan mutãne, bã su kusantar fahimtar magana? [4.79] Abin da ya sãme ka daga alhħri, to, daga Allah yake, kuma abin da ya sãme ka daga sharri, to, daga kanka yake, kuma Mun aike ka zuwa ga mutãne, (kana) Manzo, kuma Allah Yã isa ga zama shaida. [4.80] Wanda ya yi ɗã´a ga Manzo, to, haƙĩƙa, yã yi ɗã´a ga Allah. Kuma wanda ya jũya bãya, to, ba Mu aike ka ba don ka zama mai tsaro a kansu. [4.81] Kuma sunã cħwa, "Dã´a" sa´an nan idan sun fita daga wurinka, sai wata ƙungiya daga cikinsu ta kwãna da niyyar wanin abin da take faɗa, alhãli kuwa Allah na rubũta abin da suke kwãna da niyyarsa. Sabõda haka ka kau da kai daga gare su, kuma ka dõgara ga Allah, kuma Allah Yã isa ya zama wakĩli. [4.82] Shin, bã su kula da Alƙur´ãni, kuma dã yã kasance daga wurin wanin Allah haƙĩƙa, dã sun sãmu, a cikinsa, sãɓã wa jũna mai yawa? [4.83] Kuma idan wani al´amari(1) daga aminci ko tsõro ya je musu, sai su wãtsa shi. Dã sun mayar da shi zuwa ga Manzo da ma´abũta al´amari daga gare su, lalle ne, waɗanda suke yin bincikensa, daga gare su, zã su san shi. Kuma bã dõmin falalar Allah bã a kanku da rahamarSa, haƙĩƙa, dã kun bi Shaiɗan fãce kaɗan. [4.84] Sabõda haka, ka(2) yi yãƙi a cikin hanyar Allah, ba a kallafa maka ba, face a kanka, kuma ka kwaɗaitar da mũminai. Akwai tsammãnin Allah Ya kange gãfin waɗanda suka kãfirta, kuma Allah ne Mafi tsananin gãfi, kuma Mafi tsananin azabtãwa. [4.85] Wanda ya yi(3) cħto, cħto mai kyau, zai sãmi rabo daga gare shi, kuma wanda ya yi cħto,cħto mummũna, zai sãmi ma´auni daga gare shi, Kuma Allah Yã kasance, a kan dukkan kõme, Mai ƙayyade lõkaci. [4.86] Kuma idan an gaishe(4) ku da wata gaisuwa, to, ku yi gaisuwa da abin da yake mafi kyau daga gare ta, kõ kuwa ku mayar da ita. Kuma Allah Yã kasance a kan dukkan kõme Mai lissãfi. [4.87] Allah bãbu abin bautawa face Shi. Lalle ne haƙĩƙa Yana tãra(1) ku har zuwa ga Yinin Ƙiyãma bãbu shakka a cikinsa. Kuma wãne ne mafi gaskiya daga Allah ga 1ãbãri. [4.88] To, mħne ne ya sãme(2) ku a cikin munãfukai kun zama ƙungiya biyu, alhãli kuwa Allah ne Ya mayar da su sabõda abin da suka tsirfanta? Shin, kunã nufin ku shiryar da wanda Allah Ya ɓatar ne? Kuma wanda Allah Ya ɓatar to bã zã ka sãmi wata hanya ba zuwa gare shi. [4.89] Suna gũrin ku kãfirta kamar yadda suka kãfirta, dõmin ku kasance daidai. Sabõda haka kada ku riƙi wasu masõya daga cikinsu, sai sun yõ hijira a cikin hanyar Allah. Sa´an nan idan sun jũya, to, ku kãmã su kuma ku kashe su inda duk kuka sãme su. Kuma kada ku riƙi wani masõyi daga gare su ko wani mataimaki. [4.90] Fãce dai waɗanda suke sãduwa zuwa ga wasu mutãne waɗanda a tsakãninku da su akwai alkawari, kõ kuwa waɗanda suke sun je muku (domin) ƙirãzansu sun yi ƙunci ga su yãke ku, kõ su yãƙi mutãnensu. Kuma dã Allah Yã so lalle ne, dã Yã bã su ĩko a kanku, sa´an nan, haƙĩka, su yãke ku. To, idan sun nĩsance ku sa´an nan ba su yãƙe ku ba, kuma suka jħfa sulhu zuwa gare ku, to, Allah bai sanya wata hanya ba, a gare ku, a kansu. [4.91] Za ku sãmi wasu(3) sunã nufin su amintar da ku kuma su amintar da mutãnensu, kõ da yaushe aka mayar da su ga fitina, sai a dulmuyã su a cikinta. To, idan ba su nĩsance ku ba, kuma sun jħfa sulhu zuwa gare ku, kuma sun kange hannuwansu, to, ku kãmã su, kuma ku kashe su inda duk kuka kãmã su, kuma waɗannan, Mun sanya muku dalĩli bayyananne a kansu. [4.92] Kuma bã ya kasancħwa(1) ga mũmini ya kashe wani mũmini, fãce bisa ga kuskure. Kuma wanda ya kashe mũmini bisa ga kuskure, sai ya ´yanta wuya mũmina tare da mĩƙa diyya ga mutãnensa, f?ce idan sun bari sadaka. Sa´an nan idan (wanda aka kashe) ya kasance daga wasu mutãne maƙiya a gare ku, kuma shi mũmini ne, sai ya ´yanta wuya mũmina. Kuma idan ya kasance daga wasu mutãne ne (waɗanda) a tsakãninku da tsakãninsu akwai alkawari, sai ya bãyar da diyya ga mutãnensa, tare da ´yanta wuya mũmina. To, wanda bai sãmi (wuyan ba) sai azumin watanni biyu jħre, dõmin tũba daga Allah. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima. [4.93] Kuma wanda ya kashe wani mũmini da ganganci,(2) to, sakamakonsa Jahannama, yana madawwami a cikinta kuma Allah Yã yi fushi a kansa, kuma Ya la´ane shi, kuma Ya yi masa tattalin azãba mai girma. [4.94] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi tafiya (a cikin ƙasa), dõmin jihãdi, to, ku nħmi bãyani.(3) Kuma kada ku ce wa wanda ya jĩfa sallama zuwa gare ku: "Bã Musulmi kake ba." Kunã nħman hãjar rãyuwar dũniya, to, a wurin Allah akwai ganimõmi mãsu yawa. Kamar wannan ne kuka kasance a gabãnin ku musulunta, sa´an nan Allah Ya yi muku falala. Sabõda haka ku zan nħman bayãni.Lalle ne Allah Yã kasance, ga abin da kuke aikatãwa, Masani. [4.95] Mãsu zama(1) daga barin yãƙi daga mũminai, wasun ma´abũta larũra da mãsu jihãdi a cikin hanyar Allah da dũkiyõyinsu da rãyukansu, bã su zama daidai. Allah Yã fĩfĩta mãsu jihãdi da dũkiyoyinsu da rãyukansu a kan mãsu zama, ga daraja. Kuma dukansu Allah Yã yi musu alkawari da abu mai kyau(2) . Kuma Allah yã fĩfĩta mãsu jihãdi a kan mãsu zama da lãda mai girma. [4.96] Darajõji daga gare Shi da gãfara da rahama. Kuma Allah Yã kasance Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [4.97] Lalle ne, waɗanda malã´ĩku(3) suka karɓi rãyukansu, (alhãli) sunã mãsu zãluntar kansu,sun ce (musu): "A cikin me kuka kasance?" (Su kuma) suka ce: "Mun kasance waɗanda aka raunana a cikin ƙasa." Suka ce: "Ashe ƙasar Allah ba ta kasance mayalwaciya ba, dõmin ku yi hijira a cikinta?" To, waɗannan makõmarsu Jahannama ce. Kuma tã mũnana ta zama makõma. [4.98] Fãce waɗanda aka raunana daga maza da mãtã da yãra waɗanda bã su iya yin wata dabãra, kuma bã su shiryuwa ga hanya. [4.99] To, waɗannan akwai tsammãnin Allah Ya yãfe laifi daga gare su, kuma Allah Yã kasance Mai yãfħwa ne, Mai gãfara. [4.100] Kuma wanda ya yi hijira a cikin hanyar(4) Allah, zai sãmu, a cikin ƙasa, wurãren jũyãwa mãsu yawa da yalwa. Kuma wanda ya fita daga gidansa yana mai hijira zuwa ga Allah da ManzonSa, sa´an nan kuma mutuwa ta riske shi, to, lalle ne, lãdarsa tã auku ga Allah, Kuma Allah Yã kasance, a gare ku, Mai gãfara, Mai jin ƙai. [4.101] Kuma idan kun yi tafiya a cikin ƙasa to, bãbu laifi a kanku ku rage(5) daga salla idan kun ji tsõron waɗanda suka kãfirta su fitine ku. Lalle ne kãfirai sun kasance, a gare ku, maƙiyi bayyananne. [4.102] Kuma idan kã kasance a cikinsu, sai ka tsayar musu da salla, to, wata ƙungiya daga gare su ta tsaya tãre da kai, kuma sai su riƙe makãmansu. Sa´an nan idan sun yi salla, to, sai su kasance daga bãyanku. Kuma wata ƙungiya ta dabam (ta) waɗanda ba su yi sallar ba, ta zo, sa´an nan su yi sallar tãre da kai. Kuma su riƙi shirinsu da makãmansu. Waɗanda suka kãfirta sun yi gũrin dã dai kuna shagala daga makamanku da kãyanku dõmin su karkata a kanku, karkata guda. Kuma bãbu laifi, a kanku idan wata cũta daga ruwan sama ta kasance a gare ku, kõ kuwa kun kasance mãsu jinya ga ku ajiye makãmanku kuma dai ku riƙi shirinku. Lalle ne, Allah Yã yi tattali, ga kãfirai, azãba mai walakantarwa. [4.103] Sa´an nan idan kun ƙãre salla, to ku ambaci Allah tsaye da zaune da a kan sãsanninku. Sa´an nan idan kun natsu, to, ku tsayar da Salla. Lalle ne salla tã kasance a kan mũminai, farilla mai ƙayyadaddun lõkuta. [4.104] Kuma kada ku sassauta a cikin nħman mutãnen idan kun kasance kuna jin zõgi, to, lalle sũ ma, suna jin zõgi kamar yadda kuke jin zõgi. Kuma kuna tsammãni, daga Allah, abin da bã su tsammãni. Kuma Allah Yã kasance Masani Mai hikima. [4.105] Lalle ne, Mũ, Mun saukar(1) , zuwa gare ka, Littãfi da gaskiya, dõmin ka yi hukunci a tsakãnin mutãne da abin da Allah Ya nũna maka, kuma kada ka kasance mai husũma dõmin mãsu yaudara. [4.106] Kuma ka nħmi Allah gãfara. Lalle ne Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai. [4.107] Kuma kada ka yi jãyayya dõmin tunkuɗe wa waɗanda suka yaudari kansu. Lalle ne Allah ba Ya son wanda ya kasance mai yawan hã´inci mai yawan zunubi. [4.108] Suna nħman ɓõyewa daga mutãne kuma bã su nħmanɓõyewa daga Allah, alhãli kuwa Shi Yana tãre da su a lõkacin da suke kwãna da niyyar yin abin da bã Ya yarda da shi daga maganar. Kuma Allah Yã kasance ga abin da suke aikatãwa Mai kħwayħwa. [4.109] Gã ku, yã waɗannan(1) ! Kun yi jidãli, dõmin tunkuɗe musu (kunya) a cikin rãyuwar dũniya, to, wane ne zai yi jidali domin tunkuɗe musu a Rãnar Ƙiyãma? Ko kuwa wãne ne zai kasance wakĩli a kansu? [4.110] Kuma wanda ya aikata cũta kõ kuwa ya zãlunci kansa, sa´an nan kuma ya nħmi Allah gãfara, zai sãmi Allah Mai gãfara, Mai jin ƙai. [4.111] Kuma wanda ya yi tsirfar zunubi, to yanã tsirfarsa ne a kan kansa kawai. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima. [4.112] Kuma wanda ya yi tsiwirwirin kuskure ko kuwa zunubi sa´an nan kuma ya jħfi wani barrantacce da shi, to, lalle ne yã tattali ƙirƙiren ƙarya da zunubi bayyananne. [4.113] Kuma bã dõmin falalar Allah ba, a kanka, da rahamarSa, haƙĩƙa, dã wata ƙungiya daga gare su ta himmatu ga su ɓatar da kai. Kuma bã su ɓatarwa fãce kansu, kuma bã su cũtar ka daga kõme, Kuma Allah Yã saukar da Littãfi da hikima gare ka, kuma Ya sanar da kai abin da ba ka kasance kã sani ba. Kuma falalar Allah tã kasance mai girma a gare ka. [4.114] Bãbu wani alhħri a cikin mãsu yawa daga gãnawarsu(1) fãce wanda ya yi umurni da wata sadaka kõ kuwa wani alhħri kõ kuwa gyãra a tsakãnin mutãne. Wanda ya aikata haka dõmin nħman yardõdin Allah to zã Mu bã shi lãda mai girma. [4.115] Kuma wanda ya sãɓã wa(2) Manzo daga bãyan shiriya tã bayyana a gare shi, kuma ya bi wanin hanyar mũminai, zã Mu jiɓintar masa abin da ya jiɓinta, kuma Mu ƙõne shi da Jahannama. Kuma tã mũnana ta zama makõma. [4.116] Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki da Shi, kuma Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan, ga wanda Yake so. Kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ɓace ɓata mai nĩsa.(3) [4.117] Bã su kiran kõwa, baicin Shi, fãce mãtã kuma bã su kiran kõwa fãce Shaiɗan, mai tsaurin kai. [4.118] Allah Yã la´ane shi. Kuma ya ce: "Lalle ne, zã ni riƙi rabõ yankakke(4) , daga bãyinKa. [4.119] "Kuma lalle ne, inã ɓatar da su, kuma lalle ne inã sanya musu gũri, kuma lalle ne ina umurnin su dõmin su kãtse(5) kunnuwan dabbõbi, kuma lalle ne inã umurnin su dõmin su canza halittar Allah." Kuma wanda ya riƙi Shaiɗan majiɓinci, baicin Allah, to, haƙĩƙa yã yi hasara, hasara bayyananniya. [4.120] Yanã yi musu alkawari, kuma yanã sanya musu gũri, alhãli Shaiɗan bã ya yi musu wani wa´adĩn kõme face ruɗi. [4.121] Waɗannan matattararsu Jahannama ce, kuma bã sãmun makarkata daga gare ta. [4.122] Kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, zã mu shigar da su gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙõramu sunã gudãna a ƙarƙashinsu, sunã mãsu dawwama a cikinsu har abada bisa ga wa´adin Allah tabbatacce. Wãne ne mafi gaskiya daga Allah ga magana? [4.123] (Al´amari) bai zama gũrace- gũracenku ba, kuma(1) ba gũrace- gũracen Mutãnen Littãfi ba ne. Wanda ya aikata mummunan aiki zã a sãka masa da shi kuma bã zai sãmi wani masõyi ba, baicin Allah, kuma bã zai sãmi mataimaki ba. [4.124] Kuma wanda ya yi aiki daga ayyukan ƙwarai, namiji ne ko kuwa mace, alhãli kuwa Yanã mũmini, to, waɗannan sunã shiga Aljanna kuma bã zã a zãlunce su da gwargwadon hancin gurtsun dabĩno ba. [4.125] Kuma wãne ne ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yanã mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar Ibrãhĩm, Yanã mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Yã riƙi Ibrãhĩm badãɗayi(2) . [4.126] Kuma Allah ke da(3) (mallakar) abin da ke cikin sammai da kuma abin da ke cikin ƙasa kuma Allah Yã kasance, ga dukkan, kõme, Mai kħwayewa. [4.127] Sunã yi maka fatawa a cikin sha´anin mãtã. Ka ce: "Allah Yanã bayyana fatawarku a cikin sha´aninsu, da abin da ake karantãwa a kanku a cikin Littãfi, a cikin sha´anin marãyun mãtã waɗanda ba ku bã su abin da aka rubũta musu(4) (na gãdo) ba, kuma kunã kwaɗayin ku aurħ su, da sha´anin waɗanda aka raunana daga yãra, da sha´anin tsayuwarku ga marãyu da ãdalci. Kuma abin da kuka aikata daga alhħri, to, lalle ne, Allah Yã kasance Masani a gare shi." [4.128] Kuma idan wata mace ta ji tsõron ƙiyo daga mijinta kõ kuwa bijirħwa to, bãbu laifi a kansu su yi sulhu a tsakãninsu, sulhu (mai kyau). Kuma yin sulhu ne mafi alhħri. Kuma an halartar wa rayũka yin rõwa. Kuma idan kun kyautata, kuma kuka yi taƙawa, to, lalle ne, Allah Yã kasance, ga abin da kuke aikatãwa, Masani. [4.129] Kuma bã zã ku iya yin ãdalci ba a tsakanin(1) mãtã kõ dã kun yi kwaɗayin yi. Sabõda haka kada ku karkata, dukan karkata, har ku bar ta kamar wadda aka rãtaye. Kuma idan kun yi sulhu, kuma kuka yi taƙawa, to, lalle ne Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai. [4.130] Kuma idan sun rabu, Allah zai wadãtar da kõwanne daga yalwarSa. Kuma Allah Yã kasance Mayalwaci, Mai hikima. [4.131] Kuma Allah ne da mulkin abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun yi wasiyya ga waɗanda aka bai wa Littãfi a gabãninku, da kũ, cħwa ku bi Allah da taƙawa, kuma idan kun kãfirta, to, lalle ne, Allah Yanã da abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin ƙasa. Kuma Allah Yã kasance wadãtacce, Gõdadde. [4.132] Kuma Allah ne da mulkin abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin ƙasa, kuma Allah Yã isa Ya zama wakĩli. [4.133] Idan Yã so, zã Ya tafi da ku, yã kũ mutãne! kuma Ya zo da wasu. Allah Yã kasance a kan haka, Mai ĩkon yi ne. [4.134] Wanda ya kasance(2) Yanã nufin sakamakon dũniya, to, a wurin Allah sakamakon dũniya da Lãhira yake. Kuma Allah Yã kasance Mai ji, Mai gani. [4.135] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kasance mãsu tsayuwa da ãdalci, mãsu shaida(1) sabõda Allah, kuma kõ dã a kanku ne kõ kuwa, mahaifa da mafi kusantar zumunta, ko (wanda ake yi wa shaida kõ a kansa) ya kasance mawadãci kõ matalauci, to, Allah ne Mafi cancanta da al´amarinsu. Sabõda haka, kada ku bĩbiyi son zũciya, har ku karkata. Kuma idan kuka karkatar da magana, kõ kuwa kuka kau da kai, to lalle ne Allah Yã kasance Masani ga abin da kuke aikatãwa. [4.136] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ĩmãni(2) da Allah da Manzonsa, da Littãfin da Ya sassaukar ga ManzonSa da Littãfin nan wanda Ya saukar daga gabãni. To, wanda ya kãfirta da Allah da malã´ikunSa, da LittattafanSa, da ManzanninSa, da Rãnar Lãhira, to, lalle ne yã ɓace, ɓata mai nĩsa. [4.137] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, sa´an nan kuma suka kãfirta, sa´an nan kuma suka yi ĩmani, sa´an nan kuma suka kãfirta sa´an nan kuma suka ƙãra kãfirci, Allah bai kasance Yanã gãfarta musu ba, kuma bã zai shiryar da su ga hanya ba. [4.138] Ka yi wa munãfukai bushãra da cħwa lalle ne sunã da azãba mai raɗaɗi. [4.139] Waɗanda suke riƙon kãfirai masõya, baicin mũminai. Shin sunã nħman izza ne a wurinsu? To, lalle ne izza ga Allah take gabã ɗaya. [4.140] Kuma lalle ne Yã sassaukar(3) muku a cikin Littãfi cħwa idan kun ji ãyõyin Allah, anã kãfirta da su, kuma anã izgili da su, to, kada ku zauna tãre da sũ, sai sun shiga cikin wani lãbãri. Lalle ne kũ, a lõkacin nan misãlinsu kuke. Lalle ne, Allah Mai tãra munãfukai da kãfirai ne a cikin Jahannama gabã ɗaya. [4.141] Waɗanda suke jiran dãko game da ku; har idan wata nasara daga Allah ta kasance a gare ku, sai su ce: "Ashe, ba mu kasance tãre da kũ ba?" Kuma idan wani rabo ya sãmu ga kãfirai sai su ce: "Ashe ba mu rinjãye ku ba, kuma muka tsare ku daga mũminai?" To,Allah ne Yake yin hukunci tsakãninku a Rãnar Ƙiyãma, kuma Allah bã zai sanya hanya ba ga kãfirai a kan mũminai. [4.142] Lalle ne munãfukai sunã yaudarħwa da Allah, alhãli kuwa Shi ne mai yaudararsu; kuma idan sun tãshi zuwa ga salla, sai su tãshi sunã mãsu kasãla. Suna nũnawa mutãne, kuma ba su ambatar Allah sai kaɗan. [4.143] Mãsu kai-kawo ne a tsakãnin wancan; bã zuwa ga waɗannan ba, kuma bã zuwa ga waɗannan ba. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, bã za ka sãmar masa wata hanya ba. [4.144] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi kãfirai masõya, baicin mũminai. Shin, kunã nufin ku sanyã wa Allah dalĩli bayyananne a kanku? [4.145] Lalle ne, manãfukai sunã a magangara mafi ƙasƙanci daga wuta. Kuma bã zã ka sãma musu mataimaki ba. [4.146] Sai waɗanda suka tũba, kuma suka gyãra, kuma suka nħmi fakuwa ga Allah, kuma suka tsarkake addininsu dõmin Allah, to, waɗannan sunã tãre da mũminai, kuma Allah zai bai wa mũminai lãda mai girma. [4.147] Mħne ne Allah zai amfãna da yi maku azãba idan kun gõde, kuma kun yi ĩmãni? Allah Yã ksance Mai gõdiya Masani. [4.148] Allah bã Ya son bayyanãwa da mũnãna daga magana(1) fãce ga wanda aka zãlunta. Kuma Allah Yã kasance Mai ji, Masani. [4.149] Idan kun bayyana alhħri, kõ kuwa kuka ɓõye shi, kõ kuwa kuka yãfe laifi daga cũta, to, lalle ne Allah Yã kasance Mai yãfewa, Mai ikon yi. [4.150] Lalle ne, waɗanda suke kãfirta da Allah da ManzonSa kuma sunã nufin su rarrabe(2) a tsakãnin Allah da manzanninSa, kuma sunã cħwa: "Munã ĩmãni da sãshe, kuma munã kãfirta da sãshe." Kuma sunã nufin su riƙi hanya a tsakãnin wannan. [4.151] Waɗannan sũ ne kãfirai sõsai, kuma Mun yi tattali, dõmin kãfirai, azãba mai walãkantarwa. [4.152] Kuma waɗanda suka yi ĩmãni da Allah da manzanninSa, kuma ba su rarrabe a tsakãnin kõwa ba daga gare su, waɗannan zã Mu bã su ijãrõrinsu, kuma Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai. [4.153] Mutãnen Littãfi sunã tambayar ka ka saukar da wani littãfi daga sama, a kansu, to, lalle ne sun tambayi Mũsã mũfã girma daga wannan, suka ce: "Ka nũna mana Allah bayyane." Sai tsãwa ta kãmã su sabõda zãluncinsu, sa´an nan kuma suka riƙi maraƙi (abin bautãwa) bãyan hujjoji bayyanannu sun je musu. Sa´an nan Muka yãfe laifi daga wancan. Kuma Mun bai wa Mũsã dalĩli bayyananne. [4.154] Kuma Muka ɗaukaka dũtse sãma da su, sabõda alkawarinsu, kuma Muka ce musu: "Ku shiga ƙõfar kunã mãsu tawãli´u," Kuma Muka ce musu: "Kada ku ƙħtare haddi a cikin Asabat," kuma Muka riƙi alkawari mai kauri daga gare su." [4.155] To, sabõda warwarħwarsu ga alkawarinsu, da kãfirtarsu da ãyõyin Allah, da kisansu ga Annabãwa, bã da hakki ba, da maganarsu: "Zukãtanmu sunã cikin rufi." ôa, Allah ne Ya yunƙe a kansu sabõda kãfircinsu, sabõda haka bã zã su yi ĩmãni ba fãce kaɗan. [4.156] Kuma sabõda kãfircinsu da faɗarsu, a kan Maryama, ƙiren ƙarya mai girma. [4.157] Da faɗarsu(1) : "Lalle ne mu, mun kashe Masĩhu ĩsã ɗan Maryama Manzon Allah," alhãli kuwa ba su kashe shi ba, kuma ba su kħre shi ba, kuma amma an kamanta shi ne a garħ su. Lalle ne waɗanda suka sãɓã wa jũna a cikin sha´aninsa lalle ne, sunã shakka daga gare shi, bã su da wani ilmi fãce bin zato kuma ba su kashe shi ba bisa ga yaƙĩni. [4.158] ôa, Allah Ya ɗauke shi zuwa garħ Shi, kuma Allah Yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima. [4.159] Kuma bãbu kõwa daga Mutãnen Littafi(2) , fãce lalle yanã ĩmãni da shi a gabãnin mutuwarsa, kuma a Rãnar Ƙiyãma yana kasancħwa mai shaida, a kansu. [4.160] To, sabõda zãlunci daga waɗanda suka tũba (Yahũdu) Muka haramta musu abũbuwa masu dãɗi waɗanda aka halatta su a gare su, kuma sabõda taushħwarsu daga hanyar Allah da yawa. [4.161] Da karɓarsu ga riba, alhãli kuwa an hana su daga gare ta, da cin su ga dũkiyar mutãne daƙarya. Kuma Muka yi tattali, dõmin kãfirai, azãba mai raɗaɗi. [4.162] Amma tabbatattu(3) a cikin ilmi daga gare su, da mũminai, suna ĩmani da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar daga gabãninka, madalla da masu tsai da salla, da mãsu bãyar da zakka, da mãsu ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Waɗannan zã Mu bã su lãda mai girma. [4.163] Lalle ne Mu, Mun(1) yi wahayi zuwa gare ka, kamar yadda Muka yi wahayi zuwa ga Nũhu da annabãwa daga bãyansa. Kuma Mun yi wahayi zuwa ga Ibrãhĩma da Ismã´ĩla da Is´hãƙa da Yaƙũbu da jĩkõki da ĩsa da Ayũba da Yũnusa da Hãruna da Sulaimãn. Kuma Mun bai wa Dãwũda zabũra. [4.164] Da wasu Manzanni, haƙĩ ƙa, Mun bã da lãbarinsu a gare ka daga gabãni, da wasu manzanni waɗanda ba Mu bã da lãbãrinsu ba a gare ka, kuma Allah Yã yi magana da Mũsã, magana sõsai. [4.165] Manzanni mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kan Allah bãyan Manzannin. Kuma Allah yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima. [4.166] Amma Allah Yanã shaida da abin da Ya saukar zuwa gare ka. Yã saukar da shi da saninSa. Kuma malã´iku sunã shaida. Kuma Allah Yã isa Ya zama shaida. [4.167] Lalle ne, waɗanda suka kãfirta kuma suka kange (wasu mutãne) daga hanyar Allah, haƙĩƙa, sun ɓace, ɓata mai nĩsa. [4.168] Lalle ne waɗanda suka kãfirta, kuma suka yi zãlunci, Allah bai kasance Yana yi musu gãfara ba, kuma bã Ya shiryar da su ga hanya. [4.169] Fãce hanyar Jahannama, sunã mãsu dawwama a cikinta har abada, kuma wannan yã kasance, ga Allah, mai sauƙi. [4.170] Yã kũ mutãne! Haƙĩƙa, Manzo yã je muku da gaskiya daga Ubangijinku. Sabõda haka ku yi ĩmãni yã fi zama alhħri a gare ku. Kuma idan kun kãfirta, to, Allah Yanã da abin da ke cikin sammai da ƙasa. Kuma Allah Yã kasance Masani, Mai hikima. [4.171] Yã Mutãnen Littãfi! Kada ku zurfafã a cikin addininku. Kuma kada ku faɗa, ga Allah, fãce gaskiya. Abin da aka sani kawai, Masĩhu ĩsa ɗan Maryama Manzon Allah ne, kuma kalmarSa, yã jħfa ta zuwa ga Maryama, kuma rũhi ne daga gare Shi. Sabõda haka, ku yi ĩmãni da Allah da manzanninSa, kuma kada ku ce, "Uku". Ku hanu (daga faɗin haka) yã fi zama alhħri a gare ku. Abin da aka sani kawai, Allah Ubangiji ne Guda. TsarkinSa yã tabbata daga wani abin haifuwa ya kasance a gare Shi! Shĩ ne da abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa kuma Allah Yã isa Ya zama wakĩli. [4.172] Masĩhu bã ya ƙyãmar ya kasance bãwa ga Allah, kuma haka malã´ikun nan makusanta. Kuma wanda ya yi ƙyãmar bautarSa kuma yi yi girman kai, to, zai tãra su zuwa gare shi gabã ɗaya. [4.173] To, amma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, to zã Ya cika musu ijãrõrinsu, kuma Yanã ƙãra musu daga falalarSa. Kuma amma waɗanda suka yi ƙyãma, kuma suka yi girman kai, to, zã Ya yi musu azãba, azãba mai raɗɗi kuma bã su samun wani masõyi dõmin kansu, baicin Allah, kuma bã su samun mataimaki. [4.174] Yã kũ mutãne! Haƙĩƙa wani dalĩli daga Ubangijinku yã je muku kuma Mun saukar da wani haske, bayyananne zuwa gare ku. [4.175] To, amma waɗanda suka yi ĩmãni da Allah kuma suka faku a gare Shi, to, zai shigar da su cikin wata rahama daga gare Shi da wata falala, kuma Ya shiryar da su zuwa gare Shi ga tafarki madaidaici. [4.176] Sunã yi maka fatawa.(1) Ka ce: "Allah Yanã bayyana muku fatawa a cikin ´Kalãla."´ Idan mutum ya halaka, ba shi da rħshe kuma yana da ´yar´uwa, to, tana da rabin abin da ya bari, kuma shi yana gãdon ta, idan wani rħshe bai kasance ba a gare ta. Sa´an nan idan (´yan´uwa mãtã) suka kasance biyu, to suna da kashi biyu daga kashi uku ɗin abin da ya bari. Kuma idan sun kasance, ´yan´uwa, maza da mãtã to namiji yana da misãlin rabon mãtã biyu. Allah Yana bayyanawa a gare ku, dõmin kada ku ɓace. Kuma Allah ne, Masani ga dukan kõme. @AL MAA-IDAH Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [5.1] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! ku cika alkawurra. An halatta muku dabbobin jin dãɗi fãce abin da ake karantãwa a kanku, bã kunã mãsu halattar da farauta ba alhãli kuwa kunã mãsu harama. Lalle ne, Allah Yanã hukunta abin da yake nufi. [5.2] Ya kũ waɗanda suka yi ĩmãni! kada ku halattar da ayyukan ibãdar Allah game da hajji, kuma da watã mai alfarma, kuma da hadaya, kuma da rãtayar raƙuman hadaya, kuma da mãsu nufin Ɗãki mai alfarma, sunã neman falala daga Ubangijinsu da yarda. Kuma idan kun kwance harama, to, ku yi farauta. Kuma kada ƙiyayya da wasu mutãne ta ɗauke ku, dõmin sun kange ku daga Masallãci Mai alfarma, ga ku yi zãlunci. Kuma ku taimaki junã a kan aikin ƙwarai da taƙawa. Kuma kada ku taimaki juna a kan zunubi da zãlunci, kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne. [5.3] An haramta muku mũshe da jini da nãman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah a gare shi, da mãƙararriya da jefaffiya da mai gangarõwa da sõkakkiya, da abin da mãsu dãgi suka ci, fãce abin da kuka yanka, da abin da aka yanka a kan gunki (shĩ ma an haramta). Kuma kada ku yi rabo da kibiyoyi na cãca wannan fãsiƙanci ne. A yau waɗanda suka kãfirta sun yanke ƙauna daga addininku. Sabõda haka kada ku ji tsõronsu kuma ku ji tsõroNa. A yau Nã kammalã muku addininku, Kuma Nã cika ni´imaTa a kanku, Kuma Nã yarda da Musulunci ya zama addini a gare ku. To, wanda aka sanya wa lalũra a cikin yunwa mai tsanani, bã yana mai karkata zuwa ga wani zunubi ba, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [5.4] Suna tambayar ka cewa mene ne aka halatta musu? Ka ce: "An halatta muku abũbuwa mãsu dãɗi da abin da kuka sanar (farauta) daga mãsu yin mĩki, kunã mãsu sakinsu daga hannuwanku, kunã sanar da su daga abin da Allah Ya sanar da ku. To, ku ci daga abin da suka kama sabõda ku, kuma ku ambaci sunan Allah a kansa, kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Mai gaugawar sakamako da yawã ne. [5.5] A yau an halatta muku abũbuwa mãsu dãɗi kuma abincin waɗanda aka bai wa Littãfi(1) halal ne a gare ku, kuma abincinku halal ne a gare su, da mãtã mãsu kãmun kai daga muminai da mãtã ´yã´ya daga waɗanda aka bai wa Littãfi a gabãninku idan kun je musu da sadãkõkinsu, kuna mãsu yin aure, ba masu yin zina ba, kuma bã mãsu riƙon abõkai ba. Kuma wanda ya kãfirta da ĩmãni to, lalle ne aikinsa yã ɓãci, kuma shĩ, a cikin Lãhira, yanã daga mãsu hasãra. [5.6] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni ! idan kun tãshi(1) zuwa ga salla, to, ku wanke fuskõkinku da hannuwanku zuwa ga magincirõri, kuma ku yi shãfa ga kãnunku, kuma ku (wanke) ƙafãfunku zuwa idãnun sãwu biyu. Kuma idan kun kasance mãsu janaba, to, ku yi tsarki, kuma idan kun kasance majinyata, kõ kuwa a kan tafiya, kõ kuwa ɗaya daga gare ku ya zo daga k?shi, kõ kuka yi shãfayyar junã da mãtã, sa´an nan ba ku sãmi ruwa ba to ku yi nufin wuri(2) mai kyau, sa´an nan ku yi shãfa ga fuskõkinku da hannuwanku daga gare shi. Allah bã Ya nufi dõmin Ya sanya wani ƙunci a kanku, kuma amma Yanã nufi dõmin Ya cika ni´imarSa a kanku, tsammãninku kunã gõdewa. [5.7] Kuma ku tuna ni´imar Allah akanku da alkawarinku wanda Ya ɗaure ku da shi, a lõkacin da kuka ce: "Mun ji kuma mun yi ɗã´a Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Masani ne ga abin da ke a cikin zukata." [5.8] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kasance mãsu tsayin daka dõmin Allah mãsu shaida da ãdalci. Kuma kada ƙiyayya da wasu mutane ta ɗauke ku a kan bã zã ku yi ãdalci ba. Ku yi ãdalci Shĩ ne mafi kusa ga taƙawa. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Masani ne ga abin da kuke aikatãwa. [5.9] Allah Yã yi wa´adi ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Sunã da wata gãfara da lãda mai girma. [5.10] Kuma waɗanda suka kãfirta, kuma suka ƙaryatã, game da ãyõyinMu, waɗannan su ne abõkan wuta. [5.11] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku tuna ni´imar Allah a kanku a lõkacin da wasu mutãne suka yi niyyar su shimfiɗa hannuwansu zuwa gare ku(1) sai Ya kange hannuwansu daga gare ku, kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma sai muminai su dogara ga Allah kawai. [5.12] Kuma lalle Allah Yã riƙi alkawarin Banĩ lsrã´ ĩla kuma Muka ayyana wakilai gõma shã biyu(2) daga gare su kuma Allah Ya ce: "Lalle ne Nĩ, Inã tãre da ku, haƙĩƙa, idan kun tsayar da salla, kuma kun bãyar da zakka, kuma kun yi ĩmani da manzannĩNa, kuma kuka taimake su, kuma kuka bai wa Allah rance mai kyau, haƙĩƙa, Inã kankare laifukanku daga gare ku, kuma haƙĩƙa, Inã shigar da ku gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙõramu sanã gudãna a ƙarƙashinsu, sa´an nan wanda ya kãfirta a bãyan wannan daga gare ku, to, lalle ne, yã ɓace daga tsakar hanya." [5.13] To, sabõda warwarewarsu ga alkawarinsu Muka la´ane su, kuma Muka sanya zukãtansu ƙeƙasassu, sunã karkatar da magana daga wurãrenta, kuma suka manta da wani yanki daga abin da aka tunãtar da su da shi, kuma bã zã ka gushe ba kana tsinkãyar yaudara daga gare su fãce kaɗan daga gare su. To, ka yãfe laifi daga gare su, kuma ka kau da kai. Lalle ne, Allah Yanã son mãsu kyautatãwa. [5.14] Kuma daga waɗanda suka ce: "Lalle ne mu Nasãra ne" Mun riƙi alkawarinsu, sai suka manta da wani yanki daga abin da aka tunãtar da su da shi, sai Muka shushuta adãwa da ƙeta a tsakãninsu har ya zuwa ga Rãnar Ƙiyãma. Kuma Allah zai bã su lãbari da abin da suka kasance sunã sanã´antawa. [5.15] Yã Mutãnen littãfi! Lalle ne, ManzonMu yã je muku, yanã bayyana muku abu mai yawa daga abin da kuka kasance kunã ɓõyewa daga Littãfi, kuma yanã rangwame daga abu mai yawa. Haƙĩƙa, wani haske da wani Littafi mai bayyanãwa yã je muku daga Allah. [5.16] Dashĩ, Allah Yanã shiryar da wanda ya bi yardarsa zuwa ga hanyõyin aminci, kuma Yanã fitar da su daga duffai zuwa ga haske da izninsa, kuma Yanã shiryar da su zuwa ga hanya madaidaiciya. [5.17] Lalle haƙĩƙa waɗanda suka ce: "Lalle Allah Shĩ ne Masĩhu ɗan Maryama," sun kãfirta. Ka ce: "To, wane ne ke iya mallakar wani abu daga Allah, idan Yã nufi Ya halakar da Masĩhu ɗanMaryama da uwarsa da wanda yake a cikin ƙasa gabã ɗaya?" Kuma Allah ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, Yanã halitta abin da Yake so. Kuma Allah a kan dukkan kõme, Mai ĩkon yi ne. [5.18] Kuma Yahudu da Nasãra sun ce: "Mu ne ɗiyan Allah, kuma masõyansa." Ka ce: "To, don me Yake yi muku azãba da zunubanku? ôa ku mutãne ne daga waɗanda Ya halitta, Yanã gãfartãwa ga wanda Yake so, kuma Yanã azabta wanda Yake so. Kuma Allah ne da mulkin sammai da ƙasa da abin da ke tsakãninsu kuma zuwa gare shi makomã take." [5.19] Yã Mutãnen Littãfi! Lalle ManzonMu yã je muku yanã bayyana muku, a kan lõkacin fatara daga manzanni, dõmin kada ku ce: "wani mai bayar da bushãra bai zo mana ba, kuma haka wani mai gargaɗi bai zo ba." To, haƙĩƙa, mai bãyar da bushãra da mai gargaɗi sunje muku. Kuma Allah ne, a kan dukkan kõme, Mai ĩkon yi. [5.20] Kuma a lõkacin da Musa ya ce wa mutãnensa: "Yã ku mutãnena! Ku tuna ni´imar Allah a kanku; dõmin Yã sanya annabãwa a cikinku, kuma Yã sanya ku sarãkuna, kuma Yã bã ku abin da bai bai wa kõwa ba daga tãlikai." [5.21] "Yã mutãnena! Ku shiga ƙasar nan, abar tsarkakewa, wadda Allah Ya rubuta sabõda ku, kuma kada ku kõma da bãya, har ku juya kunã mãsu hasara." [5.22] Suka ce: "Ya Musã! Lalle ne, a cikinta akwai wasu mutãne mãsu ƙarfi kuma lalle ne bã zã mu shige ta ba sai sun fice daga gare ta, to, idan sun fice daga gare ta, to, lalle ne mu, masu shiga ne." [5.23] Wasu maza biyu(1) daga waɗanda suke tsõron Allah, Allah Yã yi ni´ima a kansu, suka ce: "Ku shiga gare su, daga ƙõfar, dõmin idan kuka shige shi, to, lalle ne ku, mãsu rinjãya ne, kuma ga Allah sai ku dogara idan kun kasance muminai." [5.24] Suka ce: "Ya Musa! Lalle ne mu, bã za mu shige ta ba har abada matuƙar sun dawwama a cikinta sai ka tafi kai da Ubangijinka dõmin ku yi yãƙi. Lalle ne mu, munã a nan zaune." [5.25] Ya ce: "Yã Ubangijina! Lalle ne nĩ, bã ni mallakar kõwa fãce kaina da ɗan´uwãna, sai Ka rarrabe a tsakãninmu da tsakãnin mutãne fãsiƙai." [5.26] (Allah) Ya ce: "To, lalle ne ita abar haramtãwa ce a gare su, shekara arba´in, sunã yin ɗimuwa a cikin ƙasa.(1) Sabõda haka kada ka yi baƙin ciki a kan mutãne fãsiƙai." [5.27] Kuma karantã musu(2) lãbãrin ɗiya biyu(3) na Ãdamu, da gaskiya, a lõkacin da suka bãyar da baiko, sai aka karɓa daga ɗayansu kuma ba a karɓa daga ɗayan ba, ya ce: "Lalle ne zan kashe ka." (Ɗayan kuma) ya ce: "Abin sani dai, Allah Yana karɓã daga mãsu taƙawa ne." [5.28] "Lalle ne idan ka shimfiɗa hannunka zuwa gare ni dõmin ka kashe ni, ban zama mai shimfiɗa hannuna zuwa gare ka ba dõmin in kashe ka. Lalle ne nĩ inã tsõron Allah Ubangijin tãlikai. [5.29] "Lalle ne nĩ inã nufin ka kõma da zunubina game da zunubinka, har ka kasance daga abõkan wuta. Kuma wannan shĩ ne sakamakon azzãlumai." [5.30] Sai ransa ya ƙawãtar masa kashewar ɗan´uwansa, sai kuwa ya kashe shi, sa´an nan ya wayi gari daga mãsu hasãra. [5.31] Sai Allah Ya aiki wani hankãka, yanã tõno a cikin ƙasa dõmin ya nuna masa yadda zai turbuɗe gãwar ɗan´uwansa. Ya ce: "Kaitõna! Nã kãsa in kasance kamar wannan hankãka dõmin in turbuɗe gãwar ɗan´uwana?" Sai ya wãyi gari daga mãsu nadãmã. [5.32] Daga sababin wannan,(1) Muka rubuta a kan Banĩ lsrã´ĩla cewa, lalle ne wanda ya kashe rai bã da wani rai ba, ko ɓarna a cikin ƙasa, to kamar yã kashe mutãne duka ne, kuma wanda ya rãya rai, to, kamar yã rãyar da mutãne ne gabã ɗaya. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, ManzanninMu sun je musu da hujjõji bayyanannu, sa´an nan kuma lalle ne, mãsu yawa daga gare su, a bãyan wannan, haƙĩƙa, mãsuɓarna ne a cikin ƙasa. [5.33] Abin sani kawai sakamakon(2) waɗanda suke Yãƙin Allah da Manzonsa, kuma sunã aiki a cikin ƙasa dõmin ɓarna a kashe su ko kuwa a kere su, kõ kuwa a kakkãtse hannuwansu da ƙafãfunsu daga sãɓãni, ko kuwa a kõre su daga ƙasa. Wannan gare su wulakanci ne a cikin rãyuwar duniya, kuma a Lãhira sunã da wata azãba mai girma. [5.34] Fãce fa waɗanda suka tuba tun a gabãnin ku sãmi ĩko akansu, to, ku sani cewa lalle ne, Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [5.35] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, kuma ku nemi tsari zuwa gare shi, kuma ku yi jihãdi(3) a cikin hanyarsa, tsammãninku, za ku ci nasara. [5.36] Lalle ne waɗanda suka kãfirta, lalle dã sunã da abin da ke a cikin ƙasa gabã ɗaya da misãlinsa tãre da shi, dõmin su yi fansa da shi daga azãbar Rãnar Ƙiyãma, bã a karɓarsa daga gare su, kuma sunã da azãba mai raɗadi. [5.37] Sunã nufin su fita ne daga wuta, kuma ba su zama mãsu fita daga gare ta ba, kuma sunã da azãba zaunanniya. [5.38] Kuma ɓarãwo da ɓarauniya sai ku yanke hannuwansu, bisa sakamako ga abin da suka tsirfanta, a kan azãba daga Allah. Kuma Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima. [5.39] To, wanda ya tuba a bãyan zãluncinsa, kuma ya gyãra (halinsa), to, lalle ne Allah Yanã karɓar tubarsa. Lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [5.40] Shin, ba ka sani ba cewa lalle ne, Allah Shi ne da mulkin sammai da ƙasa, Yanã azãbtar da wanda Yake so, kuma Yanã yin gãfara ga wanda yake so, kuma Allah a dukkan kõme, Mai ĩkon yi ne? [5.41] Yã kai Manzo! Kada waɗanda suke tseren gaugawa a cikin kãfirci su ɓãta maka rai, daga waɗanda suka ce: "Mun yi ĩmãni" da bãkunansu, alhãli zukatansu ba su yi ĩmãnin ba, kuma daga waɗanda suka tuba (watau Yahudu) mãsu yawan saurare ga wasu mutane na dabam waɗanda ba su je maka ba, sunã karkatar da zance daga bãyan wurarensa, sunã cewa: "Idan an bã ku wannan, to, ku karɓa, kuma idan ba a bã ku shĩ ba, to, ku yi sauna."Kuma wanda Allah Ya yi nufin fitinarsa, to bã zã ka mallaka masa kõme ba, daga Allah. Waɗannan ne waɗanda Allah bai yi nufin Ya tsarkake zukãtansu ba. Sunã da kunya a cikin duniya, kuma sunã da wata azãba mai girma a cikin 1ãhira. [5.42] Mãsu yawan saurãre(1) ga ƙarya ne, mãsu yawan ci ga haram, to, idan sun zo maka, sai ka yi hukunci a tsakãninsu kõ ka bijira daga gare su. Kuma idan ka bijira daga gare su, to, bã zã su cuce ka da kõme ba, kuma idan ka yi hukunci, to, sai ka hukunta a tsakãninsu da ãdalci. Lalle ne, Allah Yanã son mãsu ãdalci. [5.43] Kuma yãya suke gabãtar da kai ga hukunci, alhãli a wurinsu akwai Attaura, a cikinta akwai hukuncin Allah, sa´an nan kuma sunã karkacewa a bãyan wannan? waɗannan bã muminai ba ne! [5.44] Lalle ne Mu, Mun saukar da Attaura, a cikinta akwai shiriya da haske Annabãwa waɗanda suke sun sallamã, sunã yin hukunci da ita ga waɗanda suka tuba (Yahudu), da mãlaman tarbiyya, da manyan malamai ga abin da aka neme su da su tsare daga Littãfin Allah, kuma sun kasance, a kansa, mãsu bã da shaida. To, kada ku ji tsõron mutãne kuma ku ji tsõroNa kuma kada ku sayi ´yan kuɗi kaɗan da ãyoyiNa. wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah Ya saukar, to, waɗannan su ne kafirai. [5.45] Kuma Mun rubuta a kansu, a cikinta cewa, lalle (anã kashe) rai sabõda rai, kuma (anã ɗebe) idõ sabõda idõ, kuma (ana katse) hanci sabõda hanci, kuma kunne sabõda kunne kuma haƙori sabõda haƙõri kuma a raunuka a yi sakayya. To, wanda ya yi sadaka da shi, to, shi kaffãra ce a gare shi. Kuma wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah Ya saukar, to, waɗannan su ne azzãlumai. [5.46] Kuma Muka biyar a kan gurãbansu da Ĩsa ɗan Maryama, yãnã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Attaura, kuma Muka bã shi Injĩla a cikinsa akwai shiriya da haske, yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Attaura, kuma shi shiriya ne da wa´azi ga mãsu taƙawa. [5.47] Kuma sai mutãnen injĩla su yi hukunci da abin da Allah ya saukar a cikinta. Kuma wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah ya saukar, to, waɗannan su ne fãsiƙai. [5.48] Kuma Mun saukar da Littãfi zuwa gare ka da gaskiya, yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Littãfi (Attaura da Injĩla), kuma mai halartãwa a kansa. sai ka yi hukunci a tsakãninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bĩbiyi son zũciyõyiniu daga abin da ya zo maka daga gaskiya(1) . Ga kõwanne daga gare ku Mun sanya sharĩa da hanya (ta bin ta). Kuma dã Allah Yã so, dã Yã sanya ku al´umma guda, kuma amma dõmin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya bã ku. Sai ku yi tsere ga ayyukan alheri. Zuwa ga Allah makõmarku take gabã ɗaya. Sa´an nan Ya bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance kunã sãɓãwa a cikinsa. [5.49] Kuma ka yi hukunci a tsakãninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bĩbiyi son zũciyõyinsu, kuma ka yi saunar su fitine ka daga sãshen abin da Allah Ya saukar zuwa gare ka. To, idan sun juya bãya, to, ka sani cewa, kawai Allah yana nufin Ya sãme su da masĩfa ne sabõda sãshen zunubansu. Kuma lalle ne, mãsu yawa daga mutãne, haƙĩƙa, fãsiƙai ne. [5.50] Shin, hukuncin Jãhiliyya(2) suke nema? Kuma wane ne mafi kyau ga hukunci daga Allah sabõda mutãne waɗanda suke yin yaƙĩni (tabbataccen ĩmãni)? [5.51] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi Yahudu da Nasãra majiɓinta. Sãshensu majiɓinci ne ga sãshe. Kuma wanda ya jiɓince su daga gare ku, to, lalle ne shĩ, yanã daga gare su. Lalle Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai. [5.52] Sai ka ga waɗanda a cikin zukatansu akwai cuta, sunã tseren gaugawa a cikinsu, sunã cewa: "Munã tsõron kada wata masĩfa ta sãme mu." To, akwai tsammãnin Allah Ya zo da buɗi, kõ kuwa wani umurni daga wurinSa, har su wãyi gari a kan abin da suka ɓõye a cikin zukatansu, sunã mãsu nadãmã. [5.53] Kuma waɗanda suka yi ĩmãni sunã cewa: "Shin, waɗannan ne waɗanda suka yi rantsuwa da Allah iyãkar rantsuwõyinsu, cewa su, lalle sunã tãre da ku?" Ayyukansu sun ɓãci, sabõda haka suka wãyi gari sunã mãsu hasãra. [5.54] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! wanda ya yi ridda daga gare ku daga addininSa, to, Allah zai zo da wasu mutãne, Yanã son su kuma sunã son Sa, mãsu tawãlu´i a kan muminai mãsu izza a kan kãfirai. Sunã yin, jihãdi a cikin hanyar Allah, kuma bã su tsõron zargin wani mai zargi. Waccan falalar Allah ce, Yanã bãyar da ita ga wanda Yake so. Kuma Allah Mayalwaci ne, Mai ilmi. [5.55] Abin sani kawai, majiɓincinku Allah ne da ManzonSa da waɗanda suka yi ĩmãni,waɗanda suke sunã tsayar da salla kuma sunã bãyar da zakka kuma sunã ruku´i, [5.56] Kuma wanda ya jiɓinci Allah da ManzonSa da waɗanda suka yi ĩmãni, to, ƙungiyar Allah sune mãsu rinjãya. [5.57] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi waɗanda suka riƙi addininku bisa izgili da wãsa, daga waɗanda aka bai wa Littãfi daga gabãninku da kãfirai, masõya, Kuma ku bi Allah da taƙawa idan kun kasance muminai. [5.58] Kuma idan kuka yi kira zuwa ga salla, sai su riƙe ta bisa izgili da wãsa. Wannan dõmin lalle ne su, mutãne ne (waɗanda) bã su hankalta. [5.59] Ka ce: "Ya Mutãnen Littãfi! Shin, kunã ganin wani laifi daga gare mu? Fãce dai dõmin mun yi ĩmãni da Allah da abin da aka Saukar zuwa gare mu da abin da aka saukar daga gabãni, kuma dõmin mafi yawanku fãsiƙai ne." [5.60] Ka ce: "Shin, in gaya muku mafi sharri daga wannan, dõmin sakamako(1) daga wurin Allah? wanda Allah Ya la´ane shi kuma Ya yi fushi da shi, kuma Ya sanya daga gare su birai da aladai, kuma ya bauta wa Ɗãguta. Waɗannan ne mafiya sharrin wuri, kuma mafiya ɓata daga tsakar hanya." [5.61] Kuma idan sun zo muku sai su ce: "Mun yi ĩmãni." Alhãli kuwa haƙĩƙa, sun shigo da kãfirci,kuma su lalle ne, sun fita da shi, kuma Allah ne Mafi sani ga abin da suka kasance sunã ɓõyewa. [5.62] Kuma kana ganin mãsu yawa daga gare su, sunã tseren gaugawa a cikin zunubi da zãlunci da cinsu ga haram. Haƙĩƙa, tir da abin da suka kasance suna aikatãwa. [5.63] Don me Malaman Tarbiyya(2) da manyan malamai (na Yahudu) ba su hanã su daga faɗarsu ga zunubi da cinsu ga haram ba? Haƙiƙa, tir daga abin da suka kasance sunã sanã´antãwa. [5.64] Kuma Yahudu suka ce: "Hannun Allah abin yi wa ƙuƙumi ne.(3) " An sanya hannuwansu a cikin ƙuƙumi! Kuma an la´ane su sabõda abin da suka faɗa. ôa, hannuwanSa biyu shimfiɗaɗɗu ne, Yanã ciyarwa yadda Yake so. Kuma lalle ne abin da aka saukar zuwa gare ka yanã ƙãra wa mãsu yawa daga gare su, girman kai da kãfirci. Kuma Mun jefa a tsakãninsu, ƙiyayya da ƙeta, zuwa Rãnar Ƙiyãma, kõ da yaushe suka hura wata wuta dõmin yãƙi, sai Allah Ya bice ta. Sunã aiki a cikin ƙasa dõmin ɓarna, alhãli kuwa Allah bã Ya son mãsu fasãdi. [5.65] Kuma dã dai lalle Mutãnen Littãfi sun yi ĩmãni, kuma sun yi taƙawa, haƙĩƙa, dã Mun kankare miyãgun ayyukansu daga gare su, kuma dã Mun shigar da su gidãjen Aljannar Ni´ima. [5.66] Kuma dã dai lalle su, sun tsayar da Attaura da Injĩla da abin da aka saukar zuwa gare su daga Ubangijinsu, haƙĩƙa, dã sun ci daga bisansu da kuma daga ƙarƙashin ƙafãfunsu. Daga gare su akwai wata al´umma mai tsakaitãwa kuma mãsu yawa daga gare su, abin da suke aikatawa yã munana. [5.67] Yã kai Manzo! Ka iyar da(1) abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka. Kuma idan ba ka aikata ba, to, ba ka iyar da manzancinSa ba ke nan. Kuma Allah Yanã tsare ka daga mutãne. Lalle ne, Allah bã Ya shiryar da mutãne kãfirai. [5.68] Ka ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi! Ba ku zama a kan kõme ba, sai kun tsayar da Attaura da Injĩla da abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku."Kuma lalle ne, abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka, yanã ƙara wa mãsu yawa daga gare su girman kai da kãfirci. To, kada ka yi baƙin ciki a kan mutãne kãfirai. [5.69] Lalle ne, waɗanda suka yi ĩmãni da waɗanda sukatuba (Yahũdu) da Karkatattu da Nasãra, wanda ya yi ĩmãni da Allahda Rãnar Lãhira, kuma ya aikata aiki na ƙwarai, to, bãbu tsõro a kansu, kuma bã su zamo sunã baƙin ciki ba. [5.70] Lalle ne haƙĩƙa Mun riƙi alkawarin Bani Isrã´ĩla, kumaMun aiki manzanni zuwa gare su, ko da yaushe wani manzo ya je musu da abin da rãyukansu bã su so, wani ɓangare sun ƙaryata, kuma wani ɓangare sunã kashewa, , [5.71] Kuma suka yi zaton cewa wata fitina bã zã ta kasance ba sai Suka makanta, kuma suka kurubta, sa´an nan Allah Ya karɓi tuba a gare su, sa´an nan suka makanta kuma suka kurunta mãsu yawa daga gare su, alhãli Allah Mai gani ne ga abin da suke aikatãwa. [5.72] Lalle ne haƙĩƙa waɗanda(1) suka ce: "Lalle ne Allah, shĩne Masĩhu, ɗan Maryama," sun kãfirta. Alhãli kuwa Masĩhu yã ce: "Yã Banĩ Isrã´ĩla! Ku bauta wa Allah Ubangijina, kuma Ubangijinku." Lalle ne shĩ, wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne, Allah Yã haramta masa Aljanna. Kuma bãbu wasu mataimaka ga azzãlumai. [5.73] Lalle ne, haƙĩƙa, waɗanda suka ce: "Allah na ukun uku ne," sun kãfirta, kuma babu wani abin bautãwa fãce Ubangji Guda. Kuma idan ba su hanu daga abin da suke faɗa ba, haƙĩƙa, wata azãba mai raɗaɗi tãnã shãfar waɗanda suka kãfirta daga gare su. [5.74] shin fã, bã su tuba zuwa ga Allah, kuma su neme Shi gãfara, alhãli kuwa Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai? [5.75] Masĩhu ɗan Maryama bai zama ba fãce Manzo ne kawai, haƙĩƙa, manzanni sun shige dage gabãninsa, kuma uwarsa siddika(2) ce. Sun kasance sunã cin abinci. Ka duba yadda Muke bayyana musu ãyõyi. Sa´an nan kuma ka duba yadda ake karkatar da su. [5.76] Ka ce: "Ashe kunã bauta wa, baicin Allah, abin da ba ya mallakar wata cuta sabõda ku kuma haka wani amfani(3) alhãli kuwa Allah Shi ne Mai ji, Masani?" [5.77] Ka ce: "Yã ku Mutanen Littãfi! Kada ku zurfafa a cikin addininku, abin da bã gaskiya ba, kuma kada ku bĩbiyi son zuciyõyin waɗansu mutãne waɗanda suka riga suka ɓace a gabãni, kuma suka ɓatar da wasu mãsu yawa, kuma suka ɓace daga tsakar hanya." [5.78] An la´ani waɗanda suka kãfirta daga Banĩ Isrã´ĩla a kan harshen Dãwuda da Ĩsa ɗan Maryama. wannan kuwa sabõda sãɓãwar da suka yi ne, kuma sun kasance suna ta´addi(1) . [5.79] Sun kasance bã su hana juna daga abin ƙi, wanda suka aikata. Haƙĩƙa abin da suka kasancesunã aikatãwa yã munana. [5.80] Kana ganin mãsu yawa daga gare su, sunã jiɓintar waɗanda suka kãfirta. Haƙĩƙa tir da abin da rãyukansu suka gabãtar sabõda su, watau Allah Yã yi fushi da su, kuma a cikin azãba su mãsu dawwama ne [5.81] Kuma dã sun kasance sunã ĩmãni da Allah da Annabi da abin da aka saukar zuwa gare shi, dã ba su riƙe su masõya ba. Kuma amma mãsu yawa daga gare su, fãsiƙai ne. [5.82] Lalle ne kana sãmun mafiya tsananin mutãne a adãwa ga waɗanda suka yi ĩmãni,Yahudu ne da waɗanda suka yi shirki. Kuma lalle ne kanã sãmun mafiya kusantarsu a sõyayya ga waɗanda suka yi ĩmãni su ne waɗanda suka ce: "Lalle mu ne Nasãra." Wancan kuwa sabõda akwai Ƙissawa da ruhubãnãwa(2) daga cikinsu. Kuma lalle ne su, bã su yin girman kai. [5.83] Kuma idan suka ji abin da aka saukar zuwa ga Manzo, kanã ganin idanunsu sunã zubar da hawãye, sabõda abin da suka sani daga gaskiya, sunã cewa: "Yã Ubangijinmu! Mun yi ĩmãni, sai ka rubuta mu tãre da mãsu shaida. [5.84] "Kuma mene ne yake gare mu, bã zã mu yi ĩmãni da Allah ba, da kuma abin da ya zo mana daga gaskiya, kuma munã gurin Ubangijinmu Ya shigar da mu tãre da mutãne sãlihai?" [5.85] Sabõda haka, Allah Yã sãkã musu, dõmin abin da suka faɗa da gidãjen Aljanna (waɗanda) ƙõramu sunã gudãna a ƙarƙashinsu, sunã madawwama a cikinsu, kuma wannan ne sakamakon mãsu kyautatãwa. [5.86] Kuma waɗanda suka kãfirta kuma suka ƙaryata game da ãyõyinMu, waɗancan ne abõkan Wuta. [5.87] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku haramta abubuwa mãsu dãɗi da Allah Ya halatta muku, kuma kada ku ƙetare haddi. Lalle ne, Allah bã Ya son mãsu ƙetare haddi.(1) [5.88] Kuma ku ci daga abin da Allah Ya azurta ku, halat mai daɗi, kuma ku bi Allah da taƙawa, wanda yake ku, mãsu ĩmãni ne da shi. [5.89] Allah bã Ya kãmã ku sabõda yãsassa(2) a cikin rantsuwõyinku, kuma amma Yanã kãmã ku da abin da kuka ƙudurta rantsuwõyi (a kansa). To, kaffãrarsa ita ce ciyar da miskĩni gõma daga matsakaicin abin da kuke ciyar da iyãlanku, kõ kuwa tufãtar da su, kõ kuwa ´yantãwar wuya. Sa´an nan wanda bai sãmu ba, sai azumin kwãna uku. Wannan ne kaffãrar rantsuwõyinku, idan kun rantse. Kuma ku kiyãye rantsuwoyinku. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ãyoyinsa, tsammãninku kunã gõdewa. [5.90] Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, giya da cãca da refu da kiban ƙuri´a,(1) ƙazanta ne daga aikin shaiɗan, sai ku nĩsance shi, wa la´alla ku ci nasara. [5.91] Abin sani kawaĩ Shaiɗan yanã nufin ya aukar da adãwa da ƙeta a tsakãninku, a cikin giya da cãca, kuma ya kange ku daga ambaton Allah, kuma daga sallah. To, shin, ku mãsu hanuwa ne? [5.92] Ku yi ɗã´a ga Allah, kuma ku yi ɗã´a ga Manzo, kuma ku kiyãye. To, idan kun jũya, to, ku sani abin da kawai yake kan ManzonMu, iyarwa bayyananniya. [5.93] Bãbu laifi a kan waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, a cikin abin da suka ci, idan sun yi taƙawa kuma suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sa´an nan suka yi taƙawa kuma suka yi ĩmãni,sa´an nan kuma suka yi taƙawa kuma suka kyautata.(2) Kuma Allah Yana son mãsu kyautatãwa. [5.94] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Lalle ne, Allah zai jarraba ku da wani abu, daga farauta, hannuwanku da mãsunku sunã sãmun sa dõmin Allah Ya san wanda yake tsoron Sa a fake. To, wanda ya yi ta´addi a bãyan wannan, to, yanã da azãba mai raɗaɗi. [5.95] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku kashe farauta alhãli kunã mãsu harama.(3) Kuma wanda ya kashe shi daga gare ku, yanã mai ganganci, sai sakamako misãlin abin da ya kashe, daga dabbõbin ni´ima, ma´abuta ãdalci biyu daga cikinku sunã yin hukunci da shi. Ya zama hadaya mai isa ga Ka´aba ko kuwa kaffãra da abincin miskĩnai ko kuwa a matsayinsa ya yi azumi dõmin ya ɗanɗani masifar al´amarinsa. Allah Yã yafe laifi daga abin da ya gabãta. Kuma wanda ya kõma, to, Allah zai yi azãbar rãmuwa daga gare shi, kuma Allah Mabuwãyi ne, ma´abũcin azabãr rãmuwa. [5.96] An halatta muku farautar ruwa da abincinsa dõmin jin dãɗi a gare ku, kuma dõmin matafiya. Kuma an haramta farautar tudu a kanku, matuƙar kun dawwama mãsu harama. Kuma ku bi Allah da taƙawa, wanda yake zuwa gare Shi ne ake tãra ku. [5.97] Allah Ya sanya Ka´aba Ɗaki Tsararre, ma´aunin addini ga mutane, kuma Yã sanya watã Mai alfarma da hadaya da rãtayõyin Allah Yã san abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, kuma cewa lalle Allah, ga dukkan, kõme, Masani(1) ne. [5.98] Ku sani cewa lalle Allah Mai tsananin uƙuba ne, kuma lalle Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [5.99] Bãbu abin da yake a kan Manzo, sai iyarwa, kuma Allah Yanã sanin abin da kuke bayyanãwa da abin da kuke ɓõyewa. [5.100] Ka ce: "Mummuna da mai kyau bã su daidaita, kuma kõ dã yawan mummuan yã bã ka sha´awa. Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, yã ma´abuta hankula ko la´alla zã ku ci nasara." [5.101] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku yi tambaya ga abubuwa, idan an bayyana muku (hukuncinsu) su ɓãta muku rai. Kuma idan kuka yi tambaya a gare su a lõkacin(2) da ake saukar da Alƙur´ãni, zã a bayyana maku. Allah Yã yãfe laifi daga gare su, Allah Mai gãfara ne, Mai haƙuri. [5.102] Lalle ne wasu mutãne sun tambaye su daga gabãninku, sa´an nan kuma suka wãyi gari da su sunã kãfirai. [5.103] Kuma Allah bai sanya wata bahĩra ba, kuma haka sã´iba, kuma haka wasĩla, kuma haka hãmi,(3) amma waɗanda suka kãfirta, su suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, kuma mafi yawansu bã su hankalta. [5.104] Kuma idan aka ce musu: "Ku zo zuwa ga abin da Allah Ya saukar, kuma zuwa ga Manzo," sai su ce: "Mai isarmu shi ne abin da muka iske ubanninmu a kansa." Shin, kuma kõ dã ubanninsu sun kasance bã su sanin kõme kuma bã su shiryuwa? [5.105] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku lazimci(1) rãyukanku, wanda ya ɓace bã zai cuce ku ba idan kun shiryu, zuwa ga Allah makõmarku take gabã ɗaya. Sa´an nan Ya bã ku lãbari ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa. [5.106] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Shaidar(2) tsakãninku, idan mutuwa ta halarci ɗayanku, a lõkacin wasiyya, maza biyu ne ma´abuta ãdalci daga gare ku, kõ kuwa wasu biyu daga wasunku idan kun tafi a cikin ƙasa sa´an nan masĩfar mutuwa ta sãme ku. Kunã tsare su daga bãyan salla har su yi rantsuwa da Allah; idan kun yi shakka: "Bã mu sayen kuɗi da shi, kõ dã ya kasance ma´abucin zumunta kuma bã mu ɓõye shaidar Allah. Lalle ne mu, a lõkacin, haƙĩƙa, munã daga mãsu zunubi." [5.107] To, idan aka gane cewa lalle sũ, sun cancanci zunubi to sai wasu biyu su tsayu matsayinsu daga waɗanda suka karɓa daga gare su, mutãne biyu mafiya cancanta, sa´an nan su yi rantsuwa da Allah: "Lalle ne shaidarmu ce mafi gaskiya daga shaidarsu, kuma ba mu yi zãlunci ba. Lalle mu, a lõkacin haƙĩƙa, munã daga azzãlumai." [5.108] Wannan ne mafi kusantar su zo da shaida a kan fuskarta kõ kuwa su yi tsõron a tũre rantsuwõyi a bãyan rantsuwõyinsu. Kuma ku bi Allah da taƙawa kuma ku saurara, kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne fãsiƙai. [5.109] A ranar da Allah Yake tãra manzanni sa´an nan Ya ce: "Mene ne aka karɓa muku?" (Zã) su ce: "Bãbu ilmi a gare mu. Lalle ne Kai, Kai ne Masanin abubuwan fake."(1) [5.110] A lõkacin da Allah Ya ce: "Yã Ĩsã ɗan Maryama! Ka tuna ni´ima Ta a kanka, kuma a kan mahaifiyarka, a lõkacin da Na ƙarfafa ka da Rũhul Ƙudusi, kanã yiwa mutãne magana a cikin shimfiɗar jariri, da kuma kanã dattijo. Kuma a lõkacin da Na sanar da kai rubutu da hikima da Attaura da Injĩla, kuma a lõkacin da kake yin halitta daga lãkã kamar surar tsuntsu da izinĩNa, sa´an nan ka hura a cikinta sai ta zama tsuntsu da izinĩNa, kuma kanã warkar da haifaffen makaho da kuturu, da izinĩNa, kuma a lõkacin da kake fitar da matattu da izinĩNa, kuma a lõkacin da Na kange Banĩ Isrã´ĩla daga gare ka, a lõkacin da ka je musu da hujjõji bayyanannu, sai waɗanda suka kãfirta daga cikinsu suka ce: ´Wannan bã kõme ba ne, fãce sihiri bayyananne.´ [5.111] "Kuma a lõkacin da Na yi wahayi zuwa ga Hawãriyãwa(2) cewa ku yi ĩmãni da Ni, kuma da ManzoNa. Suka ce: "Mun yi ĩmãni, kuma ka shaida da cewa lalle mu, mãsu sallamãwa ne." [5.112] A lõkacin da Hawarãyãwa suka ce: "Ya Ĩsa ɗan Maryam! shin, Ubangijinka Yanã iyãwa Ya saukar da kaɓaki a kanmu daga samã?" (Ĩsã) Ya ce: "Ku bi Allah da taƙawa idan kun kasance muminai." [5.113] Suka ce: "Munã nufin mu ci daga gare shi ne, kuma zukãtanmu su natsu kuma mu san cewa lalle ne, kã yi mana gaskiya, kuma mu kasance daga mãsu shaida a kansa." [5.114] Ĩsã ɗan Maryam ya ce: "Yã Allah. Ubangijinmu! Ka saukar da kaɓaki a kanmu daga sama dõmin ya zama ĩdi ga na farkonmu da na ƙarshenmu, kuma ya zama ãyã daga gare Ka. Ka azurta mu, kuma Kai ne Mafĩfĩcin mãsu azurtawa." [5.115] Allah Ya ce: "Lalle ne Nĩ mai saukar da shi ne a kanku sa´an nan wanda ya kãfirta daga gare ku, to, lalle ne Nĩ, Inã azabta shi, da wata azãba wadda bã Ni azabta ta ga kõwa daga tãlikai." [5.116] Kuma a lõkacin da Allah Ya ce: "Yã Ĩsã ɗan Maryama! Shin, kai ne ka ce wa mutãne, ´Ku riƙe ni, ni da uwata, abubuwan bautãwa biyu, baicin Allah?" (Ĩsã) Ya ce: "Tsarkinka yã tabbata! Bã ya kasancewa a gare ni, in faɗi abin da bãbu wani hakki a gare ni. Idan nã kasance nã faɗe shi, to lalle Ka san shi, Kanã sanin abin da ke a cikin raina, kuma bã ni sanin abin da ke a cikin ranka. Lalle ne Kai Masanin abubuwan fake ne." [5.117] "Ban faɗa musu ba fãce abin da Ka umurce ni da shi; watau: ´Ku bauta wa Allah Ubangijina kuma Ubangijinku;´ kuma nã kasance mai shaida a kansu matuƙar nã dawwama a cikinsu, sa´an nan a lõkacin da Ka karɓi raina(1) Kã kasance Kai ne mai tsaro a kansu, kuma Kai, a kan dukkan kõme, Halartacce ne. [5.118] "Idan Ka azabta su, to lalle ne su, bãyinKa ne, kuma idan Ka gãfarta musu, to, lalle ne Kai ne Mabuwayi Mai hikima." [5.119] Allah Ya ce: "Wannan ce rãnar da mãsu gaskiya, gaskiyarsu take amfãninsu. Sunã da gidãjen Aljanna, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwama a cikinsu har abada. Allah Yã yarda da su, kuma sun yarda da Shi. wannan ne babban rabo mai girma." [5.120] Allah ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a cikinsu kuma shi, a kan dukkan kõme Mai ĩkon yi ne. @AL AN'AAM Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [6.1] Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya halitta sammai da ƙasa, kuma Ya sanya duffai da haske(1) , sa´an nan kuma waɗanda suka kãfirta, da Ubangijinsu suke karkacewa. [6.2] Shi ne wanda Ya halitta ku daga lãkã, sa´an nan kuma Ya yanka ajali alhãli wani ajali ambatacce yanã wurinSa. Sa´an nan kuma ku kunã yin shakka. [6.3] Kuma Shĩ ne Allah a cikin sammai, kuma a cikin ƙasa Yanã sanin asĩrinku da bayyanenku, kuma Yanã sanin abin da kuke yi na tsirfa. [6.4] Kuma wata ãyã daga Ubangijinsu ba zã ta jħ musu ba, fãce su kasance, daga gare ta, mãsu bijirħwa. [6.5] Sabõda haka, lalle sun ƙaryata (Manzo) game da gaskiya, a lõkacin da ta jħ musu, to lãbãrun abin da suka kasance sunã izgili da shi, zã su jħ musu. [6.6] Shin, ba su gani ba, da yawa Muka halakar da wani ƙarni daga gabãninsu, Mun mallaka musu, a ckikin ƙasa, abin da ba Mu mallaka muku ba kuma Muka saki sama a kansu tanã ta zuba, kuma Muka sanya kõguna sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sa´an nan Muka halakã su sabõda zunubansu kuma Muka ƙãga halittar wani ƙarni na dabam daga bayansu? [6.7] Kuma dã Mun sassaukar da wani littãfi, zuwa gare ka, a cikin takarda, sa´an nan suka taɓa shi da hannuwansu, lalle dã waɗanda suka kãfirta sun ce: "Wannan bai zama ba, face sihiri bayyananne." [6.8] Suka ce: "Don me ba a saukar da wani malã´ika ba a gare shi?" To dã Mun saukar da malã´ika haƙĩƙa dã an hukunta al´amarin(2) sa´an nan kuma ba zã a yi musu jinkiri ba. [6.9] Kuma dã Mun sanya malã´ika ya zama manzo lalle ne dã Mun mayar da shi mutum, kuma dã Mun rikita musu abin da suke rikitãwa. [6.10] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili da manzanni daga gabaninka, sai waɗanda suka yi izgilin, abin da suka kasance sunã izgili da shi ya fãɗa musu. [6.11] Ka ce: "Ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa´an nan kuma ku dũba yadda ãƙibar mãsu ƙaryatãwa ta kasance." [6.12] Ka ce: "Na wãne ne abin da yake a cikin sammai da ƙasa?" Ka ce: "Na Allah ne." Yã wajabta rahama ga kanSa. Lalle ne Yanã tãra ku zuwa ga Rãnar Ƙiyãma, babu shakka a gare Shi. Waɗanda suka yi hasãrar rãyukansu, to, sũ ba zã su yi ĩmani ba." [6.13] "Kuma Shĩ ne da mallakar abin da ya yi kawaici a cikin dare da yini, kuma Shi ne Mai ji, Masani." [6.14] Ka ce: "Shin, wanin Allah nike riƙo majiɓinci, (alhãli Allah ne ) Mai ƙãga halittar sammai da ƙasa, kuma Shi, Yanã ciyarwa, kuma ba a ciyar da Shi?" Ka ce: "Lalle ne nĩ, an umurce ni da in kasance farkon wanda ya sallama, kuma kada lalle ku kasance daga mãsu shirki." [6.15] Kace: "Lalle ne nĩ inã tsõron azãbar Yini Mai girma, idan nã sãɓã wa Ubangijina." [6.16] "Wanda aka jũyar da shi daga gare shi, a wannan Rãnar, to, lalle ne,( Allah) Yã yi masa rahama, Kuma wannan ne tsĩra bayyananniya." [6.17] "Idan Allah Ya shãfe ka da wata cũta, to, babu mai kuranyħwa gare ta, fãce Shĩ, kuma idanYa shãfe ka da wani alhħri to shĩ ne, a kan kõme, Mai ĩkon yi." [6.18] "Kuma Shĩ ne mai Tanƙwasa a kan bayinSa, kuma Shi ne Mai hikima, Masani." [6.19] Ka ce: "Wane abu ne mafi girma ga shaida?" Ka ce: "Allah ne shaida a tsakãnina da tsakaninku. Kuma an yiwo wahayin wannan Alƙur´ãni dõmin in yi muku gargaɗi da shi, da wanda lãbãri ya kai gare shi. Shin lalle ne ku, haƙĩƙa, kunã shaidar cħwa, lalle ne tãre da Allah akwai wasu abũbuwan bautawa?" Ka ce: "Bã zan yi shaidar ( haka) ba." Ka ce: "Abin sani, Shi ne Abin bautãwa Guda kumã lalle ne nĩ barrantacce ne daga abin da kuke yi na shirki." [6.20] Waɗanda Muka bã su Littãfi sunã sanin sa(1) kamar yadda suke sanin ɗiyansu. Waɗanda suka yi hasãrar rãyukansu, to, sũ bã su yin ĩmãni. [6.21] Wãne ne mafi zãlunci daga wanda yake ƙirƙira karya ga Allah, kõ kuwa ya ƙaryata game da ãyõyinsa? Lalle ne shĩ, azzalumai bã zã su ci nasara ba. [6.22] Kuma rãnar da Muka tãra su gabã ɗaya, sa´an nan Mu ce wa waɗanda suka yi shirki: "Inã abõkan tãrayyarku waɗanda kuka kasance kunã riyãwa?" [6.23] Sa´an nan kuma fitinarsu ba ta kasance ba, fãce dõmin sun ce: "Munã rantsuwa da Allah Ubangijinmu, ba mu kasance mãsu yin shirki ba." [6.24] Ka dũba yadda suka ƙaryata kansu! Kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙira ƙaryarsa, ya ɓace daga gare su. [6.25] Kuma daga cikinsu akwai wanda yake saurãre gare ka. Kuma Mun sanya abũbuwan rufi a kan zukãtansu dõmin kada su fahimcħ shi kuma a cikin kunnuwansu (Mun sanya) wani nauyi. Kuma idan sun ga kõwace ãyã bã zã su yi ĩmãni da ita ba har idan sunjħ maka sunã jãyayya da kai, waɗanda suka kãfirta sunã cħwa: "Wannan bai zama ba fãce tãtsũniyõyin mutãnen farko." [6.26] Kuma sunã hanãwa daga gare shi, kuma sunã nĩsanta daga gare shi, kuma bã su halakarwa, fãce kansu, kuma bã su sansancħwa. [6.27] Kuma dã kanã gani, a lõkacin da aka tsayar da su a kan wuta, sai suka ce: "Yã kaitõnmu! Dã ana mayar da mu, kuma bã zã mu ƙaryata ba daga ãyõyin Ubangijinmu, kuma zã mu kasance Daga mũminai." [6.28] ôaha, abin da suka kasance suna ɓõyħwa, daga gabãni, ya bayyana a gare su. Kuma dã an mayar da su, lalle dã sun kõma ga abin da aka hana su daga barinsa. Kuma lalle ne sũ, haƙĩƙa, maƙaryata ne. [6.29] Kuma suka ce: "Ba ta zama ba, fãce rayuwarmu ta duniya, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba." [6.30] Kuma dã kana gani, a lõkacin da aka tsayar da su ga UbangiJinsu, Ya ce: "Ashe wannan bai zama gaskiya ba?" Suka ce: "Nã´am, muna rantsuwa da Ubangijinmu!" Ya ce: "To ku ɗanɗani azaba sabõda abin da kuka kasance kuna yi na kãfirci." [6.31] Lalle ne waɗanda suka ƙaryata game da gamuwa da Allah sun yi hasara, har idan Sa´a ta je musu kwatsam, sai su ce: "Yã nadãmarmu a kan abin da muka yi sakaci a cikinta!" Alhãli kuwa su suna ɗaukar kayansu masu nauyi a kan bayayyakinsu. To, abin da suke ɗauka yã mũnana. [6.32] Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba, fãce wãsa da shagala, kuma lalle ne, Lãhira ce mafi alhħri ga waɗanda suka yi taƙawa. Shin, ba za ku yi hankali ba? [6.33] Lalle ne Muna sani cewa haƙĩƙa, abin da suke faɗa yana ɓãta maka rai. To, lalle ne su, bã su ƙaryata ka (a cikin zukatansu ) kuma amma azzãlumai da ãyõyin Allah suke musu. [6.34] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an ƙaryata manzanni daga gabãninka, sai suka yi haƙuri a kan abin da aka ƙaryata su, kuma aka cũtar da su, har taimakonMu ya je musu, kuma babu mai musanyãwa ga kalmõmin Allah. Kuma lalle ne (abin da yake natsar da kai) ya zo maka daga lãbãrin (annabãwan) farko. [6.35] Kuma idan yã kasance cewa finjirewarsu tã yi nauyi a gare ka, to, idan kana iyãwa, ka nemi wani ɓullõ a cikin ƙasa, kõ kuwa wani tsãni a cikin sama dõmin ka zo musu da wata ãyã, ( sai ka yi). Kuma dã Allah Yã so haƙĩƙa dã Yã tãra su a kan shiriya. Sabõda haka, kada lalle ka kasance daga jãhilai. [6.36] Abin sani kawai, waɗanda suke saurare ne suke karɓãwa, kuma matattu Allah Yake tãyar da su, Sa´an nan kuma zuwa gare Shi ake mayar da su. [6.37] Kuma suka ce: "Don me ba a saukar da ãyã ba, a kansa, daga Ubangjinsa?" Ka ce: "Lalle ne Allah Mai ĩko ne a kan Ya saukar da ãyã, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba." [6.38] Kuma bãbu wata dabba a cikin ƙasa kuma bãbu wani tsuntsu wanda yake tashi da fukafukinsa fãce al´umma ne misãlanku. Ba Mu yi sakacin barin kõme ba a cikin Littãfi, sa´an nan kuma zuwa ga Ubangjinsu ake tãra su. [6.39] Kuma waɗanda suka ƙaryata gameda ãyõyinMu, kurãme ne kuma bebãye, acikin duffai. Wanda Allah Ya so Yanã ɓatar da shi, kuma wanda Ya so zai sanya shi a kan hanya madaidaiciya. [6.40] Ka ce: "Shĩn, kun gan ku, idan azãbar Allah ta zo muku, kõ Sã´ar Tashin Kiyãma ta zo muku, shin wanin Allah kuke kira, idan dai kun kasance mãsu gaskiya?" [6.41] "ôa, Shĩ dai kuke kira sai Ya kuranye abin da kuke kira zuwa gare Shi, idan Ya so, kuma kunã mantãwar abin da kuke yin shirkin tãre da shi." [6.42] Kuma lalle Mun aika zuwa ga al´ummai daga gabãninka, sai Muka kãmã su da tsanani da cũta, tsammãninsu zã su ƙanƙan da kai, [6.43] To, don me, a lõkacin da tsananinMu ya jħ musu ba su yi tawãlu´i ba? Kuma amma zukatansu sun ƙħƙashe kuma shaiɗan yã ƙawãta musu abin da suka kasance sunã aikatãwa. [6.44] Sa´an nan kuma a lõkacin da suka manta da abin da aka tunãtar da su da shi, sai Muka bũɗe, a kansu, ƙõfõfin dukkan kõme, har a lõkacin da suka yi farin ciki da abin da aka ba su, Muka kãmã su, kwatsam, sai gã su sun yi tsuru tsuru. [6.45] Sai aka katse ƙarshen mutãnen, waɗanda suka yi zãlunci. Kuma gõdiya tã tabbata ga Allah Ubangijin tãlikai. [6.46] Ka ce: "Shin, kun gani, idan Allah Ya riƙe jinku, da gannanku, kuma Ya sanya hãtimi a kan zukãtanku, wane abin bauttãwa ne, wanin Allah, zai jħ muku da shi?" Ka dũba yadda Muke sarrafa ãyõyi, sa´an nan kuma sũ, sunã finjirħwa. [6.47] Ka ce: "Shin, kun gan ku, idan azãbar Allah ta jħ muku, kwatsam, kõ kuwa bayyane, shin, anã halakarwa, fãce dai mutãne azzãlumai?" [6.48] Kuma bã Mu aikãwa da manzãnni fãce mãsu bayar da bushãra, kuma mãsu gargaɗi. To, wanda ya yi ĩmãni kuma ya gyãra aiki, to, babu tsõro a kansu, kuma ba su yin baƙin ciki. [6.49] Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu, azãba tanã shãfar su sabõda abin da suka kasance sunã yi na fãsiƙanci. [6.50] Ka ce: "Ba zan ce muku, a wurina akwai taskõkin Allah ba. Kuma ba ni sanin gaibi, kuma ba ni gaya muku cħwa ni malã´ika ne. Ba ni bi, fãce abin da ake yiwo wahayi zuwa gare ni." Ka ce: "Shin, makãho da mai gani sunã daidaita? Shin fa, ba ku yin tunãni?" [6.51] Kuma ka yi gargaɗi da shi ga waɗanda suke jin tsõron a tãra su zuwa ga Ubangijinsu, ba su da wani masõyi baicinSa, kuma babu mai cħto, tsammãninsu, sunã yin taƙawa. [6.52] Kuma kada ka kõri waɗanda(1) suke kiran Ubangijinsu sãfe da maraice, sunã nufin yardarSa, babu wani abu daga hisãbinsu a kanka, kuma babu wani abu daga hisãbinka a kansu, har ka kõre su ka kasance daga azzãlumai. [6.53] Kuma kamar wannan ne, Muka fitini sãshensu da sãshe, dõmin su ce: "Shin waɗannan ne Allah Ya yi falala a kansu daga tsakãninmu?" Shin, Allah bai zama Mafi sani ba ga mãsu gõdiya? [6.54] Kuma idan waɗanda suke yin ĩmãni da ãyõyinMu suka jħ maka, sai ka ce: "Aminci ya tabbata a gareku; Ubangjinku Ya wajabta rahama ga kanSa, cħwa lalle ne wanda ya aikata aibi da jãhilci daga cikinku, sa´an nan kuma ya tũba daga bãyansa, kuma ya gyãra, to, lalle Shi, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai." [6.55] Kuma kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki-daki, kuma dõmin hanyar mãsu laifi ta bayyana. [6.56] Ka ce: "Lalle ne ni, an hana ni in bauta wa waɗanda kuke kira daga baicin Allah." Ka ce: "Ba ni bin son zũciyõyinku, (dõmin in nã yi haka) lalle ne, nã ɓace. A sa´an nan, kuma ban zama daga shiryayyu ba." [6.57] Ka ce: "Lalle ne inã kan hujja daga Ubangjina, kuma kun ƙaryata (ni) game da Shi; abin da kuke nħman gaugãwarsa, bã ya wurina, hukunci kuwa bai zama ba fãce, ga Allah, Yanã bãyar da lãbãrin gaskiya, kuma shĩ ne mafi alhħrin mãsu rarrabħwa." [6.58] Ka ce: "Lalle ne, dã a wurina akwai abin da kuke nħman gaugãwa da shi, haƙĩƙa dã an hukunta al´amarin, a tsakãnina da tsakãninku, kuma Allah Shĩ ne Mafi sani ga azzũlumai." [6.59] Kuma a wurinSa mabũdan(1) gaibi suke, babu wanda yake sanin su fãce Shi, kuma Yanã sanin abin da ke a cikin tudu da ruwa, kuma wani ganye ba ya fãɗuwa, fãce Yã san shi, kuma bãbu wata ƙwãya a cikin duffan ƙasã, kuma babu ɗanye, kuma babu ƙħƙasasshe, fãce yanã a cikin wani Littãfi mai bayyanãwa. [6.60] Kuma Shĩ ne wanda Yake karɓar(1) rãyukanku da dare, kuma Yanã sanin abin da kuka yãga da rãna, sa´an nan Yanã tãyar da ku a cikinsa, dõmin a hukunta ajali ambatacce sa´an nan kuma zuwa gare shi makõmarku take, sa´an nan kuma Ya ba ku lãbari da abin da kuka kasance kunã aikatãwa. [6.61] Kuma Shĩ ne Mai rinjãya bisa ga bãyinSa, kuma Yanã aikan mãsu tsaro a kanku, har idan mutuwa ta jħ wa ɗayanku, sai manzanninMu su karɓi ransa alhãli su ba su yin sakaci. [6.62] Sa´an nan kuma a mayar da su zuwa ga Allah Ubangjinsu na gaskiya. To! A gare shi hukunci yake, kuma Shi ne Mafi gaugãwar mãsu bincike. [6.63] Ka ce: "Wane ne Yake tsĩrar da ku daga duhũhuwan tudu da ruwa, kunã kiran Sa bisa ga ƙanƙan da kai kuma a ɓõye: ´Lalle ne idan Ka tsĩrar da mu daga wannan (masĩfa), haƙĩƙa, muna kasancħwa daga mãsu gõdiya?´" [6.64] Ka ce: "Allah ne Yake tsĩrar da ku daga gare ta, kuma daga dukan baƙin ciki sa´an nan kuma ku, kunã yin shirki!" [6.65] Ka ce: "Shĩ ne Mai ĩko a kan Ya aika da wata azãba a kanku daga bisanku, kõ kuwa daga ƙarƙashin ƙafãfunku, kõ kuwa Ya gauraya ku ƙungiyõyi, kuma Ya ɗanɗanã wa sãshenku masĩfar sãshe." "Ka dũba yadda Muke sarrafa ãyõyi, tsammãninsu sunã fahimta!" [6.66] Kuma mutãnenka sun ƙaryata (ka) game da Shi, alhãli kuwa Shi ne gaskiya. Ka ce: "Nĩ ban zama wakĩli a kanku ba." [6.67] "Akwai matabbata ga dukan lãbãri, kuma zã ku sani." [6.68] Kuma idan kã ga waɗanda suke kũtsawa a cikin ãyõyinMu, to, ka bijire daga gare su, sai sun kũtsa a cikin wani lãbãri waninsa. Kuma imma dai shaiɗan lalle ya mantar da kai, to, kada ka zauna a bayan tunãwa tãre da mutãne azzãlumai. [6.69] Kuma babu wani abu daga hisãbinsu (mãsu kutsãwa a cikin ayõyin Allah (a kan mãsu taƙawa amma akwai tunãtarwa (a kansu), tsãmmãninsu (mãsu kutsawar) zã su yi taƙawa. [6.70] Kuma ka bar waɗanda suka riƙi addĩninsu abin wãsa(1) da wargi alhãli rãyuwar dũniya tã rũɗe su, kuma ka tunãtar game da shi (Alƙur´ãni): Kada a jħfa rai a cikin halaka sabõda abin da ya tsirfanta; ba shi da wani majiɓinci baicin Allah, kuma babu wani mai cħto; kuma, kõ ya daidaita dukan fansa, ba zã a karɓa ba daga gare shi. Waɗancan ne aka yanke wa tsammãni sabõda abin da suka tsirfanta; sunã da wani abin shã daga ruwan zãfi, da wata azãba mai raɗaɗi, sabõda abin da suka kasance sunã yi na kãfirci. [6.71] Ka ce: "Shin, zã mu yi kiran abin da bã ya amfãninmu, baicin Allah, kuma bã ya cũtar damu, kuma a mayar da mu a kan dugãduganmu, a bayan Allah Yã shiryar da mu kamar wanda shaiɗãnu suka kãyar da shi a cikin ƙasa, yanã mai ɗĩmuwa, yanã da abõkai sunã kiran sa zuwa ga shiriya, ´Ka zo mana´"(2) Kace: "Lalle ne, shiriyar Allah ita ce shiriya. Kuma an umurce mu, mu sallama wa Ubangijin tãlikai." [6.72] "Kuma (an ce mana): Ku tsai da salla kuma ku bĩ shi (Allah) da taƙawa kuma Shi ne wanda Yake zuwa gare Shi ake tãra ku." [6.73] Kuma Shĩ ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa da mulkinSa, kuma a Rãnar da Yake cħwa: "Ka kasance," sai abu ya yi ta kasancħwa. MaganarSa ce gaskiya, kuma gare Shi mulki yake a Rãnar da ake bũsa a cikin ƙaho. Masanin fake da bayyane ne, Kuma Shi ne Mai hikima Masani. [6.74] Kuma a lõkacin da Ibrãhĩma ya ce wa ubansa Ãzara: "Shin, kanã riƙon gumãka abũbuwan bautãwa? Lalle nĩ, inã ganin ka kai da mut?nenka, a cikin ɓata bayyananniya." [6.75] Kuma kamar wancan ne, Muke nũna wa Ibrãhĩma mulkin sammai da ƙasa, kuma dõmin ya kasance daga mãsu yaƙĩni. [6.76] To, a lõkacin da dare ya rufe a kansa, ya ga wani taurãro, ya ce: "Wannan ne, ubangijina?" Sa´an nan a lõkacin da ya faɗi, ya ce: "Ba ni son mãsu fãɗuwa." [6.77] Sa´an nan a lõkacin da ya ga watã yanã mai bayyana, ya ce: "Wannan ne Ubangijina?" Sa´an nan a lõkacin da ya fãɗi, ya ce: "Lalle ne idan Ubangijina bai shiryar da ni ba, haƙĩƙa, inã kasancħwa daga mutãne ɓatattu." [6.78] Sa´an nan a lõkacin da ya ga rãnã tanã bayyana, ya ce: "Wannan shĩ ne Ubangijina, wannan ne mafi girma?" Sa´an nan a lõkacin da ta fãɗi, ya ce: "Ya mutãnena! Lalle ne ni barrantacce nake daga abin da kuke yi na shirki." [6.79] "Lalle ne nĩ, na fuskantar da fuskata ga wanda, Ya ƙãga halittar sammai da ƙasa, inã mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bã ni cikin mãsu shirki." [6.80] Kuma mutãnensa suka yi musu da shi. Ya ce: "Shin kunã musu da ni a cikin sha´anin Allah, alhãli kuwa Yã shiryai da ni? Kuma bã ni tsõron abin da kuke yin shirki da shi, fãce idan Ubangijina Yã so wani abu. Ubangijina Ya yalwaci dukkan kõme da ilmi. Shin, ba zã ku yi tunãni ba?" [6.81] "Kuma yãyã nake jin tsõron abin da kuka yi shirki da shi, kuma ba ku tsõron cħwa lalle ne kũ, kun yi shirki da Allah, abin da (Allah) bai saukar da wata hujja ba game da shi? To, wane ɓangare daga sãshen biyu ne mafi cancanta da aminci, idan kun kasance kunã sani?" [6.82] "Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma ba su gauraya ĩmãninsu da zãlunci ba, waɗannan sunã da aminci, kuma sũ ne shiryayyu." [6.83] Kuma waccan ita ce hujjarMu, Mun bayãr da ita ga Ibrãhĩma a kan mutãnensa. Munã ɗaukaka wanda Muka so da darajõji. Lalle ne Ubangijinka Mai hikima ne, Masani. [6.84] Kuma Muka bã shi Is´hãƙa da Yãƙubu, dukansu Mun shiryar, kuma Nũhu Mun shiryar da shi a gabãni, kuma daga zuriyarsa akwai Dãwũda da Sulaimãnu da Ayyũba, da Yũsufu da Mũsã da Hãrũna, kuma kamar wancan ne Muke sãka wa mãsu kyautatãwa. [6.85] Da Zakariyya da Yahaya da Isa da Ilyasu dukansu daga sãlihai suke. [6.86] Da Ismã´la da Ilyasa, a da Yũnusa da Luɗu, kuma dukansu Mun fĩfĩtã su a kan tãlikai. [6.87] Kuma daga ubanninsu, da zũriyarsu, da ´yan´uwansu, kuma Muka zãɓe su, kuma Muka shiryar da su zuwa ga hanya madaidaiciya. [6.88] Wancan ne shiryarwar Allah, Yanã shiryar da wanda Yake so daga bayinSa. Kuma dã sun yi shirki dã haƙĩƙa abin da suka kasance sunã ,aikatãwa yã lãlãce. [6.89] Waɗancan ne waɗanda Muka bai wa Littãfi da hukunci da Annabci. To idan waɗannan (mutãne ) sun kãfirta da ita, to, haƙĩƙa, Mun wakkala wasu mutãne gare ta, ba su zama game da ita kãfirai ba. [6.90] Waɗancan ne Allah Ya shiryar, sabõda haka ka yi kõyi da shiryarsu. Ka ce: "Ba ni tambayar ku wata ijãra. Shĩ (Alƙur´ãni) bai zama ba fãce tunãtarwa ga tãlikai." [6.91] Kuma ba su ƙaddara Allah a kan hakkin ƙaddara shi ba, a lõkacin da suka ce: "Allah bai saukar da kõme ba ga wani mutum." Ka ce: "Wãne ne ya saukar da Littãfi wanda Mũsã ya zo da shi, yanã haske da shiriya ga mutãne, kunã sanya shi takardu, kũna bayyana su, kuma kunã ɓõye mai yawa, kuma an sanar da ku abin da ba ku sani ba, ku da ubanninku?" Ka ce: "Allah,"(1) sa´an nan ka bar su a cikin sharhõliyarsu sunã wãsã. [6.92] Kuma wannan Littãfi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, mai gaskata wanda yake a gabansa ne, kuma dõmin ka yi gargaɗi ga Uwar Alƙaryu (Makka) da wanda yake gefenta. Kuma waɗanda suke yin ĩmãni da Lãhira sunã ĩmãni da shi (Alƙur´ãni), kuma sũ, a kan sallarsu, sunã tsarħwa. [6.93] Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ce: "An yi wahayi zuwa gare ni," alhãli kuwa ba a yi wahayin kõme ba zuwa gare shi, da wanda ya ce: "zan saukar da misãlin abin da Allah Ya saukar?" Kuma dã kã gani, a lõkacin da azzãlumai suke cikin mãyen mutuwa, kuma malã´iku sunã mãsu shimfiɗa hannuwansu, (sunã ce musu) "Ku fitar da kanku; a yau anã sãka muku da azãbar wulãƙanci sabõda abin da kuka kasance kunã faɗa, wanin gaskiya, ga Allah kuma kun kasance daga ãyõyinSa kunã yin girman kai." [6.94] Kuma lalle ne haƙĩƙa, kun zo Mana ɗai ɗai, kamar yadda Muka halittã ku a farkon lõkaci. Kuma kun bar abin da Muka mallaka muku a bayan bayayyakinku, kuma ba Mu gani a tãre da kũ ba, macħtanku waɗanda kuka riya cħwa lalle ne sũ, a cikinku mãsu tãrayya ne. Lalle ne, h?ƙĩƙa, k?me yã yanyanke a tsakãninku, kuma abin da kuka kasance kunã riyãwa ya ɓace daga gare ku. [6.95] Lalle ne, Allah ne Mai ts?gewar ƙw?yar hatsi da kwalfar gurtsu. Yan? fitar da mai rai daga mamaci, kuma (Shi) Mai fitar da mamaci ne daga mai rai.(1) Wannan ne Allah. To, yãya ake karkatar da ku? [6.96] Mai tsãgħwar sãfiya, kuma Ya sanya dare mai natsuwa, kuma da rãna da watã a bisa liss?fi. Wannan ne ƙaddarãwar Mabuwãyi Masani. [6.97] Kuma Shi ne Ya sanya muku taurãri dõmin ku shiryu da su a cikin duffan tudu da ruwa. Lalle ne Mun bayyana ãyõyi daki-daki, ga mutãne waɗanda suke sani. [6.98] Kuma Shi ne Ya ƙãga halittarku daga rai guda, sa´an nan da mai tabbata da wanda ake ajħwa. Lalle ne Mun bayyanã ãyõyi daki-daki, ga mutãne waɗanda suke fahimta. [6.99] Kuma Shi ne Ya saukar da ruwa daga sama, Muka fitar da tsiron dukkan kõme game dã shi, sa´an nan Muka fitar da kõre daga gare shi, Muna fitar da kwãya ɗamfararriya daga gare shi (kõren),(2) kuma daga dabĩno daga hirtsinta akwai dumbuje-dumbuje makusanta, kuma (Muka fitar) da gõnaki na inabõbi da zãitũni da rummãni, mãsu kamã da jũna da wasun mãsu kama da jũna. Ku dũba zuwa ´ya´yan itãcensa, idan ya yi ´ya´yan, da nunarsa. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyõyi ga waɗanda suke yin ĩmãni. [6.100] Kuma suka sanya wa Allah abõkan tãrayya, aljannu, alhãli kuwa (Shi) Ya halitta su. Kuma sun ƙirƙira masa ɗiya da ´yã´ya, bã da ilmi ba. TsarkinSa yã tabbata! Kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke sifantãwa. [6.101] Mafarin(3) halittar sammai da ƙasa. Yãya ɗã zai zama a gare Shi alhãli kuwa mãta ba ta kasance ba, a gare Shi, kuma Ya halitta Dukkan k?me, kuma Shĩ, game da dukan kõme, Masani ne? [6.102] Wancan ne Allah Ubangijinku. Bãbu wani abin bautãwa fãce Shĩ, Mahaliccin dukan kõme. Sabõda haka ku bauta Masa kuma Shi ne wakĩli a kan dukan, kõme. [6.103] Gannai bã su iya riskuwarSa, kuma Shĩ Yanã riskuwar gannai, kuma Shĩ ne Mai tausas?wa, Masani. [6.104] Lalle ne abũbuwan lũra sun je muku daga Ubangijinku, to, wanda ya kula, to, dõmin kansa, kuma wanda ya makanta, to, laifi yanã a kansa, kuma nĩ, a kanku, bã mai tsaro ba ne. [6.105] Kamar wannan ne Muke sarrafa ãyõyi, kuma dõmin su ce: "Kã karanta!" Kuma dõmin Mu bayyana shi ga mutãne waɗanda sunã sani. [6.106] Ka bi abin da aka yi wahayi zuwa gare ka daga Ubangijinka; babu wani abin bautãwa fãce Shi, kuma ka bijire daga mãsu shirki. [6.107] Kuma dã Allah Yã so, dã ba su yi shirki ba, kuma ba Mu sanya ka mai tsaro a kansu ba, kuma ba kai ne wakĩli a kansu ba. [6.108] Kuma kada ku zãgi waɗanda suke kira, baicin Allah, har su zãgi Allah bisa zãlunci, ba, da ilmi ba. Kamar wannan ne Muka ƙawãta ga kõwace al´umma aikinsu, sa´an nan zuwa ga Ubangijinsu makõmarsu take, sa´an nan Ya ba su lãbari da abin da suka kasance sunã aikatãwa. [6.109] Kuma suka yi rantsuwa da Allah iyakar rantsuwõyinsu (cħwa) lalle ne idan wata ãyã ta j musu, haƙĩƙa, sunã yin ĩmãni da ita. Ka ce: "Abin sani kawai, ãyõyi a wurin Allah suke. Kuma mħne ne zai sanya ku ku sansance cħwa, lalle ne su, idan ãyõyin sun je, ba zã su yi ĩmãni ba?" [6.110] Kuma Munã jujjũya zukãtansu da ganansu, kamar yadda ba su yi ĩmãni da shi ba a farkon lõkaci kuma Munã barin su a cikin kũtsãwarsu, sunã ɗĩmuwa. [6.111] Kuma dã a ce, lalle Mũ Mun saukar da Malã´iku zuwa gare su, kuma matattu suka yi musu magana, kuma Muka tãra dukkan kõme a kansu, gungu-gungu, ba su kasance sunã iya yin ĩmãni ba, sai fa idan Allah Yã so, Kuma amma mafi yawansu sunã jãhiltar haka. [6.112] Kuma kamar wancan ne Muka sanya wa kõwane Annabi maƙiyi; shaiɗãnun mutãne da aljannu, sãshensu yanã yin ishãra(1) zuwa sãshe da ƙawãtaccen zance bisa ga rũɗi. Kuma dã Ubangijinka Yã so, dã ba su aikatã shi ba, don haka ka bar su da abin da, suke ƙirƙirãwa. [6.113] Kuma dõmin zukãtan waɗanda ba su yi ĩmãni da Lãhira ba su karkata saurãrħ zuwa gareshi, kuma dõmin su yarda da shi, kuma dõmin su kamfaci abin da suke mãsu kamfata. [6.114] Shin fa, wanin Allah nake nħma ya zama mai hukunci, alhãli kuwa Shĩ ne wanda Ya saukar muku da Littãfi abin rabħwa daki-daki? Kuma waɗanda Muka bai wa Littãfi sunã sanin cħwa lalleshi (Alƙur´ãni) abin saukarwa ne daga Ubangijinka, da gaskiya? Sabõda haka kada ku kasance daga mãsu shakka. [6.115] Kuma kalmar Ubangijinka tã cika, tanã gaskiya(2) da ãdalci. Babu mai musanyãwa ga kalmõminSa, kuma Shi ne Maiji, Masani. [6.116] Kuma idan ka bi mafiya yawan waɗanda suke a cikin ƙasa da ɗã´a sunã ɓatar da kai daga hanyar Allah. Ba su bin kõme sai fãce ƙaddari-faɗi(3) suke yi. [6.117] Lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Mafi sani ga wanda yake ɓacħwa daga hanyarsa kuma Shi ne mafi sani ga masu shiryuwa. [6.118] Sabõda haka ku ci daga abin da aka ambaci sũnan Allah(4) kansa, idan kun kasance mãsu ĩmãni da ãyõyinSa. [6.119] Kuma mħne ne ya sãme ku, bã zã ku ci ba daga abin da aka ambaci sũnan Allah a kansa,alhãli kuwa, haƙĩƙa, Ya rarrabe, muku daki-daki, abin da Ya haramta a kanku, fãce fa abin da aka bukãtar da ku bisa lalũra zuwa gare shi? Kuma lalle ne mãsu yawa sunã ɓatarwa, da son zũciyõyinsu, ba da wani ilmi ba. Lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Mafi sani ga mãsu ta´addi. [6.120] Kuma ku bar bayyanannen zunubi da ɓõyayyensa. Lalle ne waɗanda suke tsiwurwurin zunubi za a sãka musu da abin da suka kasance sunã kamfata. [6.121] Kada ku ci daga abin da ba a ambaci sũnan Allah ba a kansa(1) . Kuma lalle ne shĩ fãsiƙanci ne. Kuma lalle ne, shaiɗãnu, haƙĩƙa, suna yin ishãra zuwa ga masõyansu, dõmin su yi jãyayya da ku. Kuma idan kuka yi musu ɗã´a, lalle ne kũ, haƙĩƙa, mãsu shirki ne. [6.122] Shin, kuma wanda ya kasance matacce sa´an nan Muka rãyar da shi, kuma Muka sanya wani haske dõminsa, yanã tafiya da shi, yanã zama kamar wanda misãlinsa yanã cikin duffai, shĩ kuma ba mai fita ba daga gare su? Kamar wancan ne aka ƙawãta wa kãfirai abin da suka kasance sunã aikatãwa. [6.123] Kuma kamar wancan ne Mun sanya a cikin kõwace alƙarya, shugabanni sũ ne mãsu laifinta dõmin su yi mãkirci a cikinta, alhãli kuwa ba su yin makirci fãce ga rayukansu, kuma ba su sansancħwa. [6.124] Kuma idan wata ãyã ta je musu sai su ce: "Ba zã mu yi ĩmãni ba, sai an kãwo mana kamar abin da aka kãwo wa manzannin Allah." Allah Mafi sanin inda Yake sanya manzancinSa.(2) Wani wulaƙanci(3) a wurin Allah da wata azãba mai tsanani zã su sãmi waɗanda suka yi laifi, sabõda abin da suka kasance sunã yi na mãkirci. [6.125] Dõmin haka wanda Allah Ya yi nufin ya shiryar da shi sai ya bũɗa ƙirjinsa dõmĩn Musulunci, kuma wanda Ya yi nufin Ya ɓatar da shi, sai Ya sanya ƙirjinsa mai ƙunci matsattse, kamar dai yanã tãkãwa(1) ne a ckin sama. Kamar wannan ne Allah Yake sanyãwar ƙazanta a kan waɗanda bã su yin ĩmãni. [6.126] Wannan ita ce hanya ta Ubangijinka madaidaiciya. Lalle ne Mun bayyana ãyõyi daki-daki ga mutãne mãsu karɓar tunãtarwa. [6.127] Sunã da gidan aminci a wurin Ubangjinsu, kuma Shĩ ne Majiɓincinsu, sabõda abin da suka kasance sunã aikatãwa. [6.128] Kuma rãnar da yake tãra su gaba ɗaya (Yanã cħwa): "Yã jama´ar aljannu! Lalle ne kun yawaita kanku daga mutãne." Kuma majiɓantansu daga mutãne suka ce: "Yã Ubangjinmu! Sãshenmu(2) ya ji dãɗi da sãshe, kuma mun kai ga ajalinmu wanda Ka yanka mana!" (Allah) Ya ce: "Wuta ce mazaunarku, kunã madawwama a cikinta, sai abin da Allah Ya so. Lalle ne Ubangijinka Mai hikima ne, Masani." [6.129] Kuma kamar wancan ne Muke jiɓintar da sãshen azzãlumai ga sãshe, sabõda abin da suka kasance sunã tãrãwa. [6.130] Yã jama´ar aljannu da mutãne! Shin, manzanni daga gare ku ba su jħ muku ba sunã lãbarta ãyõyiNa a kanku, kuma sunã yi muku gargaɗin haɗuwa da wannan yini nãku? Suka ce: "Mun yi shaida a kan kãwunanmu." Kuma rãyuwar dũniya tã rũɗħ su. Kuma suka yi shaida a kan kãwunansu cħwa lalle ne sũ, sun kasance kãfirai. [6.131] Wancan kuwa sabõda Ubangijinka bai kasance Mai halaka alƙaryõyi sabõda wani zãlunci ba ne, alhãli kuwa mutãnensu sunã jãhilai.(3) [6.132] Kuma ga kõwanne,(1) akwai darajõji daga abin da suka aikata. Kuma Ubangijinka bai zama mai shagala ba daga abin da suke aikatãwa. [6.133] Kuma Ubangijinika Wadãtacce(2) ne Ma´abũcin rahama. Idan Yã so zai tafi da ku, kuma Ya musanya daga bãyanku, abin da Yake so, kamar yadda Ya ƙãga halittarku daga zũriyar wasu mutãne na dabam. [6.134] Lalle ne abin da ake yi muku wa´adi lalle mai zuwa ne kuma ba ku zama mãsu buwãya ba, [6.135] Ka ce: "Yã ku mutãnena! Ku yi aiki a kan halinku, lalle ne nĩ mai aiki ne, sa´an nan da sannu zã ku san wanda ãƙibar gida zã ta kasance a gare shi. Lalle ne shi, azzãlumai bã zã su ci nasarã ba." [6.136] Kuma sun sanya wani rabõ ga Allah daga abin da Ya halitta daga shũka da dabbõbi, sai suka ce: "Wannan(3) na Allah ne," da riyãwarsu "Kuma wannan na abũbuwan shirkinmu ne." Sa´an nan Abin da ya kasance na abũbuwan shirkinsu, to, bã ya sãduwa zuwa Allah, kuma abin da ya kasance na Allah, to, shĩ yanã sãduwa zuwa ga abũbuwan shirkinsu. Tir da hukuncinsu! [6.137] Kuma kamar wancan ne abũbuwan shirkinsu suka ƙãwata wa mãsu yawa, daga mãsu shirkin; kashewar(4) ´ya´yansu, dõmin su halaka su kuma dõmin su rikitar da addininsu a gare su, kuma dã Allah Yã so dã ba su aikatã shi ba. Sabõda haka ka bar su da abin da suke ƙirƙirãwa. [6.138] Kuma suka ce: "Waɗannan dabbõbi da shũka hanannu ne; bãbu mai ɗanɗanar su fãce wanda muke so," ga riyãwarsu. Da wasu dabbõbi an hana bãyayyakinsu, da wasu dabbõbi bã su ambatar sũnan Allah a kansu, bisa ƙirƙiren ƙarya gare Shi. Zai sãka musu da abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa. [6.139] Kuma suka ce: "Abin da yake a cikin cikkunan waɗannan dabbõbi kħɓantacce ne ga mazanmu, kuma hananne ne a kan mãtan aurenmu. Kuma idan ya kasance mũshe, to, a cikinsa sũ abõkan tãrayya ne, zai sãka musu sifantãwarsu. Lalle ne Shĩ, Mai hikima ne, Masani." [6.140] Lalle ne waɗanda suka kashe ɗiyansu sabõda wauta, ba da ilmi ba, sun yi hasãra! Kuma suka haramta abin da Allah Ya azurta su, bisa ƙirƙira ƙarya ga Allah. Lalle ne sun ɓace, kuma ba su kasance mãsu shiryuwa ba. [6.141] Kuma Shĩ ne Wanda Ya ƙãga halittar gõnaki mãsu rumfuna da wasun mãsu rumfuna da dabĩnai da shũka, mai sãɓãwa ga ´yã´yansa na ci, da zaituni da rummãni mai kama da jũna da wanin mai kama da jũna. Ku ci daga ´ya´yan itãcensa, idan ya yi ´yã´yan, kuma ku bãyar da hakkinSa a rãnar girbinsa, kuma kada ku yi ɓarna. Lalle ne Shĩ, ba Ya son mabarnata. [6.142] Kuma daga dabbõbi (Ya ƙãga halittar) mai ɗaukar kãya da ƙanãna; Ku ci daga abin da Allah Ya azurta ku, kuma kada ku bi zambiyõyin shaiɗan: Lalle ne shi, a gare ku, maƙiyi ne bayyananne. [6.143] Nau´õ´i takwas daga tumãkai biyu, kuma daga awãkai biyu; ka ce: Shin mazan biyu ne Ya haramta ko mãtan biyu, ko abin da mahaifar mãtan biyu suka tattara a kansa? Ku bã ni lãbãri da ilmi, idan kun kasance mãsu gaskiya. [6.144] Kuma daga rãƙuma akwai nau´i biyu, kuma daga shãnu biyu; ka ce: Shin, mazan biyu ne Ya hana ko mãtan biyu Ya hana, kõ abin da mahaifar mãtan biyu suka tattara a kansa? Kõ kun kasance halarce ne a lõkacin da Allah Ya yi muku wasiyya da wannan? To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, dõmin ya ɓatar da mutãne bã da wani ilmi ba? Lalle ne, Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai. [6.145] Ka ce: "Bã ni sãmu,(1) a cikin abin da aka yõ wahayi zuwa gare Ni, abin haramtãwa a kan wani mai ci wanda yake cin sa fãce idan ya kasance mũshe kõ kuwa jini abin zubarwa kõ kuwa nãman alade, to lalle ne shi ƙazanta ne, kõ kuwa fãsiƙanci wanda aka kurũrũta, dõmin wanin Allah da shi." Sa´an nan wanda larũra ta kãmã shi, bã mai fita jama´a ba, kuma bã mai ta´addi ba, to, lalle Ubangijinka Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [6.146] Kuma a kan waɗanda suka tũba (Yahũdu) Mun haramta(2) dukan mai akaifa, kuma daga shãnu da bisãshe Mun haramta musu kitsattsansu fãce abin da bãyukansu suka ɗauka, kõ kuwa kãyan ciki, kõ kuwa abin da ya garwaya da ƙashĩ. Wannan ne Muka sãka musu sabõda zãluncinsu, kuma Mu, haƙĩƙa, Mãsu gaskiya ne. [6.147] To, idan sun ƙaryatã ka, sai ka ce: "Ubangijinku Ma´abũcin rahama ne Mai yalwa; kuma bã a mayar da azãbarSa daga mutãne mãsu laifi." [6.148] Waɗanda suka yi shirki(1) zã su ce: "Dã Allah Yã so dã ba mu yi shirki ba, kuma dã ubanninmu ba su yi ba, kuma dã ba mu haramta wani abu ba." Kamar wannan ne mutãnen da suke a gabãninsu suka ƙaryata, har suka ɗanɗani azãbarMu. Ka ce: "Shin, kunã da wani ilmi a wurinku dõmin ku fito mana da shi? Bã ku bin kõme fãce zato kuma ba ku zama ba fãce ƙiri-faɗi kawai kuke yi." [6.149] Ka ce: "To Allah ne da hujja isasshiya, sabõda haka: Dã Yã so, dã Yã shiryar da ku gabã ɗaya." [6.150] Ka ce: "Ku kãwo shaidunku, waɗanda suke bãyar da shaidar cħwa Allah ne Ya haramta wannan." To idan sun kãwo shaida kada ka yi shaida tãre da su. Kuma kada ka bi son zũciyõyin waɗanda suka ƙaryata, game da ãyõyinMu, da waɗanda bã su yin ĩmãni da Lãhira, alhãli kuwa sũ daga Ubangijinsu suna karkacħwa. [6.151] Ka ce: "Ku zo, in karanta abin da Ubangijinku Ya haramta." wãjibi ne a kanku kada ku yi shirkin kõme da Shi, kuma ga mahaifa biyu (ku kyautata) kyautatãwa, kuma kada ku kashe ɗiyanku sabõda talauci, Mũ ne Muke azurta ku, kũ da su, kuma kada ku kusanci abũbuwan alf?sha, abin da ya bayyana daga gare ta da abin da ya ɓõyu, kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta, fãce da hakki. Wannan ne (Allah) Ya yi muku wasiyya da Shi: Tsammãninku, kunã hankalta. [6.152] Kada ku kusanci dũkiyar marãya fãce da wadda take ita ce mafi kyau, har ya kai ga ƙarfinsa. Kuma ku cika mũdu da sikħli da ãdalci, bã Mu kallafã wa rai fãce iyãwarsa. Kuma idan kun faɗi magana, to, ku yi ãdalci, kuma ko dã yã kasance ma´abũcin zumunta ne. Kuma da alkawarin Allah ku cika. Wannan ne Ya yi muku wasiyya da shi: tsamm?ninku, kunã tunãwa. [6.153] Kuma lalle wannan ne tafarkĩNa, yana madaidaici: Sai ku bĩ shi, kuma kada ku bi wasu hanyõyi, su rarrabu da ku daga barin hanyãTa. Wannan ne Allah Ya yi muku wasiyya da shi tsammãninku, kunã yin taƙawa. [6.154] Sa´an nan kuma Mun bai wa Mũsã Littãfi, yanã cikakke bisa ga wanda ya kyautata (hukuncin Allah) da rarrabħwa, daki-daki, ga kõwane abu, da shiriya da rahama, tsammãninsu,(1) sunã yin ĩmãni da haɗuwa da Ubangijinsu. [6.155] Kuma wannan Littãfi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, sai ku bĩ shi kuma ku yi taƙawa, tsammãninku, anã jin ƙanku. [6.156] (Dõmin) kada ku ce: "Abin sani kawai, an saukar da littãfi a kan ƙungiya(2) biyu daga gabãninmu, kuma lalle ne mũ, mun kasance, daga karatunsu, haƙĩƙa, gãfilai." [6.157] Kõ kuwa ku ce: "Dã dai lalle mũ an saukar da Littãfi a kanmu, haƙĩƙa, dã mun kasance mafiya,shiryuwa daga gare su." To, lalle ne wata hujja bayyananniya, daga Ubangijinku, tã zo muku, da shiriya da rahama. To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙaryata game da ãyõyin Allah, kuma ya hinjire daga barinsu? Zã Mu sãka wa waɗanda suke hinjirħwa daga barin ãyõyinMu da mugunyar azãba, sabõda abin da suka kasance sunã yi na hinjirħwa. [6.158] Shin, sunã jiran (wani abu), fãce dai malã´iku(1) su je musu kõ kuwa Ubangijinka Ya je, kõ kuwa sãshen ãyõyin Ubangijinka ya je. A rãnar da sãshen ãyõyin Ubangijinka yake zuwa, ĩmãnin rai wanda bai kasance yã yi ĩmãnin ba a gabãni, kõ kuwa ya yi tsiwirwirin wani alhħri, bã ya amfãninsa. Ka ce: "Ku yi jira: Lalle ne mũ, mãsu jira ne." [6.159] Lalle ne waɗanda(2) suka rarraba addininsu, kuma suka kasance ƙungiyã-ƙungiyã, kai ba ka zama daga gare su ba, a cikin kõme: abin sani kawai al´amarinsu zuwa ga Allah yake. Sa´an nan Ya bã su lãbãri game da abin da suka kasance sunã aikatãwa. [6.160] Wanda ya zo da kyakkyãwan aiki guda, to, yanã da gõma ɗin misãlansa. Kuma wanda ya zo da mũgun aiki gũda, to, bã zã a sãka masa ba fãce da misãlinsa. Kuma sũ bã a zãluntar su. [6.161] Ka ce: "Lalle nĩ, Ubangijina Yã shiryar da ni zuwa ga tafarki madaidaici, addĩni, ƙĩmantãwa ( ga abũbuwa), mai aƙĩdar Ibrãhĩm, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba." [6.162] Ka ce: "Lalle ne sallãta, da baikõna, da rãyuwãta, da mutuwãta, na Allah ne Ubangijin tãlikai." [6.163] "Bãbu abõkin tãrayya a gare Shi. Kuma da wancan aka umurce ni, kuma ni ne farkon mãsu sallamãwa." [6.164] Ka ce: "Shin wanin Allah nake nħma ya zama Ubangiji, alhãli kuwa Shĩ ne Ubangijin dukan kõme? Kuma wani rai bã ya yin tsirfa fãce dõmin kansa, kuma mai ɗaukar nauyi, bã ya ɗaukar nauyin wani, sa´an nan kuma kõmawarku zuwa ga Ubangijinku take; Sa´an nan Yã bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance, a cikinsa, kunã sãɓã wa jũnã?" [6.165] "Kuma Shĩ ne wanda Ya sanya ku mãsu maye wa jũna ga ƙasa. Kuma Ya ɗaukaka sãshenku bisa ga sãshe da darajõji; dõmin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya bã ku." Lalle ne, Ubangijinka Mai gaggãwar uƙkũba ne, kuma lalle ne Shi, haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. @AL A'RAAF Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [7.1] A. L̃. M̃. Ṣ̃. [7.2] Littãfi ne aka saukar zuwa gare ka, kada wani ƙunci ya kasance a cikin ƙirjinka daga gare shi, dõmin ka yi gargaɗi da shi. Kuma tunãtarwa ne ga mũminai. [7.3] Ku bi abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku, kuma kada ku dinga bin wasu majiɓinta baicinSa. Kaɗan ƙwarai kuke tunãwa. [7.4] Kuma da yawa wata alƙarya Muka halaka ta, sai azãbarMu ta jħ mata da dare kõ kuwa sunã mãsu ƙailũla. [7.5] Sa´an nan bãbu abin da yake da´awarsu, a lõkacin da azãbarMu ta jħ musu, fãce suka ce: "Lalle ne mũ muka kasance mãsu zãlunci," [7.6] Sa´an nan lalle ne Munã tambayar waɗanda aka aika zuwa gare su, kuma lalle Munã tambayar Manzannin. [7.7] Sa´an nan haƙĩƙa Munã bã su lãbãri da ilmi kuma ba Mu kasance mãsu fakuwa ba. [7.8] Kuma awo a rãnar nan ne gaskiya. To, wanda sikħlansa suka yi nauyi, to, waɗannan sũ ne mãsu cin nasara. [7.9] Kuma wanda sikħlansa suka yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasarar rayukansu, sabõda abin da suka kasance, da ãyõyinMu, sunã yi na zãlunci. [7.10] Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun sarautar da ku, a cikin ƙasa, kuma Mun sanya muku abũbuwan rãyuwa, a cikinta; kaɗan ƙwarai kuke gõdħwa. [7.11] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun halittã ku sa´an nan kuma Mun sũrantã ku, sa´an nan kuma Mun ce wa malã´iku: "Ku yi sujada ga Ãdam." Sai suka yi sujada fãce Iblĩs, bai kasance daga mãsuyin sujadar ba.(1) [7.12] Ya ce: "Mħne ne ya hana ka, ba ka yi sujada ba, a l?kacin da Na umurce ka?" Ya ce: "Nĩ ne mafĩfĩci daga gare shi, Ka halitta ni daga wuta alhãli kuwa Kã halitta shi daga lãka." [7.13] Ya ce: "To, ka sauka daga gare ta; d?min b? ya kasancħwa a gare ka ga ka yi girman kai a cikinta. Sai ka fita. Lalle ne kanã daga mãsu ƙasƙanci." [7.14] Ya ce: "Ka yi mini jinkiri zuwa ga rãnar da ake tãyar(1) da su." [7.15] Ya ce: "Lalle ne, kanã daga waɗanda aka yi wa jinkiri."(2) [7.16] Ya ce: "To inã rantsuwa da halakarwar da Ka yi mini, lalle ne, inã zaune musu tafarkinKa madaidaici." [7.17] "Sa´an nan kuma haƙĩƙa, Inã je musu daga gaba gare su, kuma daga bãya gare su, kuma daga jihõhin damansu da jihõhin hagunsu; Kuma bã zã ka sãmi mafi yawansu mãsu gõdiya ba." [7.18] Ya ce: "Ka fita daga gare ta kanã abin zargi kõrarre. Lalle ne wanda ya bĩ ka daga gare su, haƙĩƙa, zã Ni cika jahannama daga gare ku, gabã ɗaya." [7.19] "Kuma ya Ãdam! Ka zauna kai da matarka a Aljanna sai ku ci daga inda kuka so; kuma kada ku kusanci Wannan itãciya, har ku kasance daga azzãlumai." [7.20] Sai Shaiɗan ya sanya musu waswãsi dõmin ya bayyana musu abin da aka rufe daga barinsu, daga al´aurarsu, kuma ya ce: "Ubangijinku bai hanã ku daga wannan itãciya ba fãce dõmin kada ku kasance malã´iku biyu ko kuwa ku kasance daga madawwama." [7.21] Kuma ya yi musu rantsuwa; Lalle ne nĩ, a gare ku, haƙĩƙa, daga mãsu nasĩha ne. [7.22] Sai ya saukar da su da rũɗi. Sa´an nan a lõkacin da suka ɗanɗani itãciyar, al´aurarsu ta bayyana gare su, kuma suka shiga sunã lĩƙawar ganye a kansu daga ganyen Aljanna. Kuma Ubangjinsu Ya kira su: "Shin, Ban hanã ku ba daga waccan itãciya, kuma Na ce muku lalle ne Shaiɗan, a gare ku, maƙiyi ne bayyananne?" , [7.23] Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Mun zãlunci kanmu. Kuma idan ba Ka gãfarta mana ba, kuma Ka yi mana rahama, haƙĩƙa, Munã kasancħwa daga mãsu hasãra." [7.24] Ya ce: "Ku sauka, s?shenku zuwa ga s?she yan? maƙiyi, kuma kun? da matabbata a cikin ƙasa, da ɗan jin d?ɗi zuwa ga wani l?kaci." [7.25] Ya ce: "A cikinta kuke rãyuwa, kuma a cikinta kuke mutuwa, kuma daga gare ta ake fitar da ku." [7.26] Yã ɗiyan Ãdam! Lalle ne Mun saukar da wata tufa(1) a kanku, tanã rufe muku al´aurarku, kuma da ƙawã. Kuma tufar taƙawa wancan ce mafi alhħri. Wancan daga ãyõyin Allah ne, tsammãninsu sunã tunãwa! [7.27] Yã ɗiyan Ãdam! Kada Shaiɗan, lalle, ya fitine ku, kamar yadda ya fitar da iyãyenku, biyu daga Aljanna, yanã fizge tufarsu daga gare su, dõmin ya nũna musu al´aurarsu. Lalle ne shĩ, yanã ganin ku, shi da rundunarsa, daga inda bã ku ganin su. Lalle ne Mũ, Mun sanya Shaiɗan majiɓinci ga waɗanda bã su yin ĩmãni. [7.28] Kuma idan suka aikata alfãsha(2) su ce: "Mun sãmi ubanninmu a kanta." Kuma Allah ne Ya umurce mu da ita."Ka ce: "Lalle ne, Allah bã Ya umurni da alfãsha. Shin kunã faɗar abin da bã ku da saninsa ga Allah?" [7.29] Ka ce: "Ubangjina Yã yi umurni da ãdalci; kuma ku tsayar da fuskõkinku a wurin kõwane masallãci, kuma ku rõƙħ Shi, kunã mãsu tsarkake addini gare Shi. Kamar yadda Ya fãra halittarku kuke kõmãwa." [7.30] Wata ƙungiya (Allah) Yã shiryar, kuma wata ƙungiya ɓata tã wajaba a kansu; lalle ne sũ, sun riƙi shaiɗanu majiɓinta, baicin Allah, kuma sunã zaton, lalle sũ, mãsu shiryuwa ne. [7.31] Yã ɗiyan Ãdam! Ku riƙi ƙawarku a wurin kõwane masallãci kuma ku ci, kuma ku sha; Kuma kada ku yi ɓarna. Lalle ne Shĩ (Allah), bã Ya son mãsu ɓarna. [7.32] Ka ce: "Wãne ne ya haramta ƙawar Allah, wadda Ya fitar sabõda bãyinSa, da mãsu dãɗi daga abinci?" Ka ce: "Sũ, dõmin waɗanda suka yi ĩmani suke a cikin rãyuwar dũniya, suna keɓantattu a Rãnar Kiyãma. "Kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki-daki, ga mutãnen da suke sani. [7.33] Ka ce: "Abin sani kawai, Ubangijina Yã hana abũbuwan alf?sha; abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya ɓõyu, da zunubi da rarraba jama´a, bã da wani hakki ba, kuma da ku yi shirki da Allah ga abin da bai saukar da wani dalĩli ba gare shi, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba, ga Allah." [7.34] Kuma ga kõwace al´umma akwai ajali. Sa´an nan idan ajalinsu ya je, bã zã a yi musu jinkiri ba, sa´a guda, kuma bã zã su gabãce shi ba. [7.35] Yã ɗiyan Ãdam! Ko dai wasu manzanni, daga cikinku, su jħ muku, sunã gaya muku ay?yiNa - to, wanda ya yi taƙawa, kuma ya gyara aikinsa, to, bãbu tsoro a kansu, kuma bã su yin baƙin ciki. [7.36] Kuma waɗanda suka ƙaryatã game da ãyõyinMu, kuma suka yi girman kai daga gare su, waɗannan sũ ne abõkan wuta, sũ, a cikinta madawwama ne. [7.37] To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ƙaryata game da ãyõyinSa? Waɗannan rabonsu daga Littãfi yanã sãmunsu, har a lõkacin da ManzanninMu suka je musu, sunã karɓar rãyukansu, su ce: "Ĩnã abin da kuka kasance kunã kira, baicin Allah?" Su ce: "Sun ɓace daga gare mu, "Kuma su yi shaida a kansu cħwa lalle sũ, sun kasance kãfirai." [7.38] Ya ce: "Ku shiga a cikin al´ummai waɗanda, haƙĩƙa, sun shige daga gabãninku, daga aljannu da mutãne, a cikin Wuta. A kõ da yaushe wata al´umma ta shiga sai ta la´ani ´yar´uwarta, har idan suka riski jũna, a cikinta, gabã ɗaya, ta ƙarshensu ta ce wa ta farkonsu: "Ya Ubangijinmu! Waɗannan ne suka ɓatar da mu, sai Ka kãwo musu azãba ninki daga wuta." Ya ce: "Ga kõwane(1) akwai ninki; kuma amma ba ku sani ba." [7.39] Kuma ta farkonsu ta ce wa ta ƙarshe: "To, bã ku da wata falala a kanmu, sai ku ɗanɗana azãba sabõda abin da kuka kasance kunã tsirfawa!" [7.40] Lalle ne waɗanda suka ƙaryatã game da ãyõyinMu, kuma suka yi girman kai daga barinsu, bã zã a bubbuɗe musu kõfõfin sama ba, kuma bã su shiga Aljanna sai raƙumi ya shiga kafar allũra, kuma kamar wannan ne Muke sãka wa mãsu laifi. [7.41] Sunã da wata shimfiɗa daga Jahannama kuma daga samansu akwai wasu murafai. Kuma kamar wancan ne Muke sãka wa azzãlumai. [7.42] Kuma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, bã Mu ƙallafa wa rai fãce iyãwarsa, Waɗannan ne abõkan Aljanna, sũ, a cikinta, madawwma ne. [7.43] Kuma Muka fitar da abin da yake a cikin ƙirãzansu, daga ƙiyayya, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, kuma suka ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah, wanda Ya shiryar da mu ga wannan. Kuma ba mu kasance munã iya shiryuwa ba, bã dõmin Allah Ya shiryar da mu ba. Lalle ne haƙĩƙa, Manzannin Ubangjinmu, sun jħ mana da gaskiya." Kuma aka kira su, cħwa: "Waccan Aljanna an gãdar da ku ita, sabõda abin da kuka kasance kunã aikatãwa." [7.44] Kuma ´yan Aljanna suka kirãyi ´yan Wuta suka ce: "Lalle ne mun sãmi abin da Ubangijinmu Ya yi mana wa´adi, gaskiya ne. To, shin, kun sãmi abin da Ubangijinku Ya yi muku wa´adi, gaskiya?" Suka ce: "Na´am." Sai mai sanarwa ya yi yħkuwa, cħwa: "La´anar Allah ta tabbata a kan azzãlumai." [7.45] "Waɗanda suke kangħwa daga hanyar Allah, kuma sunã nħman ta ta zama karkatacciya,. kuma sũ, game da Lãhira, kãfirai ne." [7.46] Kuma a tsakãninsu akwai wani shãmaki,(1) kuma a kan A´arãf akwai wasu maza sunã sanin kõwa da alãmarsu; Kuma suka kirãyi abõkan Aljanna cħwa: "Aminci ya tabbata a kanku: "Ba su shige ta ba, alhãli kuwa sũ, sunã tsammãni. [7.47] Kuma idan an jũyar da gannansu wajen abõkan wuta, su ce: "Yã Ubangijinmu! Kada Ka sanyã mu tãre da mutãne azzãlumai." [7.48] Kuma abõkan A´araf suka kirãyi wasu maza, sunã sanin su da alãmarsu, suka ce: "Tãrawar dũkiyarku da abin da kuka kasance kunã yi na girman kai, bai wadãtar ba daga barinku?" [7.49] "Shin, waɗannan ne waɗanda kuka yi rantsuwa, Allah bã zai sãme su da rahama ba? Ku shiga Aljanna, bãbu tsõro a kanku, kuma ba ku zama kunã baƙin ciki ba." [7.50] Kuma ´yan wuta suka kirãyi ´yan Aljanna cħwa: "Ku zubo a kanmu daga ruwa kõ kuwa daga abin da Allah Ya azurta ku." Su ce: "Lalle ne Allah Ya haramtã su a kan kãfirai." [7.51] "Waɗanda suka riƙi addininsu abin shagala da wãsa, kuma rãyuwar dũniya ta rũɗe su." To, a yau Munã mantãwa da su, kamar yadda suka manta da haɗuwa da yininsu wannan, da kuma abin da suka kasance da ãyoyinMu sunã musu. [7.52] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun jħ musu da Littãfi, Mun bayyana Shi, daki-daki, a kan ilmi, yanã shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suke yin ĩmani. [7.53] Shin, sunã jira, fãce fassararsa, a rãnar da fassararsa take zuwa, waɗanda suka manta da Shi daga gabãni, sunã cħwa: "Lalle ne, Manzannin Ubangijin mu sun jħ da gaskiya. To, shin, munã da wasu mãsu cħto, su yi cħto gare mu, kõ kuwa a mayar da mũ, har mu aikata wanin wanda muka kasance muna aikatãwa?" Lalle ne sun yi hasãrar rãyukansu, kuma abin da suka kasance sunã ƙĩrƙirawa yã ɓace musu. [7.54] Lalle ne Ubangijinku Allah ne, wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin kwãnaki shida, sa´an nan kuma Ya daidaita a kan Al´arshi, Yanã sanya dare ya rufa yini, yanã nħman sa da gaggawa, kuma rãnã da watã da taurãri hõrarru ne da umurninSa. To, Shĩ ne da halittar kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu tã bayyana! [7.55] Ku kirãyi Ubangijinku da ƙanƙan da kai, da kuma a ɓõye: lalle ne Shĩ, bã Yã son mãsu wuce iyãka. [7.56] Kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa a bãyan gyaranta. Kuma ku kirãye shi sabõda tsõro da tsammãni; lalle ne rahamar Allah makusanciya ce daga mãsu kyautatãwa. [7.57] Kuma Shĩ ne wanda Yake aika iskõki, sunã bishãra gaba ga rahamarSa, har idan sun ɗauki gizãgizai mãsu nauyi,(1) sai Mu kõra su ga wani gari matacce, sa´an nan Mu saukar da ruwa gare shi, sa´an nan Mu fitar, game da shi, daga dukkan ´ya´yan itace. Kamar wancan ne Muke fitar da matattu; tsammãninku, kunã tunãni. [7.58] Kuma gari mai kyau, tsirinsa yanã fita da iznin Ubangijinsa, kuma wanda ya mũnana, (tsirinsa) bã ya fita, fãce da wahala; kamar wannan ne, Muka sarrafa ãyõyi dõmin mutãne waɗanda suke gõdħwa. [7.59] Lalle ne, haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutãnħnsa, sai ya ce: "Yã mutãnħna! Ku bauta wa Allah! Bã ku da wani abin bautãwa waninSa. Lalle ne nĩ, inã yi muku tsõron azãbar wani Yini mai girma." [7.60] Mashawarta(1) daga mutãnensa suka ce: "Lalle ne mu, haƙĩƙa, Munã ganin ka a cikin ɓata bayyananniya." [7.61] Ya ce: "Yã mutãnena! Bãbu ɓata guda gare ni, kuma amma nĩ Manzo ne daga ubangijin halittu !" [7.62] "Inã iyar muku da sãƙonnin Ubangijina; kuma inã yi muku nasĩha, kuma inã sani, daga Allah, abin da ba ku sani ba. [7.63] "Shin, kunã mãmãkin cħwa ambato yã zo muku daga Ubangijinku a kan wani namiji, daga gare ku, dõmin ya yi muku gargaɗi, kuma dõmin ku yi taƙawa, kuma tsammãninku anã jin ƙanku?" [7.64] Sai suka ƙaryata shi, sa´an nan Muka tsĩrar da shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgin; kuma Muka nutsar da waɗanda suka ƙaryata shi game da ãyõyinMu. Lalle ne sũ, sun kasance wasu mutãne ɗĩmautattu. [7.65] Kuma zuwa ga Ãdãwa, ɗan´uwansu Hudu, ya ce: "Ya mutãnena! Ku bautã wa Allah! Bã ku da wani abin bautã wa, waninSa. Shin fa, bã zã ku yi taƙawa ba?" [7.66] Mashawarta waɗanda suka kãfirta daga mutãnensa suka ce: "Lalle ne mũ, haƙĩƙka, Munã ganin ka a cikin wata wauta! Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, Munã zaton ka daga maƙaryata." [7.67] Ya ce: "Yã mutãnena! Bãbu wata wauta a gare ni, kuma amma nĩ, Manzo ne daga Ubangijin halittu!" [7.68] Inã iyar muku da sãƙonnin Ubangijina, kuma nĩ, gare ku, mai nasĩha ne amintacce. [7.69] "Shin, kuma kun yi mãmãki cħwa ambato daga Ubangijinku ya zo muku a kan wani namiji daga gare ku, dõmin ya yi muku gargaɗi? Kuma ku tunã a lõkacin da Ya sanyã ku mãsu mayħwa daga bãyan mutãnen Nũhu, kuma Ya ƙãra muku zãti a cikin halitta. Sabõda haka ku tuna ni´imõmin Allah; tsammãninku kunã cin nasara." [7.70] Suka ce: "Shin, kã zo mana ne dõmin mu bauta wa Allah Shi kaɗai, kuma mu bar abin da ubanninmu suka kasance sunã bauta wa? To, ka zõ mana da abin da kake yi mana wa´adi da shi idan kã kasance daga mãsu gaskiya." [7.71] Ya ce: "Haƙĩƙa azãba da fushi sun auku a kanku daga Ubangijinku! Shin, kunã jãyayya da ni a cikin wasu sunãye waɗanda kũ ne kuka yi musu sunãyen, kũ da ubanninku, Allah bai saukar da wani dalili ba a gare su? To, ku yi jira. Lalle ne ni, tãre da ku mai jira ne." [7.72] To, sai Muka tsĩrar da shi, shĩ da waɗanda suke tãre da shi sabõda wata rahama daga gare Mu, kuma Muka katse ƙarshen waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu, kuma ba su kasance mũminai ba. [7.73] Kuma zuwa ga Samũdãwa ɗan´uwansu, Sãlihu, ya ce: "Yã mutãnena! Ku bauta wa Allah; bã ku da wani abin bauta wa wanninSa. Haƙĩƙa hujja bayyananniya tã zo muku daga Ubangijinku! wannan rãƙumar Allah ce, a gare ku, wata ãyã ce. Sai ku bar ta ta ci, a cikin ƙasar Allah, kuma kada ku shãfe ta da wata cũta har azãba mai raɗaɗi ta kãmã ku." [7.74] "Kuma ku tuna a lõkacin da Ya sanyã ku mamaya daga bãyan Ãdãwa kuma Ya zaunar da ku a cikin ƙasa, kunã riƙon manyan gidãje daga tuddanta, kuma kunã sassaƙar ɗãkuna daga duwãtsu; sabõda haka ku tuna ni´imõmin Allah, kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa kuna mãsu fasãdi."(1) [7.75] Mashawarta waɗanda suka yi girman kai daga mutanensa suka ce ga waɗanda aka raunanar,(2) ga waɗanda suka yi ĩmãni daga gare su: "Shin, kunã sanin cħwa Sãlihu manzo ne daga Ubangijinsa?" Suka ce: "Lalle ne mũ, da abin da aka aiko shi, mãsu ĩmãni ne." [7.76] Waɗanda suka yi girman kai suka ce: "Lalle ne mu, ga abin da kuka yi ĩmãni da shi kãfirai ne." [7.77] Sai suka sõke rãƙumar, kuma suka kangare daga barin umurnin Ubangijinsu, kuma suka ce: "Yã Sãlihu! Ka zõ mana da abin da kake yi mana wa´adi da shi, idan kã kasance daga manzanni !" [7.78] Sai tsãwa ta kãmã su, sabõda haka suka wãyi gari a cikin gidansu guggurfãne! [7.79] Sai ya jũya daga barinsu, kuma ya ce: "Ya mutãnena! Lalle ne, haƙĩƙa, nã iyar muku da manzancin Ubangijina. Kuma nã yi muku nasĩha kuma amma bã ku son mãsu nasĩha!" [7.80] Da Lũɗu, a lõkacin da ya ce wa mutãnensa: "Shin, kunã jħ wa alfãsha, bãbu kõwa da ya gabãce ku da ita daga halittu?" [7.81] "Lalle ne ku, haƙĩƙa kunã jħ wa maza da sha´awa, baicin mata; ôa, kũ mutãne ne maɓarnata." [7.82] Kuma bãbu abin da ya kasance jawãbin mutãnensa, fãce ɗai suka ce: "Ku fitar da su daga alƙaryarku: lalle ne sũ, wasu mutãne ne mãsu da´awar tsarki!" [7.83] Sai Muka tsĩrar da shi, shĩ da iyãlansa, fãce matarsa, ta kasance daga mãsu wanzuwa. [7.84] Kuma Muka yi ruwa a kansu da wani irin ruwa; Sai ka dũba yadda ãƙibar mãsu laifi ta kasance! [7.85] Kuma zuwa Madayana ɗan´uwansu Shu´aibu, ya ce: "Ya mutãnena! Ku bauta wa Allah; bã ku da wani abin bauta wa waninSa. Lalle ne, wata hujja bayyananniya daga Ubangijinku tã zõ muku! Sai ku cika mũdu da sikeli kuma kada ku nakasa wa mutãne kãyansu, kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa a bãyan gyaranta. Wannan ne mafi alhħri a gare ku, idan kun kasance mũminai." [7.86] "Kuma kada ku zauna ga kõwane tafarki kunã ƙyacħwa, kuma kunã kangħwa, daga hanyar Allah, ga wanda ya yi ĩmãni da shi, kuma kunã nħman ta ta zama karkatacciya, kuma ku tuna, a lõkacin da kuka kasance kaɗan, sai Ya yawaita ku, kuma ku dũba yadda ãƙibar mãsu fasãdi ta kasance:" [7.87] "Kuma idan wata ƙungiya daga gare ku ta kasance ta yi ĩmãni da abin da aka aiko ni da shi, kuma wata ƙungiya ba ta yi ĩmãni ba, to, ku yi haƙuri, har Allah Ya yi hukunci a tsakãninmu; kuma Shi ne Mafi alhħrin mãsu hukunci." [7.88] Mashawarta waɗanda suka kangare daga mutãnensa, suka ce: "Lalle ne, Munã fitar da kai, Yã Shu´aibu, kai da waɗanda suka yi Ĩmãni tãre da kai, daga alƙaryarmu; kõ kuwa lalle ku kõmo a cikin addininmu." Ya ce: "Ashe! Kuma kõ dã mun kasance mãsu ƙĩ?" [7.89] "Lalle ne mun ƙirƙira ƙarya ga Allah idan mun kõma a cikin addininku a bãyan lõkacin da Allah ya tsĩrar da mu daga gare shi, kuma bã ya kasancewa a gare mu, mu kõma a cikinsa, fãce idan Al1ah, Ubangijinmu Ya so. Ubangijinmu Yã yalwaci dukan kõme ga ilmi. Ga Allah muka dõgara. Yã Ubangijinmu! Ka yi hukunci a tsakãninmu da tsakanin mutãnenmu da gaskiya, kuma Kai ne Mafi alhħrin mãsu hukunci." [7.90] Kuma mashawarta waɗanda suka kãfirta daga mutãnensa, suka ce: "Lalle ne, idan kun bi Shu´aibu haƙĩƙa kũ, a lõkacin nan, mãsu hasãra ne." [7.91] Sai tsãwa ta kãma su, sabõda haka suka wãyi gari, a cikin gidansu, sunã guggurfãne. [7.92] Waɗanda suka ƙaryata Shu´aibu kamar ba su zauna ba a cikinta, waɗanda suka ƙaryata Shu´aibu, sun kasance sũ ne mãsu hasãra! [7.93] Sai ya jũya daga barinsu, kuma ya ce: "Yã mutãnena! Haƙĩƙa, nã iyar muku da sãƙonnin Ubangijina, kuma nã yi muku nasĩha! To, yãya zan yi baƙin ciki a kan mutãne kãfirai?" [7.94] Kuma ba Mu aika wani Annabi(1) a cikin wata alƙarya ba, fãce Mun kãma mutãnenta da azãba da cũta, tsammãninsu sunã yin ƙasƙantar da kai. [7.95] Sa´an nan kuma Muka musanya mai kyau a matsayin mummũna, har su yi yawa, kuma su ce: "Cũta da azãba sun shãfi ubanninmu." ( Sai su kõma wa kãfirci). Sai Mu kãmã su kwatsam! alhãli kuwa sũ, bã su sansancħwa." [7.96] Kuma dã lalle mutãnen alƙaryu sun yi ĩmãni kuma suka yi taƙawa dã haƙĩƙa Mun bũɗe albarkõki a kansu daga sama da ƙasa, kuma amma sun ƙaryata, don haka Muka kãma su da abin da suka kasance sunã tãrãwa. [7.97] Shin, mutãnen alƙaryu sun amince wa azãbar Mu ta jħ musu da dare, alhãli kuwa sunã barci? [7.98] Kõ kuwa mutãnen alƙaryu sun amince wa azãbarMu ta jħ musu da hantsi, alhãli kuwa sunã wãsa? [7.99] Shin fa, sun amince wa makarun Allah? To, bãbu mai amince wa makarun Allah fãce mutãne mãsu hasãra! [7.100] Shin, kuma bai shiryar da waɗanda suke gãdon ƙasa ba daga bãyan mutãnenta cħwa da Munã so, dã Mun sãme su da zunubansu, kuma Mu rufe a kan zukãtansu, sai su zama bã su ji? [7.101] Waɗancan alƙaryu Munã gaya maka daga lãbãransu, kuma lalle ne, haƙĩƙa manzanninMu sun jħ musu da hujjõji bayyanannnu; to, ba su kasance sunã yin ĩmãni da abin da suka ƙaryata daga gabãni ba. Kamar wancan ne Allah Yake rufħwa a kan zukãtan kãfirai. [7.102] Kuma ba Mu sãmi wani alkawari ba ga mafi yawansu, kuma lalle ne, Mun sãmi mafi yawansu, haƙĩƙa, fãsiƙai. [7.103] Sa´an nan kuma Mun aika Musa,(1) daga bãyansu, da ãyõyinMu zuwa ga Fir´auna da majalisarsa, sai suka yi zãlunci game da su. To, dũbi yadda ãƙibar maɓarnata take. [7.104] Kuma Musa ya ce: "Ya Fir´auna! Lalle ne nĩ, manzo ne daga Ubangijin halittu." [7.105] "Tabbatacce ne a kan kada in faɗi kõme ga Allah fãce gaskiya. Lalle ne, nã zo muku da hujja bayyananniya daga Ubangijinku; Sai ka saki Banĩ Isrã´ila tãre da ni." [7.106] Ya ce: "Idan kã kasance kã zo da wata ãyã, to, ka kãwõ ta, idan kã kasance daga mãsu gaskiya." [7.107] Sai ya jħfa sandarsa, sai gã ta kumurci bayyananne! [7.108] Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu dũbi! [7.109] Mashãwarta daga mutãnen Fir´auna suka ce: "Lalle ne, wannan, haƙĩƙa, matsafi ne mai ilmi." [7.110] " Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku: To, mħne ne kuke shawartawa?" [7.111] Suka ce: "Ka jinkirtar da shĩ, shĩ da ɗan´uwansa, kuma ka aika da mãsu gayyar mutãne a cikin garũruwa. [7.112] "Su zõ maka da duka matsafi, mai ilmi." [7.113] Kuma matsafa suka jħ wa fir´aunã suka ce: "Lalle ne, shin, Munã da ijãra, idan mun kasance mũ ne marinjaya?" [7.114] Ya ce: "Na´am kuma lalle ne kunã a cikin makusanta." [7.115] Suka ce: "Ya Mũsã! Kõ dai ka jħfa, kõ kuwa mu kasance, mũ ne, mãsu jħfãwa?" [7.116] Ya ce: "Ku jħfa." To a 1õkacin da suka jħfa, suka sihirce idãnun mutãne kuma suka tsõratar da su; Kuma suka jħ da tsafi mai girma." [7.117] Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cħwa: "Ka jħfa sandarka." Sai gã ta tanã lãƙumar abin da suke ƙarya da shi! [7.118] Gaskiya ta auku, kuma abin da suke aikatãwa ya ɓãci. [7.119] Sai aka rinjãye su a can, kuma suka jũya sunã ƙasƙantattu. [7.120] Kuma aka jħfar da matsafan, sunã mãsu sujada. [7.121] Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halittu." [7.122] "Ubangijin Mũsã da Harũna." [7.123] Fir´auna ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni da shi a gabãnin inyi izni a gare ku? Lalle ne, wannan, haƙĩƙa, mãkirci ne kuka mãkirta a cikin birni, dõmin ku fitar da mutãnensa daga gare shi; To, da sannu zã ku sani." [7.124] "Lalle ne, inã karkãtse hannãyenku da ƙafãfunku daga sãɓãni, sa´an nan kuma, haƙĩƙa, inã tsĩre, ku gabã ɗaya." [7.125] Suka ce: "Lalle ne mu, zuwa ga Ubangijinmu, mãsu jũyãwa ne." [7.126] "Kuma bã ka zargin kõme daga gare mu fãce dõmin mun yi ĩmãni da ãyõyin Ubangijinmu a lõkacin da suka zõ mana! Ya Ubangijinmu! Ka zuba haƙuri a kanmu, kuma Ka cika mana munã Musulmai!(1) " [7.127] Kuma mashawarta daga mutãnen Fir´auna suka ce: "Shin, zã ka bar Mũsã da mutãnensa dõmin su yi ɓarna a cikin ƙasa, kuma ya bar ka, kai da gumãkanka?" Ya ce: "Zã mu yayyanka ɗiyansu maza kuma mu rãya mãtansu; kuma lalle ne mũ, a bisa gare su, marinjãya ne." [7.128] Mũsã ya ce wa mutãnensa:(2) "Ku nħmi taimako da Allah, kuma ku yi haƙuri; Lalle ne ƙasa ta Allah ce, Yãna gãdar da ita ga wanda Yake so daga bãyinSa, kuma ãƙiba ta mãsu taƙawa ce." [7.129] Suka ce: "An cũtar da mu daga gabãnin ka zõ mana, kuma daga bãyan da kã zõ mana." Ya ce: "Akwai tsammãnin Ubangijinku, Ya halaka maƙiyanku, kuma Ya sanya ku, ku maye a cikin ƙasa, sa´an nan Ya dũba yadda kuke aikatãwa." [7.130] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun kãma mutãnen Fir´auna da tsananin shħkaru (fari) da nakasa daga ´ya´yan itãce; tsammãninsu sunã tunãwa. [7.131] Sa´an nan idan wani alhħri ya jħ musu, sai su ce: "Wannan nãmu ne," kuma idan masĩfa ta sãme su, sai su yi shu´umci da Mũsã da wanda yake tãre da shi. To, shu´umcinsu a wurin Allah yake, kuma amma mafi yawansu bã su sani!" [7.132] Kuma suka ce: "Kõ me ka zõ mana da shi daga ãyã, dõmin ka sihirce mu da ita, to, baza mu zama, sabõda kai, mãsu ĩmãni ba." [7.133] Sai Muka aika a kansu da cikõwa, da fãra, da ƙwarƙwata da kwãɗi, da jini; ãyõyi abũbuwan rarrabħwa;(1) Sai suka kangare, kuma suka kasance mutãne mãsu laifi. [7.134] Kuma a lõkacin da masĩfa ta auku a kansu, sukan ce: "Yã Mũsã! Ka rõƙa mana Ubangijinka, sabõda abin da Ya yi alkwari a wurinka, lalle ne idan ka kau da azãbar daga barinmu, haƙĩƙa Munã ĩmãni sabõda kai, kuma munã sakin Banĩ Isrã´ila tare da kai." [7.135] To, a lõkacin da Muka kuranye azãba daga barinsu zuwa a wani ajali wanda suke mãsu iske shi ne, sai gã su sunã warwarħwa! [7.136] Sai Muka yi azãbar rãmuwa, daga gare su, sabõda haka Muka nutsar da su a cikin tħku, dõmin lalle ne sũ, sun ƙaryata game da ãyõyinMu, kuma sun kasance daga barinsu, gãfilai. [7.137] Kuma Muka gãdar da mutãnen, waɗanda sun kasance anã raunana su, a gabacin ƙasa da yammacinta, wadda Muka sanya albarka a cikinta, kuma kalmar Ubangijinka mai kyau ta cika a kan Banĩ Isrã´ĩla, sabõda abin da suka yi na haƙuri. Kuma Muka murtsuke abin da Fir´auna da mutãnensa suka kasance sunã sanã´antawa, da abin da suka kasance sunã shimfiɗãwa.(2) [7.138] Kuma Muka ƙħtarar da Banĩ Isra´ila ga tħku, sai suka jħ a kan wasu mutãne waɗanda sunã lizimta da ibãda a kan wasu gumãka, nãsu suka ce: "Yã Mũsã! Ka sanya mana wani abin bautawa kamar yadda suke da abũbuwan bautãwa "(1) Ya ce: "Lalle ne kũ, mutãne ne kunã jahilta." [7.139] "Lalle ne waɗannan, abin da suke a cikinsa halakakke ne, kuma abin da suka kasance sunã aikãtawa ƙarya ne." [7.140] Ya ce: "Shin, wanin Allah nike nħma muku ya zama abin bautãwa, alhãli kuwa Shĩ (Allah) Ya fĩfĩta ku a kan halittu?" [7.141] Kuma a lõkacin da Muka tsĩrar da ku daga mutãnen Fir´auna, sunã tayã muku mugunyar azãba. sunã karkashe ɗiyanku maza, kuma sunã rãyar da matanku. Kuma a cikin wancan akwai jarrabãwa daga Ubangijinku,(2) Mai girma. [7.142] Kuma Muka yi wa´adi ga Mũsã da dare talãtin(3) kuma Muka cikã su da gõma, sai miƙatin Ubangijinsa ya cika dare arba´in. Kuma Mũsã ya ce wa ɗan´uwansa, Hãrũna: "Ka maye mini a cikin mutãnena, kuma ka gyãra, kuma kada ka bi hanyar mãsu fasãdi." [7.143] Kuma a lõkacin da Mũsã ya jħ ga mĩkatinMu, kuma Ubangijinsa Ya yi masa magana, shi Mũsã ya ce: "Yã Ubangijina! Ka nũna mini in yi dũbi zuwa gare Ka!" Ya ce: "Bã zã ka gan Ni ba, kuma amma ka dũba zuwa ga dũtse, to, idan ya tabbata a wurinsa, to, zã ka gan Ni." Sa´an nan a lõkacin da Ubangijinsa, Ya kuranye zuwa ga dũtsen, Ya sanyã shi niƙaƙƙe. Kuma Mũsã ya fãɗi sõmamme. To, a lõkacin da ya farka, ya ce: "TsarkinKa ya tabbata! Nã tũba zuwa gare Ka, kuma ni ne farkon mũminai." [7.144] Ya ce: "Ya Mũsã! Lalle ne Nĩ, Nã zãɓe ka bisa ga mutãne da manzanciNa, kuma da maganãTa. Sabõda haka ka riƙi abin da Nã bã ka, kuma ka kasance daga mãsu gõdiya." [7.145] Kuma Muka rubũta masa a cikin alluna daga kõwane abu, wa´azi da rarrabħwa ga dukan kõwane abu: "Sai ka riƙe su da ƙarfi, kuma ka umurci mutãnenka, su yi riƙo ga abin da yake mafi kyawunsu;(1) zã Ni nũna muku gidan fãsiƙai." [7.146] Zã Ni karkatar da waɗanda suke yin girman kai a cikin ƙasa, bã da wani hakki ba, daga ãyõyiNa. Kuma idan sun ga dukan ãyã, bã zã su yi ĩmãni da ita ba, kuma idan sun ga hanyar shiriya, bã zã su riƙe ta hanya ba, kuma idan sun ga hanyar ɓata, sai su riƙe ta hanya. Wancan ne, dõmin lalle ne su, sun ƙaryata da ãyõyinMu, kuma sun kasance, daga barinsu gãfilai. [7.147] Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu da gamuwa da Lãhira, ayyukansu sun ɓãci. Shin, ana saka musu, fãce da abin da suka kasance suna aikatãwa? [7.148] Kuma mutãnen Mũsã suka riƙi maraƙi,(2) jikin mutãne, yanã rũri, daga bãyan tafiyarsa, daga kãyan ƙawarsu. Shin, ba su ganĩ ba, cħwa lalle ne shi, bã ya yi musu magana, kuma bã ya shiryar da su ga hanya, sun riƙa shi, kuma sun kasance mãsu zãlunci. [7.149] Kuma a lõkacin da suka yi nadãma, kuma suka ga cħwa lalle ne sũ haƙĩƙa sun ɓace, suka ce: "Haƙĩƙa, idan UbangijinMu bai yi mana rahama ba, kuma Ya gãfarta mana, lalle ne munã kasancħwa daga mãsu hasãra." [7.150] Kuma a lõkacin da Mũsã ya kõma zuwa ga mutãnensa, yanã mai fushi, mai baƙin ciki, ya ce: "Tir da abin da kuka yi mini wakilci, a bãyanã! Shin, kun nħmi gaggawar umurnin Ubangijinku ne?" Kuma ya jefar da Allunan, kuma ya yi riƙo ga kan ɗan´uwansa yana jan sa zuwa gare shi. Ya ce: "Yã ɗan´uwata! Lalle ne mutãnen, sun ɗauke ni mai rauni, kuma sun yi kusa su kashe ni, sabõda haka kada ka dãrantar da maƙiya game da ni, kuma kada ka sanya ni tãre da mutãne azzãlumai." [7.151] Ya ce: "Yã Ubangijina! Ka gãfarta mini, nĩ da ɗan´uwana, kuma Ka shigar da mu a cikin rahamarKa, alhãli kuwa Kai ne Mafi rahamar mãsu rahama!" [7.152] Lalle ne waɗanda suka riƙi maraƙin, wani fushi daga Ubangijinsu da wani walãkanci a cikin rãyuwar dũniya, zã su sãme su: Kuma kamar wancan ne Muke sãka wa mãsu ƙirƙira ƙarya. [7.153] Kuma waɗanda suka aikata miyãgun ayyuka, sa´an nan suka tũba daga bãyansu kuma suka yi ĩmãni, lalle ne Ubangijinka daga bãyansu, haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [7.154] Kuma a lõkacin da fushin ya kwanta daga barin Mũsã, sai ya riƙi Allunan, kuma a cikin kwafensu akwai shiriya da rahama ga waɗanda suke sũ, ga Ubangijinsu, mãsu jin tsõro ne. [7.155] Kuma Mũsã ya zãɓi mutãnensa, namiji saba´in dõmin miƙãtinMu. To, a lõkacin da tsãwa ta kãma su, ya ce: "Yã Ubangijina! Dã Kã so, dã Kã halakar da su daga gabãni, sũ da ni. Shin zã Kahalaka mu, sabõda abin da wãwãyen daga gare mu suka aikata? Ba ta zama ba fãce fitinarKa Kanã ɓatarwa, da ita, wanda Kake so kuma kanã shiryarwa da ita, wanda Kake so; Kai ne Majiɓincinmu. Sai Ka gãfarta mana; kuma Ka yi mana rahama, alhãli kuwa Kai ne Mafi alhħrin mãsu gãfara." [7.156] "Kuma Ka rubũta mana alhħri a cikin wannan dũniya, kuma a cikin Lãhira. Lalle ne mũ, mun tũba zuwa gare Ka." Ya ce: "AzãbaTa Inã sãmu, da ita, wanda Nike so, kuma rahamaTa, ta yalwaci dukan kõme. Sa´an nan zã Ni rubũta ta ga waɗanda suke yin taƙawa, kuma sunã bãyar da zakka, da waɗanda suke, game da ãyõyinMu mũminai ne." [7.157] "Waɗanda suke sunã bin Manzo,(1) Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla. yanã umurnin su da alhħri kuma yana hana su daga barin abin da bã a so; kuma yanã halatta musu abũbuwa mãsu daɗi, kuma yana haramtarwar mũnana a kansu. Kuma yanã kãyar da nauyinsu daga barinsu, da ƙuƙummai waɗannan da suka kasance a kansu. To, waɗanda suka yi ĩmãni da shi kuma suka ƙarfafa shi, kuma suka taimake shi, kuma suka bi haske wanda aka saukar tãre da shi, waɗannan ne mãsu cin nasara." [7.158] Ka ce: "Yã kũ mutãne!(2) Lalle ne nĩ manzon Allah ne zuwa gare ku, gabã ɗaya. (Allah) Wanda Yake Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa; Bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Yanã rãyarwa, kuma Yanã matarwa, sai ku yi ĩmãni da Allah da ManzonSa, Annabi, Ummiyyi, wanda yake yin ĩmãni da Allah da kalmominSa; ku bĩ shi, tsammãninku, kunã shiryuwa." [7.159] Kuma daga mutãnen(3) Mũsã akwai al´umma, sunã shiryarwa da gaskiya, kuma da ita suke yin ãdalci. [7.160] Kuma Muka yayyanka su sibɗi gõma shã biyu, al´ummai. Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã a lõkacin da mutãnensa suka nħme shi, ga shãyarwa, cħwa: "Ka dõki dũtsen(1) da sandarka."Sai marmaro gõma shã biyu suka ɓuɓɓuga daga gare shi: Lalle ne kõwaɗanne mutãne sun san mashãyarsu. Kuma Muka saukar da darɓa da tantabaru a kansu."Ku ci daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku." Kuma ba su zãluncħ Mu ba; kuma amma rãyukansu suke zãlunta. [7.161] Kuma a lõkacin da aka ce masu: "Ku zauna ga wannan alƙarya,(2) kuma ku ci daga gare ta, inda kuka so, kuma ku ce: ´Saryarwa,´ kuma ku shiga kõfa kuna mãsu sujada; Mu gãfarta muku laifuffukanku, kuma zã Mu ɗãra wa mãsu kyautatãwa." [7.162] Sai waɗanda suka yi zãlunci daga gare su, suka musanya magana(3) watar wadda aka ce musu, sai Muka aika azãba a kansu, daga sama, sabõda abin da suka kasance sunã yi na zãlunci. [7.163] Kuma ka tambaye su daga alƙarya wadda ta kasance kusa ga tħku, a lõkacin da suke ƙħtare haddi a cikin Asabar, a lõkacin da kĩfãyensu, suke je musu a rãnar Asabar(4) ɗinsu jħre. Kuma a rãnar da ba su yi Asabar ba, bã su zuwa gare su; Kamar wancan ne Muke jarraba su da abin da suka kasance sunã yi na fãsiƙanci. [7.164] Kuma a lõkacin da wata al´umma daga gare su ta ce: "Don me kuke yin wa´azi ga mutãne waɗanda Allah Yake Mai halaka su kõ kuwa Mai yi musu azãba, azãba mai tsanani?" Suka ce: "Dõmin nħman hanzari zuwa ga Ubangijinku, kuma tsammãninsu, sunã yin taƙawa." [7.165] To, a lõkacin da suka manta da abin da aka tunãtar da su da shi, Mun tsĩrar da waɗanda suke hani daga cũta, kuma Muka kãma waɗanda suka yi zãlunci, da azãba mai tsanani dõmin abin da suka kasance sunã yi, na fasiƙanci. [7.166] Sa´an nan a lõkacin da suka yi girman kai daga barin abin da aka hana su daga gare shi, Muka ce musu: "Ku kasance birai ƙasƙantattu." [7.167] Kuma a lõkacin da Ubangijinku Ya sanar, lalle ne, zã Ya aika a kansu (Yahũd), zuwa, Rãnar Ƙiyãma, wanda zai ɗanɗana musu mummunar azãba, lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Mai gaggawar uƙũba ne, kuma shĩ haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [7.168] Kuma Muka yayyanka su, a cikin ƙasa, al´ummõmi, daga gare su akwai sãlihai, kuma daga gare su akwai wanda bã haka ba. Muka jarrabe su da abũbuwan alhħri da na musĩfa; Tsammãninsu, sunã kõmõwa. [7.169] Sai wasu´ yan bãya suka maye daga bãyansu, sun gaji Littãfin, sunã karɓar sifar(1) wannan ƙasƙantacciya, sunã cħwa: "Zã a gãfarta mana. "Idan kuma wata sifa irinta ta zo, za su karɓe ta. Shin, ba a karɓi alkawarin Littãfi ba a kansu cħwa kada su faɗa ga Allah, fãce gaskiya, alhãli kuwa sun karanta abin da yake a cikinsa, kuma Gidan Lãhira ne mafi alh ħri ga wanda ya yi taƙawa? Shin, bã zã ku hankalta ba? [7.170] Kuma waɗanda suke riƙħwa da littãfi kuma suka tsayar da salla, lalle ne Mũ, bã Mu tõzarta lãdar mãsu gyãrãwa. [7.171] Kuma a lõkacin da muka ɗaukaka dũtse(1) sama da su, kamar dai shi girgije ne, kuma suka haƙƙaƙe, lalle ne shĩ, mai fãɗuwa ne a gare su, (aka ce): "Ku karɓi abin da Muka kãwo muku da ƙarfi, kuma ku tuna abin da yake a cikinsa, tsammãninku kunã yin taƙawa." [7.172] Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya karɓi (alkawari) daga ɗiyan Ãdam, daga bãyayyakinsu, a zuriyarsu, kuma Ya shaidar da su a kan rãyukansu, (Ya ce): "Shin, bã Nĩ ne Ubangijinku ba?" Suka ce: "Na´am! Mun yi shaida!" (ya ce): "Kada ku ce a Rãnar Kiyãma: Lalle ne mũ, daga wannan, gafalallu ne."(2) [7.173] Kõ kuwa ku ce: "Abin sani kawai, ubanninmu suka yi shirki daga farko, kuma mũ, mun kasance zũriya daga bãyansu. Shin fa, Kanã halaka mu, sabõda abin da mãsu ɓãtãwa suka aikata?" [7.174] Kuma kamar haka Muke rarrabe ãyõyi, daki-daki; tsammãninsu, sunã kõmõwa. [7.175] Ka karanta a kansu lãbãrin wanda Muka kãwo masa(3) ãyõyinMu, sai ya sãɓule daga gare su, sai shaidan ya bi shi, sai ya kasance a cikin halakakku. [7.176] Kuma dã Mun so, da Mun ɗaukakã shi da su, kuma amma shĩ, ya nħmi dawwama a cikin ƙasa, kuma ya bi son zũciyarsa. To, misãlinsa kamar misãlin kare ne, idan ka yi ɗauki a kansa ya yi lallage, kõ kuwa ka bar shi sai ya yi lallage, wannan ne misãlin mutãne waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu: Ka jħranta karãtun lãbãrun; tsammãninsu sunã tunãni. [7.177] Tir da zama misãli, mutãnen da suka ƙaryata game da ãyõyinMu, kuma kansu suka kasance sunã zãlunta. [7.178] Wanda(4) Allah Ya shiryar, to, shĩ ne Mai shiryuwa, kuma wanda Ya ɓatar, to, waɗannan sũ ne mãsu hasãra. [7.179] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta sabõda Jahannama, mãsu yawa daga aljannu da mutãne, sunã da zukãta, ba su fahimta da su, kuma sunã da idãnu, bã su gani da su, kuma sunã da kunnuwa, ba su ji da su; waɗancan kamar bisãshe suke. ôa, sũ ne mafi ɓacħwa; Waɗancan sũ ne gafalallu. [7.180] Kuma Allah Yanã da sũnãye mãsu kyau.(1) Sai ku rõƙe shi da su, kuma ku bar waɗanda suke yin ilhãdi a cikin sũnãyenSa: zã a sãka musu abin da suka kasance sunã aikatãwa. [7.181] Kuma daga waɗanda Muka halitta akwai wata al´umma, sunã shiryarwa da gaskiya, kuma, da ita suke yin ãdalci. [7.182] Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu, zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba. [7.183] Kuma Inã yi musu jinkiri, lalle ne kaidĩNa, mai ƙarfi ne. [7.184] Shin, ba su yi Tunani ba, cħwa bãbu wata hauka ga ma´abucinsu? (2) shĩ bai zama ba fãce mai gargaɗi mai bayyanãwa. [7.185] Shin, ba su yi dũbi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kõme, kuma akwai tsammãni kasancewar ajalinsu, haƙĩƙa, ya kusanta? To, da wane lãbãri a bãyansa suke yin ĩmãni? [7.186] Wanda Allah Ya ɓatar to bãbu mai shiryarwa a gare shi: kuma Yanã barin su, a cikin ɓatarsu sunã ɗimuwa. [7.187] Sunã tambayar ka(3) daga Sa´a, a yaushe tabbatarta take? Ka ce: "Abin sani kawai, saninta a wurin Ubangijina yake. Bãbu mai bayyana ta ga lõkacinta fãce shĩ. Tã yi nauyi a cikin sammai da ƙasa. Bã zã ta zo muku ba fãce kwatsam." Sunã tambayar ka, kamar kai masani ne gare ta. Ka ce: "Abin sani kawai, saninta a wurin Allah yake, kuma amma mafi yawan mutãne bã su sani." [7.188] Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunkuɗe wata cũta, fãce abin da Allah Ya so. Kuma dã na kasance inã sanin gaibi, dã lalle ne, nã yawaita daga alhħri kuma cũta bã zã ta shãfe ni ba, nĩ ban zama ba face mai gargaɗi, kuma mai bãyar da bishãra ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni." [7.189] Shĩ ne wanda Ya halitta ku daga rai guda, kumaYa sanya, daga gare ta, ma´auranta, dõmin ya natsu zuwa gare(1) ta. Sa´an nan a lõkacin da ya rufe ta, ta yi ciki, ciki sassauƙa, sai ta shũɗe dashi. Sa´an nan a lõkacin da ya yi nauyi, sai suka rõƙi Allah, Ubangijinsu: "Lalle ne idan Ka bã mu abin ƙwarai, haƙĩƙa, zã mu kasance daga mãsu gõdiya." [7.190] To, a lõkacin da Ya bã su abin ƙwarai, suka sanya Masa abõkan tarayya a cikin abin da Ya ba su. To, Allah Yã tsarkaka daga abin da suke yi na shirki. [7.191] Shin, sunã shirki da abin da bã ya halittar kõme, kuma sũne ake halittãwa? [7.192] Kuma ba su iya bãyar da taimako gare su, kuma kansu ma, bã su iya taimaka! [7.193] Kuma idan kun kirãye su zuwa ga shiriya, bã zã su bĩ ku ba, daidai ne a gare ku, shin, kun kirãye su, kõ kuwa kũ mãsu kawaici ne! [7.194] Lalle ne waɗannan da kuke kira, baicin Allah, bãyĩ ne misãlanku: to, ku kirãye su, sa´an nan su karɓa muku, idan kun kasance mãsu gaskiya! [7.195] Shin sunã da ƙafãfu da suke yin tafiya da su? Kõ sunã da hannãye da suke damƙa da su? Kõ sunã da idãnu da suke gani da su? Ko sunã da kunnuwa da suke saurãre da su? Ka ce: "Ku kirãwo abũbuwan(2) shirkinku sa´an nan kuma ku yi mini kaidi, sa´an nan kada ku saurãra mini." [7.196] "Lalle ne, Majiɓincĩna Allah ne Wanda Ya saukar da Littãfi kuma Shĩ ne Yake jiɓintar sãlihai," [7.197] "Kuma waɗanda kuke kira, baicinSa, bã su iya taimakõn ku, kuma kansu ma, bã su iya taimaka." [7.198] Kuma idan ka kirãye su zuwa ga shiriya, bã zã su ji ba, kuma kanã ganin su, sunã dũbi zuwa gare ka, alhãli kuwa sũ, bã su gani. [7.199] Ka riƙi abin da ya sauƙaƙa; Kuma ka yi umurni da alhħri, Kuma ka kau da kai daga jãhilai.(1) [7.200] Kuma imma wata fizga daga Shaiɗan ta fizge ka, sai ka nħmi tsari ga Allah. Lalle ne shi, Mai jĩ ne, Masani. [7.201] Lalle ne waɗanda suka yi taƙawa idan wani tãshin hankali daga Shaiɗan ya shãfe su, sai su tuna (Allah) sai gã su, sun zama masu basĩra. [7.202] Kuma ´yan´uwan su (shaiɗanu) sunã taimakon su a cikin ɓata, sa´an nan kuma bã su taƙaitãwa. [7.203] Kuma idan ba ka je musu da wata ãyã ba, su ce: "Don me ba ka ƙãga ta ba?" Ka ce: "Abin sani kawai, inã biyar abin da aka yõ wahayi zuwa gare ni ne, daga Ubangjina. Wannan abũbuwan kula ne daga Ubangijinku, da shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suke yin imãni." [7.204] Kuma idan an karanta(2) Alƙur´ãni sai ku saurara gare shi, kuma ku yi shiru; Tsammãninku, anã yi muku rahama. [7.205] Kuma ka ambaci(3) Ubangijinka, a cikin ranka da ƙanƙan da kai, da tsõro, kuma kõma bãyan bayyanawa na magana, da sãfe da marece, kuma kada ka kasance daga gafalallu. [7.206] Lalle ne, waɗanda ke wurin Ubangijinka bã su yin girman kai ga bauta Masa, kuma sunã tsarake shi da tasbĩhi, kuma a gare shi suke yin sujada. @AL ANFAAL Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [8.1] Suna tambayar ka(1) ga ganĩma. ka ce: "Ganĩma ta Allah da ManzonSa ce. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma ku gyãra abin da yake a tsakãninku, kuma ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, idan kun kasance mũminai." [8.2] Abin sani kawai, mũminai sũ ne waɗanda suke idan an ambaci Allah, zukãtansu su firgita, kuma idan an karanta ãyõyinSa a kansu, su ƙãrã musu wani ĩmãni, kuma ga Ubangijinsu suke dõgara. [8.3] Waɗanda suke tsayar da salla, kuma daga abin da Muka azũrtã su sunã ciyarwa.(2) [8.4] Waɗannan sũ ne mũminai da gaskiya. Sunã da darajõji a wurin Ubangijinsu, da wata gãfara da arziki na karimci. [8.5] Kamar yadda Ubangijinka Ya fitar da kai daga gidanka da gaskiya, alhãli kuwa lalle wani ɓangare na mũminai, haƙĩƙa, sunã ƙyãma. [8.6] Sunã jãyayya da kai a cikin (sha´anin) gaskiya a bãyan tã bayyanã, kamar dai lalle anã kõra su zuwa ga mutuwa ne alhãli kuwa sunã kallo. [8.7] Kuma a lõkacin(3) da Allah Yake yi muku alkawari da ɗayan ƙungiya biyu, cħwa lalle ita tãku ce: kuma kunã gũrin cħwa lalle ƙungiya wadda bã ta da ƙaya ta kasance gare ku, kuma Allah Yanã nufin Ya tabbatar da gaskiya da kalmõminSa, kuma Ya kãtse ƙarshen kãfirai; [8.8] Dõmin Ya tabbatar da gaskiya, kuma Ya ɓãta ƙarya, kuma kõdã mãsu laifi sun ƙi. [8.9] A lõkacin da kuke nħman Ubangijinku taimako, sai Ya karɓa muku cħwa: "Lalle ne Nĩ, Mai taimakon ku ne da dubu daga malã´iku, jħre." [8.10] Kuma Allah bai sanya shi ba fãce Dõmin bishãra, kuma dõmin zukãtanku su natsu da shi, kuma taimakon, bai zama ba fãce daga wurin Allah; Lalle ne Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima. [8.11] A lõkacin da (Allah) Yake rufe ku da gyangyaɗi, ɗõmin aminci daga gare Shi, kuma Yanã saukar da ruwa(1) daga sama, a kanku, dõmin Ya tsarkake ku da shi, kuma Ya tafiyar da ƙazantar Shaiɗan daga barinku, kuma dõmin Ya ɗaure a kan zukãtanku, kuma Ya tabbatar da ƙafãfu da shi. [8.12] A lõkacin da Ubangijinka Yake yin wahayi zuwa ga Malã´iku cħwa: "Lalle ne Ni, Inã tãre da ku, sai ku tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni: Zã Ni jħfa tsõro a cikin zukãtan waɗanda suka kãfirta, sai ku yi dũka bisa ga wuyõyi kuma ku yi dũka daga gare su ga dukkan yãtsu(2) . [8.13] Wancan ne, dõmin lalle ne sũ, sunã sãɓa wa Allah da ManzonSa. Kuma wanda ya sãɓa wa Allah da ManzonSa, to, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne. [8.14] Wancan ne: "Ku ɗanɗane shi, kuma lalle ne akwai azãbar wuta ga kãfirai." [8.15] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun haɗu da waɗanda suka kãfirta ga yãƙi, to, kada ku jũya musu bãyayyakinku. [8.16] Kuma duka wanda(3) ya jũya musu bãyansa a yinin nan, fãce wanda ya karkata dõmin kõɗayya, kõ kuwa wanda ya jħ dõmin haɗuwa da wata ƙungiya, to, lalle ne ya kõma da fushi daga Allah, kuma matattararsa Jahannama, kuma tir da makõma ita! [8.17] To, bã kũ ne kuka kashe su ba; kuma amma Allah ne Ya kashe su: kuma ba ka yi jĩfa ba a lõkacin da ka yi jĩfa; kuma amma Allah ne Ya yi jĩfar.(1) Kuma dõminYa jarraba Musulmi da jarrabãwa mai kyau daga gare shi. Kuma Allah Mai ji ne, Masani. [8.18] Wancan ne, kuma lalle ne, Allah Mai raunana kaidin kãfirai ne. [8.19] Idan kun yi alfãnun cin nasara to lalle nasarar tã je muku, kuma idan kun hanu, to Shi ne Mafi alhħri a gare ku, kuma idan kun kõma zã Mu kõma, kuma jama´arku bã zã ta wadãtar muku da kõme ba, kõ dã tã yi yawa. Kuma lalle ne cħwa Allah Yanã tãre da mũminai! [8.20] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku jũya daga barinSa, alhãli kunã ji. [8.21] Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka ce: "Mun ji, alhãli kuwa sũ bã su ji." [8.22] Lalle ne, mafi sharrin dabbõbi a wurin Allah, sũ ne kurãme, bħbãye, waɗanda Bã su yin hankali. [8.23] Dã Allah Yã san wani alhħri a cikinsu, dã Yã jiyar da su, kuma kõ da Yãjiyar da su, haƙĩƙa, dã sun jũya , alhãli sũ, sunã mãsu hinjirħwa. [8.24] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku karɓa wa Allah, kuma ku karɓa wa Manzo, idan Ya kirãye ku zuwa ga abin da Yake rãyar da ku; Kuma ku sani cħwa Allah Yanã shãmakacħwa a tsakãnin mutum da zũciyarsa, kuma lalle ne Shĩ, a zuwa gare Shi ake tãra ku. [8.25] Kuma ku ji tsõron fitina wadda bã ta sãmun waɗanda suka yi zãlunci daga gare ku kħɓe, kuma ku sani, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne. [8.26] Ku tuna a lõkacin da kuke kaɗan, waɗanda ake raunanarwã a cikin ƙasa kunã tsõron mutãne su cafe ku, sai Ya tattara ku (a wurin natsuwa, Maɗina), kuma Ya ƙarfafã ku da taimakonSa kuma Ya azurtã ku daga abũbuwa mãsu dãɗi; Tsammãninku, kunã gõdħwa. [8.27] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku yaudari Allah da ManzonSa, kuma ku yaudari amãnõninku, alhãli kuwa kunã sane. [8.28] Kuma ku sani cħwa abin sani kawai, dũkiyõyinku da ´ya´yanku, wata fitina ce, kuma lalle ne Allah, a wurinSa, akwai ijãra mai girma. [8.29] Ya kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun bi Allah da taƙawa, zai sanyã muku mararraba (da tsõro) kuma Ya kankare ƙanãnan zunubanku daga barinku. Kuma Ya gãfartã muku. Kuma Allah ne Ma´abũcin falalã Mai girma. [8.30] Kuma a lõkacin da waɗanda(1) suka kãfirta sukħ yin mãkirci game da kai, dõmin su tabbatar da kai, kõ kuwa su kashe ka, kõ kuwa su fitar da kai, sunã mãkirci kuma Allah Yanã mayar musa da mãkirci kuma Allah ne Mafificin mãsu mãkirci. [8.31] Kuma idan aka karanta, ãyõyinMu a kansu, sukan ce: "Lalle ne mun ji dã muna so, haƙĩƙa, da mun faɗi irin wannan; wannan bai zama ba fãce tãtsunãyõyin mutãnen farko." [8.32] A lõkacin da suka ce: "Yã Allah! Idan wannan ya kasance shĩ ne gaskiya daga wurinKa, sai Ka yi ruwan duwãtsu, a kanmu, daga sama, kõ kuwa Kazõ mana da wata azãba, mai raɗaɗi." [8.33] Kuma Allah bai kasance Yanã yi musu azãba ba alhãli kuwa kai kanã cikinsu,(2) kuma Allah bai kasance Mai yi musu azãba ba alhãli kuwa sunã yin istigfãri. [8.34] Kuma mħne ne a gare su da Allah ba zai yi musu azãba ba, alhãli kuwa sũ, sunã kangħwa daga Masallaci Mai alfarma kuma ba su kasance majiɓintanSa ba? Bãbu majiɓintanSa fãce mãsu taƙawa. Kuma mafi yawansu ba su sani ba. [8.35] Kuma sallarsu a wurin Ɗãkin ba ta kasance ba fãce shħwa da yãyã; sai ku ɗanɗani azãba sabõda abin da kuka kasance kunã yi na kãfirci. [8.36] Lalle ne waɗanda suka kãfirta, sunã ciyar da dũkiyõyinsu, dõmin su kange daga hanyar Allah; to, zã a su ciyar da ita, sa´ an nan kuma ta kasance nadãma a kansu, sa´an nan kuma a rinjãye su. Kuma waɗanda suka kãfirta zuwa ga Jahannama ake tãra su; [8.37] Dõmin Allah Ya rarrabe mummũna daga mai kyau, kuma Ya sanya mummũnan, sãshensa a kan sãshe, sa´an nan Ya shirga shi gabã daya, sa´an nan Ya sanyã shi a cikin Jahannama. Waɗannan sũ ne mãsu hasãra. [8.38] Ka ce wa waɗanda suka kãfirta, idan sun hanu, zã a gãfarta musu abin da ya riga ya shige, kuma idan sun kõma, to, hanyar kãfiran farko, haƙĩƙa, ta shũɗe. [8.39] Kuma ku yãƙe su har wata fitina bã zã ta kasance ba, kuma addini dukansa ya kasance na Allah. To, idan sun hanu to lalle ne, Allah ga abin da kuke aikatãwa Mai gani ne. [8.40] Kuma idan sun jũya, to, ku sani cħwa lalle Allah ne Majiɓincinku: Mãdalla da Majiɓinci, kuma mãdalla da Mai taimako, Shĩ. [8.41] Kuma ku sani, abin da kuka sãmi(1) ganĩma daga wani abu, to, lalle ne Allah Yanã da humusinsa kuma da Manzo, kuma da mãsu zumunta, da marãyu da miskĩnai da ɗan hanya, idan kun kasance kun yi ĩmãni da Allah da abin da Muka saukar a kan bãwanMu a Rãnar Rarrabħwa, a Rãnar da jama´a biyu suka haɗu, kuma Allah ne, a kan kõwane abu, Mai ĩkon yi. [8.42] A lõkacin da kuke a gãɓa ta kusa sũ kuma sunã a gãɓa ta nħsa, kuma ãyarin yana a wuri mafi gangarãwa daga gare ku, kuma dã kun yi wa jũna wa´adi, dã kun sãɓa ga wa´adin; kuma amma dõmin Allah Ya hukunta abin da yake ya kasance abin aikatãwa. Dõmin wanda yake halaka ya halaka daga shaida, kuma mai rãyuwa ya rãyu daga shaida, kuma lalle Allah ne, haƙĩƙa, Mai ji Masani. [8.43] A lõkacin da Allah Yake nũna maka sũ sunã kaɗan, a cikin barcinka, kuma dã Ya nũna maka su sunã Da yawa, lalle ne dã kun ji tsõro, kuma lalle ne dã kun yi jãyayya a cikin al´amarin, kuma amma Allah Yã tsare ku: Lalle Shĩ ne Masani ga abin da yake a cikin ƙirãza. [8.44] Kuma a lõkacin da Yake nũna muku su, a lõkacin da kuka haɗu, a cikin idanunku sunã kaɗan, kuma Ya ƙarantar da ku a cikin idanunsu dõmin Allah Ya hukunta wani al´amari wanda ya kasance abin aikatãwa. Kuma zuwa ga Allah ake mayar da al´umurra. [8.45] Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun haɗu da wata ƙungiyar yãƙi, to, ku tabbata, kuma ku ambaci(2) Allah da yawa, tsammãninku kunã cin nasara. [8.46] Kuma ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku yi jãyayya har ku raunana kuma iskarku ta tafi, kuma ku yi haƙuri. Lalle ne Allah Yanã tãre da mãsu haƙuri. [8.47] Kada ku kasance kamar waɗanda suka fita daga gidãjensu(1) , sunã mãsu alfahari da yin riya ga mutãne, kuma sunã kangħwa daga hanyar Allah. Kuma Allah ne ga abin da suke aikatãwa Mai kħwayħwa. [8.48] Kuma a lõkacin da Shaiɗan(2) ya ƙawãce musu ayyukansu, kuma ya ce: "Bãbu marinjayi a gareku a yau daga mutãne, kuma nĩ maƙwabci ne gare ku." To, a lõkacin da ƙungiya biyu suka haɗu, ya kõma a kan digãdigansa, kuma ya ce: "Lalle ne nĩ barrantacce ne daga gare ku! Nĩ inã ganin abin da bã ku gani; ni inã tsõron Allah: Kuma Allah Mai tsananin uƙũba ne." [8.49] A lõkacin da munãfukai da waɗanda suke akwai cũtã a cikin zukãtansu, suke cħwa: "Addĩnin waɗannan yã rũɗe su. " Kuma wanda ya dõgara ga Allah, to, lalle ne Allah Mabuwãyi ne, Mai hikima. [8.50] Kuma dã kã gani, a lõkacin da Malã´iku suke karɓar rãyukan waɗanda suka kãfirta, sunã dukar fuskõkinsu da ɗuwãwunsu, kuma suna cħwa: "Ku ɗanɗani azãbar Gõbara." [8.51] "Wancan sabõda abin da hannãyenku suka gabãtar ne. Kuma lalle ne, Allah bai zama Mai zãlunci ba ga, bãyinSa." [8.52] "Kamar al´ãdar mutãnen Fir´auna da waɗanda suke gabãninsu, sun kãfirta da ãyõyin Allah, sai Allah Ya kãma su da zunubansu. Lalle Allah ne Mai ƙarfi, Mai tsananin uƙũba. [8.53] "Wancan ne, dõmin lalle ne, Allah bai kasance Mai canza wata ni´ima wadda ya ni´imtar da ita a kan wasu mutãne ba fãce sun sãke abin da yake ga rãyukansu, kuma dõmin lalle Allah ne Mai jĩ,Masani." [8.54] Kamar al´adar mutãnen Fir´auna da waɗanda suke a gabãninsu, sun ƙaryata game da ãyõyin Ubangijinsu, sai Muka halaka su, sabõda zunubansu, kuma Muka nutsar da mutãnen Fir´auna. Kuma dukansu sun kasance ne mãsu zãlunci. [8.55] Lalle mafi sharrin dabbõbi a wurin Allah, sũ ne waɗanda suka kãfirta, sa´an nan bã zã su yi ĩmãni ba. [8.56] Waɗanda ka yi ƙullin alkawari da su, daga gare su, sa´an nan kuma sunã warwarewar alkawarinsu a kõwane lõkaci kuma sũ, bã su yin taƙawa. [8.57] To, in dai ka kãma su a cikin yãƙi, sai ka kõre(1) waɗanda suke a bãyansu, game da su, tsammãninsu, zã su dinga tunãwa. [8.58] Kuma in ka ji tsõron wata yaudara daga wasu mutãne, to, ka jħfar da alkawarin, zuwa gare su, a kan daidaita: Lalle ne Allah, bã Ya son mayaudara. [8.59] Kuma waɗanda suka kãfirta kada su yi zaton sun tsħre: Lalle ne sũ, bã zã su gãgara ba. [8.60] Kuma ku yi tattali, dõminsu, abin da kuka sãmi ĩkon yi na wani ƙarfi,(2) kuma da ajiye dawaki, kunã tsoratarwa, game da shi, ga maƙiyin Allah kuma maƙiyinku da wasu, baicin su, ba ku san su ba, Allah ne Yake sanin su, kuma abin da kuka ciyar daga wani abu a cikin hanyar Allah, zã a cika muku sakamakonsa, kuma kũ ba a zãluntar ku. [8.61] Kuma idan sun karkata zuwa ga zaman lãfiya, to, ka karkata zuwa gare shi, kuma ka dõgara ga Allah: Lalle ne Shĩ, Mai ji ne Masani. [8.62] Kuma idan sun yi nufin su yaudare ka, to, lalle ma´ishinka Allah ne, Shĩ ne wanda Ya ƙarfafa ka da taimakonSa, kuma da mũminai. [8.63] Kuma Ya sanya sõyayya a tsakãnin zukãtansu. Dã kã ciyar da abin da yake cikin ƙasa, gabã ɗaya, dã ba ka sanya sõyayya a tsakãnin zukãtansu ba, kuma amma Allah Yã sanya sõyayya a tsakãninsu. Lalle Shi ne Mabuwãyi, Mai hikima. [8.64] Ya kai Annabi! Ma´ishinka Allah ne, kai da wanda ya biye maka daga mũminai. [8.65] Ya kai Annabi! Ka kwaɗaitar da mũminai a kan yãƙi. Idan mutum ashirin mãsu haƙuri sun kasance daga gare ku, zã su rinjãyi mħtan kuma idan ɗari suka kasance daga gare ku, zã su rinjãyi dubu daga waɗanda suka kãfirta, dõmin sũ, mutãne ne bã su fahimta. [8.66] A yanzu Allah Yã sauƙaƙe daga gare ku, kuma Yã sani cħwa lalle ne akwai mãsu rauni a cikinku. To, idan mutum ɗari, mãsu haƙuri, suka kasance daga gare ku, zã su rinjãyi mħtan, kuma idan dubu suka kasance daga gare ku, zã su rinjãyi dubu biyu, da iznin Allah. Kuma Allah Yanã tãre da mãsu haƙuri. [8.67] Bã ya kasancewa(1) ga wani annabi, kãmammu su kasance a gare shi sai (bãyan) yã zubar da jinainai a cikin ƙasa. Kunã nufin sifar dũniya kuma Allah Yanã nufin Lãhira. Kuma Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima. [8.68] Bã dõmin wani Littãfi daga Allah ba, wanda ya gabãta(2) , dã azãba mai girma daga Allah tã shãfe ku a cikin abin da kuka kãma. [8.69] Sabõda haka, ku ci daga abin da kuka sãmu ganĩma, yanã halal mai kyau. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai. [8.70] Ya kai Annabi! Ka ce wa wanda yake a cikin hannãyenku daga kãmammu: "Idan Allah Ya san akwai wani alhħri a cikin zukãtanku, zai kawo muku mafi alhħri daga abin da aka karɓa daga gare ku, kuma Ya yi muku gãfara. Kuma Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai." [8.71] Kuma idan sun yi nufin yaudararka, to, haƙĩƙa, sun yaudari Allah daga gabãni sai Ya bãyar da dãmã daga gare su: Kuma Allah ne Masani, Mai hikima. [8.72] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi hijira, kuma suka yi jihãdi da dũkiyõyinsu da rãyukansu, a cikin hanyar Allah, da waɗanda suka bãyar da masauki, kuma suka yi taimako. Waɗancan, sãshensu waliyyai ne ga sãshe. Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma ba su yi hijira(1) ba, bã ku da wani abu daga waliccinsu, sai sun yi hijira. Kuma idan suka nħme ku taimako a cikin addini, to taimako yã wajaba a kanku, fãce a kan mutãne waɗanda a tsakãninku da tsakãninsu akwai wani alkwari. Kuma Allah ne, ga abin da kuke aikatãwa, Mai gani. [8.73] Kuma waɗanda suka kãfirta sãshensu ne waliyyan sãshe, idan ba ku aikata shi ba, wata fitina zã ta kasance a cikin ƙasa, da fasãdi babba. [8.74] Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka yi hijira, kuma suka yi Jihãdi, a cikin hanyar Allah, kuma da waɗanda suka bãyar da masauki, kuma suka yi tamiako, waɗannan sũ ne mũminai da gaskiya, sunã da gãfara da wani abinci na karimci. [8.75] Kuma waɗanda suka yi ĩmãni daga bãya, kuma suka yi hijira kuma suka yi jihãdi tãre da ku, to, waɗannan daga gare ku suke. Kuma ma´abũta zumunta, sãshensu ne waliyyan(2) sãshe a cikin Littãfin Allah. Lalle Allah ne ga dukkan kõme Masani. @AT TAUBAH [9.1] Barranta daga Allah da ManzonSa zuwa ga waɗanda kuka yi wa alkawari daga mãsu shirki(1) [9.2] Sabõda haka ku yi tafiya a cikin ƙasa watã huɗu,(2) kuma ku sani lalle kũ, bã mãsu buwãyar Allah ba ne, kuma lalle Allah ne Mai kunyatar da kãfirai. [9.3] Kuma da yħkuwa daga Allah da ManzonSa zuwa ga mutãne, a Rãnar Haji Babba cħwa lallene Allah Barrantacce ne daga mãsu shirki, kuma ManzonSa (haka). To, idan kun tũba to shi ne mafi alhħri a gare ku, kuma idan kun jũya, to, ku sani lalle ne kũ, bã mãsu buwãyar Allah ba ne. Kuma ka bãyar da bishãra ga waɗanda suka kãfirta, da azãba mai raɗaɗi. [9.4] Sai waɗanda kuka yi wani alkawari daga mãsu shirki, sa´an nan kuma ba su rage ku da kõme ba, kuma ba su taimaki kõwa a kanku ba, to, ku cika alkawarin, zuwa gare su, har ga iyakar yarjħjħyarsu. Lalle ne Allah Yanã son mãsu taƙawa. [9.5] Kuma idan watanni, mãsu alfarma suka shige, to, ku yãki mushirikai inda kuka sãmħ su, kuma ku kãmã su, kuma ku tsare su, kuma ku zaune musu dukkan madãkata. To, idan sun tũba, kuma suka tsayar da salla, kuma suka bãyar da zakka to ku sakar musu da hanyarsu. Lalle Allah ne Mai gãfara,Mai jin ƙai. [9.6] Idan wani daga mushirikai ya nemi maƙwabtakarka to, ka ba shi maƙwabtakar har ya ji, maganar Allah, sa´an nan ka isar da shi ga wurin amincewarsa. Wancan fa domin lalle ne su, mutãne ne waɗanda ba su sani ba. [9.7] Yãya wani alkawari a wurin Allah a wurin ManzonSa yake kasancħwa ga mushirikai, fãce ga waɗanda kuka yi wa alkawari wurin Masallaci Mai alfarma? To matuƙar sun tsaya sõsai gare ku, sai ku tsayu sõsai gare su. Lalle ne Allah Yanã son mãsu taƙawa. [9.8] Yãya, alhãli idan sun ci nasara a kanku, bã zã su tsare wata zumun ta ba a cikinku, kuma haka wata amãna, sunã yardar da ku da bãkunansu kuma zukãtansu sunã ƙi? Kuma mafi yawansu fãsiƙai ne. [9.9] Sun saya da ãyõyin Allah, ´yan kuɗi kaɗan, sa´an nan suka kange daga hanyar Allah. Lalle ne sũ, abin da suka kasance sunã aikatãwa yã mũnana. [9.10] Bã su tsaron wata zumunta a cikin mũminai, kuma haka bãsu tsaron wata amãna. Kuma waɗannan ne mãsu ta´adi. [9.11] Sa´an nan idan sun tũba(1) kuma suka tsayar da salla, kuma suka bãyar da zakka, to, ´yan´uwanku ne a cikin addini, kuma Munã rarrabe ãyõyi daki-daki, ga mutãne waɗanda suke sani. [9.12] Kuma idan suka warware rantsuwõyin amãna daga bãyan alkawarinsu, kuma suka yi sũka a cikin addininku, to, ku yaki shũgabannin kãfirci. Lalle ne sũ, bãbu rantsuwõyin amãna a gare su. Tsammãninsu sunã hanuwa. [9.13] Shin, bã ku yaƙin mutãne, waɗanda suka warware rantsuwõyinsu, kuma suka yi niyya ga fitar da Manzo, kuma sũ ne suka fãra muku, tun a farkon lõkaci? Shin kunã tsõron su ne? To, Allah ne marfi cancantar ku ji tsõronSa, idan kun kasance mũminai! [9.14] Ku yãƙe su, Allah Ya yi musu azabã da hannãyenku, kuma Ya kunyatar da su, kuma Ya taimake ku, kuma Ya warkar da ƙirãzan mutãne mũminai. [9.15] Kuma Ya tafĩ da fushin zukãtansu, kuma Ya karɓi tũba a kan wanda Ya so. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima. [9.16] Kõ kunã zaton(1) a bar ku, tun Allah bai bayyana waɗanda suka yi jihãdi ba daga gare ku, kuma sũ ba su riƙi wani shigeba, baicin Allah da ManzonSa da mũminai? Kuma Allah ne Mai jarrabãwa ga abin da kuke aikatãwa. [9.17] Bã ya kasancewa ga mãsu shirki su rãya masallatan Allah, alhãli kuwa sunã mãsu bãyar da shaida a kan rãyukansu da kafirci, waɗannan ayyukansu sun ɓãci, kuma a cikin wutã sũ madawwama [9.18] Abin sani kawai, mai rãya masallãtan Allah, shĩ ne wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya tsayar da salla kuma ya bãyar da zakka, kuma bai ji tsõron kõwa ba fãce Allah. To, akwai tsammãnin waɗannan su kasance daga shiryayyu. [9.19] Shin, kun sanya shãyar da mahajjata da rãyar da Masallaci Mai alfarma kamar wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya yi jihãɗi a cikin hanyar Allah? Bã su daidaita a wurin Allah. Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai. [9.20] Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi hijira, kuma suka yi jihãdi, a cikin hanyar Allah, da dũkiyõyinsu, da rãyukansu, sũ ne mafi girma ga daraja, a wurin Allah, kuma waɗannan sũ ne mãsu babban rabo. [9.21] Ubangijinsu Yanã yi musu bishãra da wata rahama daga gare shi, da yarda, da gidãjen Aljanna. sunã da, a cikinsu, ni´ima zaunanniya. [9.22] Sunã madawwamã a cikinsu, har abada. Lalle ne Allah a wurinSa akwai lãda mai girma. [9.23] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi ubanninku da ´yan´uwanku masõya, idan sun nũna son kãfirci a kan ĩmãni.(1) Kuma wanda ya jiɓince su daga gare ku, to, waɗannan sũ ne azzãlumai. [9.24] Ka ce: "Idan ubanninku da ɗiyanku da ´yan´uwanku da mãtanku da danginku da dũkiyõyi, waɗanda kuka yi tsiwirwirinsu, da fatauci wanda kuke tsõron tasgaronsa, da gidaje waɗanda kuke yarda da su, sun kasance mafiya sõyuwa a gare ku daga Allah da ManzonSa, da yin jihãdi ga hanyarSa, to, ku yi jira har Allah Ya zo da umurninSa! Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne fãsiƙai." [9.25] Lalle ne, haƙĩƙa, Allah Yã taimake ku a cikin wurãre mãsu yawa, da Rãnar Hunainu,(2) a lõkacin da yawanku ya bã ku sha´awa, sai bai amfãnar da ku da kõme ba, kuma ƙasa ta yi ƙunci a kanku da yalwarta, sa´an nan kuma kuka jũya kunã mãsu bãyar da bãya. [9.26] Sa´an nan kuma Allah Ya saukar da natsuwarSa a kan ManzonSa kuma a kan mũminai, kuma Ya saukar da rundunõni waɗanda ba ku gan su ba, kuma Ya azabtar da waɗanda suka kãfirta: Wancan ne sakamakon kãfirai. [9.27] Sa´an nan kuma Allah Ya karɓi tũba daga bãyan wancana kan wanda Ya so. Kuma Allah ne Mai gãfara, Mai rahama. [9.28] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, mushirikai najasa ne, sabõda haka kada su kusanci Masallaci Mai alfarma a bãyan shħkararsu wannan. Kuma idan kun ji tsõron talauci(1) to, da sannu Allah zai wadãta ku daga falalarSa, idan Ya so. Lalle Allah ne Masani, mai hikima. [9.29] Ku yãƙi waɗanda(2) bã su yin ĩmãni da Allah kuma bã su ĩmãni da Rãnar Lãhira kumabã su haramta abin da Allah da ManzonSa suka haramta, kuma bã su yin addini, addinin gaskiya, daga waɗanda aka bai wa Littãfi, har sai sun bãyar da jizya daga, hannu, kuma sunã ƙasƙantattu. [9.30] Kuma Yahũdãwa suka ce: "Uzairu ɗan Allah ne."Kuma Nasãra suka ce: "Masĩhu ɗan Allah ne." Wancan zancensu ne da bãkunansu. Sunã kamã da maganar waɗanda suka kãfirta daga gabãni. Allah Yã la´ance su! Yãya aka karkatar da su? [9.31] Sun riƙi mãlamansu(3) (Yahũdu) da ruhubãnãwansu (Nasãra) Ubannangiji, baicin Allah, kuma sun riƙi Masĩhu ɗan Maryama ( haka). Kuma ba a umurce su ba fãce da su bautã wa Ubangiji Guda. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. TsarkinSa ya tabbata daga barin abin da suke yin shirki da shi. [9.32] Sunã nufin su bice hasken Allah da bãkunãnsu. Kuma Allah Yanã ki, fãce dai Ya cika haskenSa, kuma kõ da kãfirai sun ƙi. [9.33] Shi ne wanda Ya aiko manzonSa da shiriya da addinin gaskiya, dõmin ya bayyanl shi a kan addini dukansa, kuma kõ dã mushirikai sun ƙi. [9.34] Yã waɗanda suka yi ĩmãni! Lalle ne mãsu yawa daga Ahbãr(1) da Ruhbãnãwa haƙĩƙa sunã cin dũkiyar mutãne da ƙarya, kuma sunã kangħwa daga hanyar Allah. Kuma waɗanda suke taskacħwar zĩnãriya da azurfa, kuma bã su ciyar da ita a cikin hanyar Allah, to, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi. [9.35] A Rãnar da ake ƙõna shi a kanta a cikin wutar Jahannama, sai a yi lalas da ita ga gõshinansu da sãshinansu da bãyayyakinsu, (a ce musu): "Wannan ne abin da kuka taskace dõmin rãyukanku. To, ku ɗanɗani abin da kuka kasance kunã sanyãwa a taska." [9.36] Lallai ne ƙidãyayyun watanni a wurin Allah watã gõma shã biyu ne a cikin Littãfin(2) Allah, a Rãnar da Ya halicci sammai da ƙasa daga cikinsu akwai huɗu mãsu alfarma. Wannan ne addini madaidaici. Sabõda haka kada ku zãlunci kanku a cikinsu. Kuma ku yãƙi mushirikai gabã ɗaya, kamar yadda suke yãƙar ku gabã ɗaya. Kuma ku sani cħwa lallai ne Allah Yanã tãre da mãsu taƙawa. [9.37] Abin sani kawai, "Jinkirtãwa" ƙãri ne a cikin kãfirci, anã ɓatar da waɗanda suka kãfirta game da shi. Sunã halattar da watã a wata shħkara kuma su haramtar da shi a wata shħkara dõmin su dãce da adadin abin da Allah Ya haramta. Sabõda haka sunã halattar da abin da Allah Ya haramtar. An ƙawãce musu mũnanan ayyukansu. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne kãfirai. [9.38] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Mħne ne a gare ku, idan ance muku, "Ku fita da yãƙi a cikin hanyar Allah," sai ku yi nauyi(1) zuwa ga ƙasa. Shin, kun yarda da rãyuwar dũniya ne daga ta Lãhira? To jin dãɗin rãyuwar dũniya bai zama ba a cikin Lãhira, fãce kaɗan. [9.39] Idan ba ku fita da yãƙi ba, Allah zai azabta ku da azãba mai raɗaɗi, kuma Ya musanya wasu mutãne, wasunku (a maimakonku). Kuma bã zã ku cũtar da Shida kõme ba. Kuma Allah a kan dukan kõme Mai ĩkon yi ne. [9.40] Idan ba ku taimake shi ba, to, lalle ne Allah Yã taimake shi, a lõkacin da waɗanda suka kãfirta suka fitar da shi, Yanã na biyun biyu, a lõkacin da suke cikin kõgon dũtse, a lõkacin da yake cħwa da sãhibinsa: "Kada ka yi baƙin ciki, lalle ne Allah Yanã tãre da mu." Sai Allah Ya saukar da natsuwarSa a kansa, kuma Ya taimake shi da waɗansu rundunõni, ba ku gan su ba, kuma Ya sanya kalmar waɗanda suka kãfirta maƙasƙanciya, kuma kalmar Allah ita ce maɗaukakiya. Kuma Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima. [9.41] Ku fita da yãƙi kunã mãsu sauƙãƙan kãyã da mãsu nauyi, kuma ku yi jihãdi da dũkiyõyinku da kuma rãyukanku a cikin hanyar Allah. Wancan ne mafi alhħri a gare ku, idan kun kasance kunã sani. [9.42] Dã yã kasance(1) wata siffar dũniya ce: makusanciya, da tafiya matsakaiciya, dã sun bĩ ka, kuma amma fagen yã yi musu nĩsa.Kuma zã su yi ta yin rantsuwa da Allah, "Dã mun sãmi dãma, dã mun tafi tare da ku." Sunã halakar da kansu (da rantsuwar ƙarya) ne, kuma Allah Yanã sanin lalle, haƙĩƙa, sumaƙaryata ne.´ [9.43] Allah Ya yãfe maka laifi. Dõmin me ka yi musu izinin zama? Sai waɗanda suka yi gaskiya ssun bayyana a gare ka, kuma ka san maƙaryata. [9.44] Waɗanda suke yin ĩmãnida Allah da Rãnar Lãhira, bã zã su nħmi izininka ga yin, jihãdida dũkiyõyinsu da rãyukansu ba. Kuma Allah ne Masani ga mãsu taƙawa. [9.45] Abin sani kawai, waɗanda bã sa ĩmãni da Allah, da Rãnar Lãhira, kuma zukãtansu suka yi shakka, sũ ne ke nħman izininka, sa´an nan a cikin shakkarsu sunã ta yin kai kãwo. [9.46] Kuma dã sun yi nufin fita, dã sun yi wani tattali sabõda shi, kuma amma Allah Ya ƙi zãburarsu, sai Ya nauyayar da zamansu. Kuma aka ce ku zauna tãre da mãsu(2) zama. [9.47] Dã sun fita a cikinku bã zã su ƙãre ku da kõme ba fãce da ɓarna, kuma lalle dã sun yi gaggãwar sanya annamĩmanci a tsakãninku, sunã nħma muku fitina. Kuma a cikinku akwai ´yan rahõto sabõda su. Kuma Allah ne Masani ga azzãlumai, [9.48] Kuma lalle ne, haƙĩƙa sun nħmi fitina daga gabãni, kuma, suka jũya maka al´amari, har gaskiya ta zo,(1) kuma umurnin Allah Ya bayyana, alhãli sunã mãsu ƙyãma, [9.49] Kuma daga cikinsu(2) akwai mai cħwa, "Ka yi mini izinin zama, kuma kada ka fitine ni." To, a cikin fitinar suka fãɗa. Kuma lalle ne Jahannama, haƙĩƙa, mai ƙħwayħwa ce ga kãfirai. [9.50] Idan wani alhħri ya sãme ka, zai ɓãta musu rai, kuma idan wata masifa ta sãme ka sai su ce: "Haƙĩƙa, mun riƙe al´amarinmu daga gabãni."Kuma sujũya, alhãli kuwa sunã mãsu farin ciki. [9.51] Ka ce: "Bãbu abin da yake sãmun mu fãce abin da Allah Ya rubũta sahõda mu. Shĩ ne Majiɓincinmu. Kuma ga Allah, sai mũminai su dõgara." [9.52] Ka ce: "Shin, kunã dãko ne da mu? Fãce dai da ɗayan abũbuwan biyu(3) mãsu kyau, alhãli kuwa mũ, munã dãko da ku, AllahYa sãme ku da wata azãba daga gare Shi, kõ kuwa da hannayenmu. To, ku yi dãko. Lalle ne mũ, tãre da ku mãsu dãkon ne." [9.53] Ka ce: "Ku ciyar a kan yarda kõ kuwa a kan tĩlas. Bã zã a karɓa daga gare ku ba. Lalle ne kũ, kun kasance mutãne fãsiƙai." [9.54] Kuma bãbu abin da ya hana a karɓi ciyarwarsu daga gare su fãce dõmin sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa, kuma bã su zuwa ga salla fãce Luma sunã mãsu kasãla, kuma bã su ciyarwa fãce sunã mãsu ƙyãma. [9.55] Sabõda haka, kada dũkiyõyinsu su bã ka sha´awa, kuma haka ´ya´yansu. Abin sani kawai, Allah Yanã nufin Ya yi musu azãba, da su a cikin rãyuwar dũniya, kuma rãyukansu su fita alhãli kuwa sunã kãfirai. [9.56] Kuma sunã rantsuwa da Allah cħwa, lalle ne sũ, haƙĩƙa, daga gare ku suke, alhãli kuwa ba su zamo daga gare ku ba. Kuma amma sũ mutãne ne mãsu tsõro. [9.57] Dã sunã sãmun mafaka kõ kuwa waɗansu ɓulõli, kõ kuwa wani mashigi, da sun, jũya zuwa gare shi, kuma suna gaggawar shiga. [9.58] Kuma daga cikinsu akwai wanda yake zunɗen ka a kan sha´anin dũkiyõyin sadaka, sai idan an bã su daga cikinta, su yarda, kuma idan ba a bã su ba daga cikinta sai su zamo sunã mãsu fushi. [9.59] Kuma dã dai su lalle sun yarda da abin da Allah Ya bã su, da ManzonSa kuma suka ce: "Ma´ishinmu Allah ne, zai kãwo mana daga falalarSa kuma ManzõnSa (zai bã mu). Lalle ne mũ, zuwa ga Allah mãsu kwaɗayi ne." [9.60] Abin sani kawai, dũkiyõyin sadaka na faƙĩrai ne da miskinai da mãsu aiki a kansu, da waɗanda ake lallãshin zukãtansu, kuma a cikin fansar wuyõyi, da mabarta, da a cikin hanyar Allah da ɗan hanya (matafiyi). Farilla daga Allah. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima. [9.61] Kuma daga cikinsu akwai waɗanda suke cũtar Annabi, kuma sunã cħwa "Shi kunne(1) ne." Ka ce: "Kunnen alhħri gare ku,Yanã ĩmãni da Allah, kuma Yanã yarda da mũminai, kuma rahama ne ga waɗanda suka yi ĩmãni daga gare ku."Kuma waɗanda suke cũtar Manzon Allah sunã da azãba mai raɗaɗi. [9.62] Sunã rantsuwa da Allah sabõda ku, dõmin su yardar da ku. Kuma Allah da ManzonSa ne mafi cancantar su yardar da Shi, idan sun kasance mũminai. [9.63] Shin, ba su sani ba cħwa "Lalle ne wanda ya sãɓa wa Allah da ManzonSa, haƙĩƙa Yanã da wutar Jahannama, Yanã madawwami a cikinta? Waccan ita ce wulãkantãwa babba!" [9.64] Munãfukai sunã tsõron a saukar da wata sũra a kansu,wadda take bã su lãbãri ga abin da yake cikin zukãtansu. Ka ce: "Ku yi izgili. Lalle ne, Allah ne Mai fitai da abin da kuke tsõro." [9.65] Kuma lalle ne, idan ka tambaye(1) , su haƙĩƙa, sunã cħwa, "Abin sani kawai, mun kasance munã hĩra kuma munã wãsã. Ka ce: "Shin da Allah, da kuma ãyõyinSa da ManzonSa kuka kasance kunã izgili?" [9.66] "Kada ku kãwo wani uzuri, haƙĩƙa, kun kãfirta a bãyanĩmãninku. Idan Mun yãfe laifi ga wata ƙungiya daga gare ku, zã Mu azabta wata ƙungiya sabõda, lalle, sun kasance mãsu laifi." [9.67] Munãfukai maza da munãfukai mãtã, sãshensu(2) daga sãshe, sunã umurni da abin ƙi kuma sunã hani daga alhħri.Kuma sunã damƙħwar hannayensu.Sun mance Allah, sai Ya mantã da su. Lalle ne munãfukai sũ ne fãsiƙai. [9.68] Allah yã yi wa´adi ga munãfukai maza da munãfukai mãtã da kãfirai da wutar Jahannama, sunã madawwama a cikinta. Ita ce ma´ishiyarsu. Kuma Allah Yã la´ance su, kuma sunã da azãba zaunanniya. [9.69] Kamar waɗanda suke a gabãninku, sun kasance mafi tsananin ƙarfi daga gare ku, kuma mafi yawan dũkiyõyi da ɗiya. Sai suka ji daɗi da rabonsu, sai kuka ji daɗi da rabonku kamar yadda waɗanda suke a gabãninku suka ji dãɗi, da rabonsu, kuma kuka kũtsa kamar kũtsãwarsu. Waɗancan ayyukansu sun ɓãci a dũniya da Lãhira, kuma waɗannan sũ ne mãsu hasãra. [9.70] Shin lãbarin waɗanda suke a gabãninsu bai je musu ba, mutãnen Nũhu da Ãdãwa da Samũdãwa da mutãnen Ibrãhĩm da Ma´abũta Madyana da waɗanda aka birkice? Manzanninsu sun jħ musu da ãyõyayi bayanannu. To, Allah bai kasance Yanã zãluntar su ba, amma sun kasance rãyukansu suke zãlunta. [9.71] Kuma mummunai maza da mummunai mãtã sãshensu majiɓincin sãshe ne, sunã umurni da alhħri(1) kuma sunã hani daga abin da bã a so, kuma sunã tsayar da salla, kuma sunã bãyar da zakka, kuma sunãɗã´a ga Allah da ManzonSa. Waɗannan Allah zai yi musu rahama. Lalle Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima. [9.72] Kuma Allah Yã yi wa´adi ga mummunai maza da mummunai mãtã da gidãjen Aljanna ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwamã a cikinsu, da wurãren zama mãsu dãɗi a cikin gidãjen Aljannar. Kuma yarda daga Allah ce mafi girma. Wancan shi ne babban rabo, mai girma. [9.73] Ya kai Annabi! Ka yãƙi kãfirai da munãfukai kuma ka tsaurara a kansu. Kuma matattararsu Jahannama ce. Tir da ta zama makõmar! [9.74] Sunã rantsuwa da Allah, ba su faɗa ba, alhãli kuwa lalle ne, haƙĩƙa, sun faɗi kalmar kãfirci, kuma; sun kãfirta a bãyan musuluntarsu, kuma sun yi himma ga abin da ba su sãmu ba. Kuma ba su zargi kõme ba fãce dõmin Allah da ManzonSa Ya wadãtar da su daga falalarSa. To, idan sun tũba zai kasance mafi alhħri gare su,kuma idan sun jũya bãya, Allah zaiazabtã su da azãba mai raɗaɗi a cikin dũniya da Lãhira, kuma bã su da wani masõyi kõ wani mataimaki a cikin kasa. [9.75] Kuma daga cikinsu akwai wadɗanda suka yi wa Allah alkawari, "Lalle ne idan ya kãwo mana daga falalarSa, haƙĩƙa, munãbãyar da sadaka, kuma lalle ne munã kasancħwa, daga sãlihai." [9.76] To, a lõkacin da Ya bã su daga falalarSa, sai suka yi rõwa da shi, kuma suka jũya bãya sunã mãsu bijirħwa, [9.77] Sai Ya biyar musu da munãfunci a cikin zukatansu har zuwa ga Rãnar da suke haɗuwa da Shi sabõda sãɓã wa Allah a abin da suka yi Masa alkawari, kuma sabõda abin da suka kasance sunã yi na ƙarya. [9.78] Shin, ba su sani ba cħwa lalle ne Allah Yanã sanin asĩrinsuda gãnawarsu, kuma lalle Allah ne Masanin abũbuwan fake? [9.79] Waɗanda suke aibanta mãsu yin alhħri daga mummunaia cikin dũkiyõyin sadaka, da waɗanda ba su sãmu fãce iyãkar ƙõƙarinsu, sai sanã yi musu izgili. Allah Yanã yin izgili gare su. Kuma sunã da azãba mai raɗaɗi. [9.80] Kõ kã nħma musu gãfara ko ba ka nħma musu ba, idan ka nħma musu gãfara sau saba´in, to, Allah bã zai gãfarta musu ba. Sabõda sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne fãsiƙai. [9.81] Waɗanda aka bari sun yi farin ciki da zamansu a bãyan Manzon Allah, kuma suka ƙi su yi jihãdi da dũkiyõyinsu da rãyukansu a cikin hanyar Allah, kuma suka ce: "Kada ku fita zuwa yãƙi a cikin zãfi."Ka ce: "Wutar Jahannama ce mafi tsanlnin zãfi." Dã sun kasance sunã fahimta! [9.82] Sabõda haka su yi dãriya kaɗan, kuma su yi kũkada yawa a kan sãkamako ga abin da suka kasance sunã tsirfatãwa. [9.83] To, idan Allah Ya mayar da kai zuwa ga wata ƙungiyã daga gare su sa´an nan suka nħme ka izni dõmin su fita, to, ka ce: "Bã zã ku fita tãre da nĩ ba har abada,kuma bã zã ku yi yãƙi tãre da nĩ ba a kan wani maƙiyi. Lalle ne kũ, kun yarda da zama a farkon lõkaci, sai ku zauna tãre da mãtã mãsu zaman gida." [9.84] Kuma kada ka yi salla a kan kõwa daga cikinsu wanda ya mutu, har abada, kuma kada ka tsaya a kan kabarinsa. Lalle ne sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa, kuma sun mutu alhãli kuwa sunã fãsiƙai. [9.85] Kuma kada dũkiyõyinsu da ɗiyansu su bã ka sha´awa. Abin sani kawai, Allah Yanã nufin Ya yi musu azãba da su a cikin dũniya, kuma rãyukansu su fita alhãli kuwa sunã kãfirai. [9.86] Kuma idan aka saukar da wata sũra cħwa; Ku yi ĩmãni da Allah kuma ku yi jihãdi tãre da ManzionSa. Sai mawadãta daga gare su su nħmi izninka, kuma su ce: Ka bar mu mu kasance tãre da mazauna. [9.87] Sun yarda da su kasance tãre da mãtã mãsu zama (a cikin gidãje). Kuma aka rufe a kan zukãtansu, sabõda haka, sũ, bã su fahimta. [9.88] Amma Manzon Allah da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sun yi jihãdi da dũkiyõyinsu da rãyukansu. Kuma waɗannan sunã da ayyukan alhħri, kuma waɗannan sũ ne mãsu cin nasara. [9.89] Allah yã yi musu tattalin gidãjen Aljanna, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwamã a cikinsu. Wancan ne babban rabo mai girma. [9.90] Kuma mãsu uzuri daga ƙauyãwa zuka zo dõmin a yi musu izini, kuma waɗanda suka yi wa Allah da ManzonSa ƙarya, suka yi zamansu. wata azãba mai raɗaɗi zã ta sãmi waɗanda suka kãfirta daga gare su. [9.91] Bãbu laifi a kan maraunana kuma haka majinyata, kuma bãbu laifi a kan waɗanda bã su sãmun abin da suke ciyarwa idan sun yi nasĩha(1) ga Allah da ManzonSa. Kuma bãbu wani laifi a kan mãsu kyautatãwa. Kuma Allah ne Mai gãfara, Mai tausayi. [9.92] Kuma bãbu (laifi) a kan waɗanda idan sun je maka dõmin ka ɗauke su ka ce: "Bã ni da abin da nake ɗaukar ku a kansa," suka jũya alhãli kuwa idãnunsu sunã zubar da hawãye dõmin baƙin ciki cħwa ba su sãmi abin da suke ciyarwa ba. [9.93] Abin sani kawai, laifi Yanã a kan waɗanda suke nħman izininka alhãli kuwa sũ mawadãta ne.Sun yarda su kasance tãre da mãtã mamaya (gidãje), kuma Allah Yã danne a kan zukãtansu, dõmin haka sũ, bã su gãnħwa. [9.94] Sunã kãwo uzurinsu zuwa gare ku idan kun kõma zuwa gare su Ka ce: "Kada ku kãwo wani uzuri, bã zã mu amince muku ba. Haƙĩƙa, Allah Yã bã mu lãbãri daga lãbãrunku, Allah zai ga aikinku kuma ManzonSa (zai gani). Sa´an nan kuma a mayar da ku zuwa ga Masanin gaibi da bayyane, sai Ya bã ku lãbarin abin da kuka kasance kunã aikatãwa." [9.95] Zã su yi rantsuwa da Allah a gare ku idan kun jũya zuwa gare su, dõmin ku kau da kai daga gare su. To, ku kau da kai daga gare su don kõ sũ ƙarantã ne, kuma Jahannama ce matattararsu bisa ga sãkamakon abin da suka kasance sunã tsirfatãwa. [9.96] Sunã rantsuwã gare ku dõmin ku yarda da su. To, idan kun yarda da su, to, lalle ne Allah bã shi yarda da mutãne fãsiƙai. [9.97] Ƙauyãwã ne mafi tsananin(1) kãfirci da munãfinci, kuma sũne mafi kamanta ga, rashin sanin haddõjin abin da Allah Ya saukar a kan ManzonSa. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima. [9.98] Kuma daga ƙauyãwã akwai waɗanda(2) suke riƙon abin da suke ciyarwa a kan tãra ce, kuma sunã saurãron aukuwar masĩfa a gare ku, aukuwar mummunar masĩfa ta tabbata a kansu. Kuma Allah ne Mai ji, Masani. [9.99] Kuma daga ƙauyãwã akawi waɗanda suke yin ĩmanida Allah da Rãnar Lãhira, kuma sunã riƙon abin da suke ciyarwa (tamkar) waɗansu ibãdõdin nħman kusanta ne a wurin Allah da addu´õ´in ManzonSa. To, lalle ne ita (ciyarwar nan) ibãdar nħman kusanta ce a gare su. Allah zai shigar da su a cikin RahamarSa. Lalle Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai. [9.100] Kuma mãsu tsħrħwa(1) na farko daga Muhãjirina da Ansar da waɗanda suka bi su da kyautatãwa, Allah Ya yarda daga gare su su kuma sun yarda daga gare Shi, kuma Ya yi mãsu tattalin gidãjen Aljanna; Ƙõramu sunã gudãna a ƙarƙashinsu, suna madawwamã a cikinsu har abada. Wancan ne babban rabo mai girma. [9.101] Kuma daga waɗanda suke a għfenku daga ƙauyãwa akwai munãfukai,(2) haka kuma daga mutãnen Madnĩa. Sun gõge a kan munãfunci, bã ka sanin su, Mũ ne Muke sanin su. zã Mu yi musu azãba sau biyu, sa´an nan a mayar da su zuwa ga azãba mai girma. [9.102] Kuma da waɗansu, sun yi furuci(3) da laifinsu, sun haɗa aiki na ƙwarai da wani mummuna. Akwai tsammãnin Allah Ya karɓi tũba a kansu. Lallai Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai. [9.103] Ka karɓi sadaka daga dũkiyõyinsu kana tsarkake su, kuma kana tabbatar da kirkinsu da ita. Kuma ka yi musu addu´a. Lallai addu´õ´inKa natsuwã ne a gare su. Kuma Allah ne Mai ji, Masani. [9.104] Shin, ba su sani ba cħwa lallai Allah, ne Yake karɓar tũbã daga bãyinSa, kuma Yanã karɓar sadakõkinsu, kuma lalle Allah ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai? [9.105] Kuma ka ce: "Ku yi aiki, sa´an nan Allah zai ga aikinku, da ManzonSa da Muminai kuma zã a mayar da ku zuwa ga masanin fake da bayyane, sa´an nan Ya bã ku lãbãri ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa." [9.106] Kuma da waɗansu waɗanda(4) aka jinkirtar ga umurnin Allah, kõ dai Ya yi musu azãba kõ kuma Ya karɓi tũba a kansu.Kuma Allah ne Masani, Mai hikima. [9.107] Kuma waɗanda(1) suka riƙi wani masallãci dõmin cũta da kãfirci da nħman rarrabħwa a tsakãnin muminai da fakħwã ga taimakon wanda ya yãƙi Allah da ManzonSa daga gabãni, kuma haƙĩƙa sunã yin rantsuwa cħwa, "Ba mu yi nufin kõmai ba fãce alhħri", alhãli kuwa Allah Yanã yin shaida cħwa,su, haƙĩƙa, maƙaryata ne. [9.108] Kada ka tsaya a cikinsa har abada. Lalle ne, Masallaci wanda aka yi harsãshinsa a kan taƙawa tun farkon yini, shĩ ne mafi cancantar ka tsaya a cikinsa. A cikinsa akwai waɗansu maza sunã son su tsarkaka. (2) Kuma Allah Yanã son mãsu nħman tsarkakuwa. [9.109] Shin, wanda ya sanya harsãshin gininsa a kan taƙawa daga Allah da yarda, shi ne mafi alhħri kõ kuwa wanda ya sanya harsãshin gininsa a kan gãɓar rãmi mai tusgãwa? Sai ya rũsa da shi a cikin wutar Jahannama. Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai. [9.110] Gininsu, wanda suka gina, bã zai gushe ba Yanã abin shakka a cikin zukãtansu fãce idan zukãtansu sun yanyanke. Kuma Allah ne Masani, Mai Hikima. [9.111] Lalle ne, Allah Ya saya(3) daga mummunai, rãyukansu da dũkiyõyinsu, da cħwa sunã da Aljanna, sunã yin yãƙi a cikin hanyar Allah, sabõda haka sunã kashħwa anã kashħ su. (Allah Yã yi)wa´adi a kanSa, tabbace a cikin Attaura da Linjĩla da Alƙur´ãni. Kuma wãne ne mafi cikãwa da alkawarinsa daga Allah? Sabõda haka ku yi bushãra da cinikinku wanda kuka ƙulla da Shi. Kuma wancan shi ne babban rabo, mai girma. [9.112] Mãsu(1) tũba, mãsu bautãwa, mãsu gõdħwa, mãsu tafiya, mãsu ruku´i, mãsu sujada mãsu umurni da alhħri da mãsu hani daga abin da aka ƙi da mãsu tsarħwã ga iyãkõkin Allah. Kuma ka bãyar da bushãra ga muminai. [9.113] Bã ya kasancħwa(2) ga Annabi da waɗanda suka yi ĩmãni, su yi istigifãri ga mushirikai, kuma kõ dã sun kasance ma´abũta zumunta ne daga bãyan sun bayyana a gare su, cħwa lalle ne, sũ, ´yan Jahĩm ne. [9.114] Kuma istigifãrin Ibrãhĩm ga ubansa bai kasance ba fãce sabõda wani wa´adi ne da ya ƙulla alƙawarinsa da shi, sa´an nan a lõkacin da ya bayyana a gare shi (Ibrãhĩm) cħwa lalle ne shĩ (ubansa) maƙiyi ne ga Allah, sai ya barranta daga gare shi. Lalle ne Ibrahim, haƙĩƙa, mai yawan addu´a ne, mai haƙuri. [9.115] Kuma Allah bai kasance mai ɓatar da mutãne a bãyan Yã shiryar da su ba, sai Ya bayyanã musu abin da zã su yi taƙawa da shi. Lalle ne Allah, ga kõme, Masani ne. [9.116] Lalle ne Allah Yanã(3) da mulkin sammai da ƙasa, Yanã rãyarwa kuma Yanã matarwa. Kuma bã ku da wani masõyi, kuma bã ku da mataimaki, baicin Allah. [9.117] Lalle ne, haƙĩƙa, Allah Ya karɓi tũbar Annabi da(4) Muh?jirĩna da Ans?r waɗanda suka bĩ shi, a cikin s?´ar tsanani, daga b?ya zuk?tan wani ɓangare daga gare su sun yi kusa su karkata, sa´an nan ( Allah) Ya karɓi tũbarsu. Lalle, Shĩ ne Mai tausayi, Mai jin ƙai gare su. [9.118] Kuma (Allah) Yã karɓi tũba a kan ukun(1) nan waɗanda aka jinkirtar har ƙasa da yalwarta ta yi ƙunci a kansu, kuma rãyukansu suka yi ƙunci a kansu, kuma suka yi zaton bãbu wata mafakã daga Allah fãce (kõmãwa) zuwa gare Shi. Sa´an nan Allah Ya karɓi tũbarsu, dõmin su tabbata a kan tũba. Lalle Allah ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai. [9.119] Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, kuma ku kasance tãre da mãsu gaskiya. [9.120] Bã ya kasancħwa(2) ga mutãnen Madĩna da wanda yake a għfensu, daga ƙauyãwã, su sãba daga bin Manzon Allah, kuma kada su yi gudu da rãyukansu daga ransa. Wancan, sabõda ƙishirwa bã ta sãmun su, haka kuma wata wahala, haka kuma wata yunwa, a cikin hanyar Allah, kuma bã su tãkin wani matãki wanda yake takaitar da kãfirai kuma bã su sãmun wani sãmu daga maƙiyi fãce an rubuta musu da shi, lãdar aiki na ƙwarai. Lallai ne Allah bã Ya tõzarta lãdar mãsu kyautatãwa. [9.121] Kuma bã su ciyar da wata ciyarwa, ƙarama kõ babba, kuma bã su kħta wani rafi sai an rubutã musu, dõmin Allah Ya sãka musu da mafi kyãwon abin da suka kasance sunã aikatãwa. [9.122] Kuma bã ya kasancħwã ga muminai su fita zuwa yãƙi gabã ɗaya.(3) Sabõda haka, don me ne wata jama´a daga kowane ɓangare daga gare su ba ta fita (zuwa nħman ilimi ba) dõmin su nħmi ilimi ga fahimtar addĩni kuma dõmin su yi gargaɗi ga mutãnensu idan sun kõma zuwa gare su, tsammãninsu, sunã yin sauna? [9.123] Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yãƙi waɗanda suke kusantar(1) ku daga kãfirai. Kuma su sami tsanani daga gare ku. Kuma ku sani cħwa Allah Yanã tãre da mãsu taƙawa. [9.124] Kuma idan aka saukar(2) da wata sũra, to, daga gare su akwai waɗanda suke cħwa: "Wãne ne a cikinku wannan sũra ta ƙãra masa ĩmãni?" To amma waɗanda suka yi ĩmãni, to, ta ƙara musu imani, kuma sũ, sunã yin bushãra (da ita). [9.125] Amma kuma waɗanda suke a cikin zukãtansu akwai cũta, to, tã ƙãra musu ƙazanta zuwa ga ƙazantarsu, kuma su mutu alhãlin kuwa sunã kãfirai. [9.126] Shin, bã su ganin cħwa anã fitinar su a cikin kõwace shħkara: sau ɗaya kõ kuwa sau biyu, sa´an nan kuma bã su tũba, kuma ba su zama sunã tunãni ba? [9.127] "Kuma idan haƙĩƙa, aka saukar da wata sũra, sai sãshensu ya yi dũbi zuwa ga wani sãshe, (su ce): "Shin, wani mutum yanã ganin ku?" Sa´an nan kuma sai su jũya. Allah Ya jũyar da zukãtansu, dõmin, haƙĩƙa sũ mutãne ne, bã su fahimta. [9.128] Lalle ne, haƙĩƙa, Manzo(3) daga cikinku yã je muku. Abin da kuka wahala da shi mai nauyi ne a kansa. Mai kwaɗayi ne sabõda ku. Ga muminai Mai tausayi ne, Mai jin ƙai. [9.129] To, idan sun jũya, sai ka ce: Ma´ishĩna Allah ne. Bãbu abin bautãwa fãce shi. A gare Shi nake dõgara. Kuma Shi ne Ubangijin Al´arshi mai girma. @YUNUS Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [10.1] A. L̃. R. Waɗancan ãyõyin littãfi ne kyautatacce. [10.2] Shin, yã zama abin mãmaki ga mutãne dõmin Mun yi wahayi zuwa ga wani namiji daga gare su cħwa, "Ka yi gargaɗi ga mutãne kuma ka yi bushãra ga waɗanda suka yi ĩmãni da cħwa: Lalle ne sunã da abin gabãtarwar gaskiya a wurin Ubangijinsu."Kãfirai suka ce: "Lalle ne wannan, haƙĩƙa, masihirci ne bayyananne." [10.3] Lalle Allah ne Ubangijinku wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwãna shida, sa´an nan kuma Ya daidaita a kan Al´arshi Yanã gudãnar da al´amari. Bãbu wani macħci fãce a bayan izninSa. Wannan ne Allah, Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Shin fa, ba ku tunãni? [10.4] Zuwa gare Shi makõmarku take gabã ɗaya, wa´adin Allah gaskiya ne. Haƙĩƙa, Shi ne Yake fara halitta, sa´an nan kuma Ya mayar da ita dõmin Ya sãka wa waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai da ãdalci, kuma waɗanda suka kãfirta sunã da abin sha daga ruwan zãfi, da azãba mai raɗaɗi, sabõda abin da suka kasance sunã yi na kãfirci. [10.5] Shĩ ne wanda Ya sanya muku rãnã, babban haske, da watã mai haske, kuma Ya ƙaddara shi ga Manzilõli, dõmin ku san ƙidãyar shħkaru da lissãfi. Allah bai halitta wannan ba, fãce da gaskiya, Yanã bayyana ãyõyi daki-daki dõmin mutãne waɗanda suke sani. [10.6] Lalle ne a cikin sãɓãwar dare da yini, da abin da Allah Ya halitta a cikin sammai da ƙasa, haƙĩƙa akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin taƙawa. [10.7] Lalle ne waɗanda ba su ƙaunar gamuwa da Mũ, kuma suka yarda da rãyuwar dũniya kuma suka natsu da ita, da waɗanda suke gafalallu ne daga ãyõyinMu, [10.8] Waɗannan matattãrarsu Jahannama ce sabõda abin da suka kasance sunã tsirfãtawa. [10.9] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, Ubangijinsu Yanã shiryar da su sabõda ĩmãninsu, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, a cikin gidãjen Aljannar ni´ima. [10.10] Kiransu a cikinta, "TsarkinKa yã Allah!" Kuma gaisuwarsu a cikinta,"Salãmun", kuma ƙarshen kiransu, cħwa, "Gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu." [10.11] Kuma dã Allah Yana gaggãwa ga mutãne da sharri kamar yadda Yake gaggauta musu da alhħri, haƙĩƙa dã an hukunta ajalinsu zuwa gare su. Sabõda haka Munã barin waɗanda ba su ƙaunar gamuwa da Mu, a cikin kangararsu sunã ta ɗimuwa. [10.12] Kuma idan cũta ta shãfi mutum, sai ya kirãye Mu, yanã (kwance) ga sãshensa kõ kuwa zaune, kõ kuwa a tsaye. To, a lõkacin, da Muka kuranye cũtar daga gare shi, sai ya shũɗe kamar ɗai bai kirãye Mu ba zuwa ga wata cũta wadda ta shãfe shi. Kamar wannan ne aka ƙawãta ga maɓannata, abin da suka kasance sunã aikatãwa. [10.13] Kuma, haƙĩƙa, Mun halakar da al´ummomi daga gabãninku, a lõkacin da suka yi zãlunci, kuma manzanninsu suka jħ musu da hujjõji bayyanannu, amma ba su kasance sunã ĩmãni ba. Kamar wannan ne, Muke sãkãwa ga mutãne mãsu laifi. [10.14] Sa´an nan kuma Muka sanya ku mãsu mayħwa a cikin ƙasa daga bãyansu, dõmin Mu ga yãya kuke aikatãwa. [10.15] Kuma idan anã karatun ãyõyĩnMu bayyanannu a kansu, sai waɗanda bã su ƙaunar gamuwa da Mu, su ce: "Ka zo da wani Alƙur´ãni, wanin wannan, ko kuwa ka musunyã shi."(1) Ka ce: "Bã ya kasancħwa a gare ni in musanyã shi da kaina. Bã ni biyar kõme fãce abin da aka yiwo wahayi zuwa gare ni. Kuma, haƙĩƙa ni inã tsõro idan na sãɓã wa Ubangijina, ga azãbar wani yini mai girma." [10.16] Ka ce: "Dã Allah Ya so dã ban karanta shi ba a kanku, kuma dã ban sanar da kũ ba gameda shi, dõmin lalle ne nã zauna a cikinku a zãmani mai tsawo daga gabãnin (fãra saukar) sa. Shin fa, bã ku hankalta?" [10.17] "Sabõda haka wãne ne mafi Zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ƙaryata ãyõyinSa? Haƙĩƙa, mãsu laifi bã su cin nasara!" [10.18] Kuma sunã bautã wa, baicin Allah, abin da bã ya cũtar dasu kuma bã ya amfãninsu, kuma sunã cħwa: "Waɗannan ne macħtanmu a wurin Allah."Ka ce: "Shin, kunã bai wa Allah lãbãri ne, ga abin da bai sani ba, a cikin sammai ko a cikin ƙasa? TsarkinSa ya tabbata kuma Yã ɗaukaka daga abin da duk suke yin shirki da Shi." [10.19] Kuma mutãne ba su kasance ba fãce al´umma guda, sa´an nan kuma suka sãɓã wa jũna, kuma ba dõmin wata kalma ba wadda ta gabãta daga Ubangijinka, dã an yi hukunci a tsakãninsu a kan abin da yake a cikinsa suke sãɓã wa jũna. [10.20] Kuma sunã cħwa: "Don me ba a saukar da wata ãyã ba a gare shi, daga Ubangijinsa?" To, ka ce: "Abin sani kawai, gaibi ga Allah yake. Sai ku yi jira. Lalle ne nĩ, tãre da ku, inã daga mãsu jira." [10.21] Kuma idan Muka ɗanɗanã wa mutãne wata rahama, a bãyan wata cũta tã shãfe su, sai gã su da mãkirci a cikin ãyõyinMu. Ka ce: "Allah ne mafi gaggãwar (sakamakon) mãkirci." Lalle ne ManzanninMu sunã rubũta abin da kuke yi na mãkirci. [10.22] Shĩ ne wanda Yake tafiyar da ku a cikin tudu da (kuma) tħku, sai idan kun kasance a cikin jirãge, su gudãna tãre da su da iska mai dãɗi, kuma su yi farin ciki da ita, sai wata gũguwa ta je wa jirãgen, kuma tãguwar ruwa ta jħ musu daga kõwane wuri, kuma su tabbata cħwa sũ, an kħwaye su, sai su kirãyi Allah, sunã mãsu tsarkake addini gare Shi, (sunã cħwa): Lalle ne idan Ka kuɓutar da mu daga wannan, haƙĩƙa munã kasancħwa daga mãsu gõdiya. [10.23] To, a lõkacin da Ya kuɓutar da su, sai, gã su sunã zãlunci a cikin ƙasa, bã da wanĩ hakki ba. Yã ku mutãne! Abin sani kawai, zãluncinku a kanku yake, a bisa rãyuwar dũniya. Sa´an nan kuma zuwa gare Mu makõmarku take, sa´an nan Mu bã ku lãbãri game da abin da kuka kasance kunã aikatãwa, [10.24] Abin sani kawai, misãlin rãyuwar dũniya kamar ruwa ne Muka saukar da shi daga sama, sa´an nan tsiron ƙasa ya garwaya da shi. Daga abin da mutãne da dabbõbi suke ci, har idan ƙasa ta riƙi zinãriyarta kuma ta yi ƙawa, kuma mutãnenta suka zaci cħwa sũ ne mãsu ĩkon yi a kanta, sai umurninMu ya je mata da dare kõ kuma da rãna, sai Mu maishħta girbabba kamar ba ta wadãta ba a jiya. Kamar wannan ne Muke rarrabe ãyõyi, daki-daki, ga mutãne waɗanda suke tunãni. [10.25] Kuma Allah Yanã kira zuwa ga gidan aminci, kuma, Yanã shiryar da wanda Yake so zuwa ga tafarki madaidaici. [10.26] Waɗanda suka kyautata yi, sunã da abu mai kyãwo kuma da ƙari,(1) wata ƙũra bã ta rufe fuskõkinsu, kuma haka wani ƙasƙanci. Waɗancan ne abokan Aljanna, sunã madawwama a cikinta. [10.27] Kuma waɗanda suka yi tsirfar mũnanan ayyuka, sakamakon mummuna da kamarsa yake, kuma ƙasƙanci yanã rufe su. Bã su da wani matsari daga Allah, kamar an rufe fuskokinsu da guntãyen ƙirãruwa daga dare mai duhu. Waɗannan ne abõkan wuta, sunã madawwama a cikinta. [10.28] Kuma a rãnar da Muke tãra su gabã ɗaya, sa´an nan kuma Mu ce wa waɗanda suka yi shirki, "Ku kãma matsayinku, kũ da abũbuwan shirkĩnku." Sa´an nan Mu rarrabe a tsakãninsu, kuma abũbuwan shirkinsu su ce: "Bã mũ kuka kasance kunã bauta wa ba." [10.29] "To, kuma Allah Yã isa zama shaida a tsakãninmu da tsakãninku. Haƙĩƙa mun kasance ba mu san kõme ba na bautãwarku a gare mu!" [10.30] A can ne kõwane rai yake jarraba abin da ya bãyar bãshi, kuma aka mayar da su zuwa ga Allah, Majiɓincinsu Tabbatacce kuma, abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa ya ɓace musu. [10.31] Ka ce: "Wãne ne Yake azurtã ku daga sama da ƙasa? Shin kõ kuma Wãne ne Yake mallakar jĩ da ganĩ, kuma Wãne ne Yake fitar da mai rai daga mamaci, kuma Ya fitar da mamaci daga mai rai, Kuma Wãne ne Yake shirya al´amari?" To, zã su ce: "Allah ne." To, ka ce: "Shin fa, bã zã ku yi taƙawa ba?" [10.32] To, Wancan ne Allah, Ubangijinku Tabbatacce. To, mħne ne a bãyan gaskiya fãce ɓãta? To, yãya ake karkatar da ku? [10.33] Kamar wancan ne kalmar Ubangijinka, ta tabbata a kan waɗanda suka yi fãsiƙanci, cħwa haƙĩƙa sũ, bã zã su yi ĩmãni ba. [10.34] Ka ce: "Shin, daga abũbuwan shirkinku akwai wanda yake fãra halitta, sa´an nan kuma ya mayar da ita?" Ka ce: "Allah ne Yake fãra halitta, sa´an nan kuma Ya mayar da ita. To, yãyã ake jũyar da ku?" [10.35] Ka ce: "Shin, daga abũbuwan shirkinku akwai wanda yake shiryarwa zuwa ga gaskiya?" Ka ce: "Allah ne Yake shiryarwa zuwa ga gaskiya. Shin fa, wanda Yake shiryarwa ne mafi cancantar a bi Shi, ko kuwa wanda bã ya shiryarwa fãce dai a shiryar da shi? To, mħne ne a gare ku? Yãya kuke yin hukunci?" [10.36] Kuma mafi yawansu bã su biyar kõme fãce zato. Lalle ne zato bã ya wadãtar da kõme daga gaskiya. Lalle Allah ne Masani ga abin da suke aikatãwa. [10.37] Kuma wannan Alƙur´ãni bai kasance ga a ƙirƙira shi ba daga wanin Allah, kuma amma shi gaskatawar wannan ne da yake a gabãninsa da bayãnin hukuncin littãffan Allah, Bãbu shakka a cikinsa, daga Ubangijin halittu yake. [10.38] Kõ sunã cħwa, "Yã ƙirƙira shi?" Ka ce: "Ku zo da sũra guda misãlinsa, kuma ku kirãyi wanda kuka iya duka, baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya." [10.39] ôa, sun ƙaryata game da abin da ba su kħwaye da saninsa ba, kuma fassararsa ba ta riga ta jħ musu ba. Kamar waɗancan ne waɗanda suke a gabãninsu. Sai ka dũba, yãya ãƙibar azzãlumai ta kasance? [10.40] Kuma daga cikinsu akwai wanda yake yin ĩmãni da Shi, kuma daga cikinsu akwai wanda bã ya yin ĩmãni da Shi. Kuma Ubangijinka ne Mafi sani ga maɓarnata. [10.41] Kuma idan sun ƙaryata ka, to, ka ce: "Inã da aikĩna kuma kunã da aikinku, kũ kuɓutattu ne daga abin da nake aikatãwa kuma ni kuɓutacce ne daga abin da kuke aikatãwa." [10.42] Kuma daga cikinsu akwai waɗanda suke saurare zuwa gare ka. Shin fa, kai kana jiyar da kurma, kuma kõ dã sun kasance bã su hankalta? [10.43] Kuma daga cikinsu akwai wanda yake tsõkaci zuwa gare ka. Shin fa, kai kana shiryar da makãfi, kuma kõ dã sun kasance bã su gani? [10.44] Lalle ne Allah ba Ya zãluntar mutãne da kõme, amma mutãnen ne ke zãluntar kansu. [10.45] Kuma rãnar da Yake tãra su, kamar ba su zauna ba fãce sa´a guda daga yini. Sunã gãne jũna a tsakãninsu. Haƙĩƙa, waɗanda suka ƙaryata game da gamuwa da Allah sun yi hasãra. Kuma ba su kasance mãsu shiryuwa ba. [10.46] Kuma imma dai, haƙĩƙa, Mu nũna maka sãshen abin da Muke yi musu alkawari, kõ kuwa Mu karɓi ranka, to, zuwa gare Mu makõmarsu take. Sa´an nan kuma Allah ne shaida a kan abin da suke aikatãwa. [10.47] Kuma ga kõwace al´umma akwai Manzo.(1) Sa´an nan idan Manzonsu ya je, sai a yi hukunci a tsakãninsu da ãdalci, kuma sũ, bã a zãluntar su. [10.48] Kuma sunã cħwa, "A yaushe wannan wa´adi zai auku, idan kun kasance mãsu gaskiya?" [10.49] Ka ce: "Ba na mallaka wa kaina wata cũta, haka kuma wani amfãni, sai abin da Allah Ya so. Ga kõwace al´umma akwai ajali, idan ajalinsu ya zo, to, bã zã su yi jinkiri daga gare shi ba, kõ dã sã´ã guda, kuma bã zã su gabãta ba." [10.50] Ka ce: "Shin, kun gani, idan azãbarSa ta zo muku da dare ko da rãna? Mħne ne daga gare shi mãsu laifi suke nħman gaggãwarsa?" [10.51] Shin sa´an nan kuma idan har ya auku, kun yi ĩmãni da shi? Ashe? Yanzu kuwa, alhãli kun kasance game da shi kunã nħman gaggãwar aukuwarsa? [10.52] Sa´an nan kuma aka ce ga waɗanda suka yi zãlunci, "Ku ɗanɗani azãbar dawwama! Shin, anã sãka muku fãce da abin da kuka kasance kuna aikatãwa?" [10.53] Kuma sunã tambayar ka: Shin gaskiya ne? Ka ce: "Ĩ, ina rantsuwa da Ubangijĩna. Lalle gaskiya ne, kuma ba ku zama mãsu buwãya ba." [10.54] Kuma dã kõwane rai wanda ya yi zãlunci yã mallaki duka abin da yake a cikin ƙasa, to, dã yã yi fansa da shi. Kuma suka dinga nadãma a lõkacin da suka ga azãba. Sa´an nan aka yi hukunci a tsakãninsu da ãdalci, kuma bã zã a zãlunce su ba. [10.55] To! Haƙĩƙa Allah Ya mallaki abin da yake a cikin sammai da ƙasa. To! Haƙĩƙa wa´adin Allah gaskiya ne. Amma kuma mafi yawansu ba su sani ba. [10.56] Shi ne Yake rãyarwa kuma Yake matarwa. Kuma zuwa gare Shi ne ake mayar da ku. [10.57] Ya ku mutãne! Lalle wa´azi yã jħ muku daga Ubangijinku, da waraka ga abin da yake a cikin ƙirãza, da shiriya da rahama ga muminai. [10.58] Ka ce: "Da falalar Allah da rahamarSa. Sai su yi farin ciki da wannan." Shĩ ne mafi alhħri daga abin da suke tãrãwa. [10.59] Ka ce: "Shin, kun ga abin da Allah Ya saukar sabõda ku na arziki, sai kuka sanya hukuncin haramci da halacci a gare shi?" Ka ce: "Shin, Allah ne Ya yi muku izni, ko ga Allah kuke ƙirƙirãwar ƙarya?" [10.60] Kuma mħne ne zaton waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, a Rãnar Ƙiyãma? Lalle haƙĩƙa, Allah Ma, abũcin falala ne a kan mutãne, amma kuma mafi yawansu bã su gõdħwa. [10.61] Kuma ba ka kasance a cikin wani sha´ani ba, kuma ba ka karanta wani abin karatu daga gare shi ba, kuma ba ku aikata wani aiki ba, fãce Mun kasance Halarce a lõkacin da kuke zubuwa a cikinsa. Kuma wani ma´aunin zarra bã zai yi nĩsa ba daga Ubangijinka a cikin ƙasa, haka kuma a cikin sama, kuma bãbu wanda yake mafi ƙaranci daga haka, kuma bãbu mafi girma, fãce yana a cikin littãfi bayyananne. [10.62] To, Lalle ne masõyan(1) Allah bãbu tsõro a kansu, kuma bã zã su kasance sunã yin baƙin ciki ba. [10.63] Waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka kasance sunã yin taƙawa. [10.64] Sunã da bushãra a cikin rãyuwar dũniya da ta Lãhira.Bãbu musanyãwa ga kalmõmin Allah. Wancan shi ne babban rabo mai girma, [10.65] Kada maganarsu(2) ta sanya ka a cikin baƙin ciki. Lalle ne alfarma ga Allah take gaba ɗaya. Shi ne Mai jĩ, Masani. [10.66] To! Haƙĩƙa Allah Yanã da mulkin wanda ke a cikin sammai da wanda ke a cikin ƙasa kuma waɗanda suke kiran wanin Allah, bã su biyar waɗansu abõkan tarħwa (ga Allah a MulkinSa). Bã su biyar kõme fãce zato. Kuma ba su zama ba fãce sunã ƙiri faɗi kawai. [10.67] Shĩ ne wanda Ya sanya muku dare, dõmin ku natsu a cikinsa, da yini mai sanya a yi gani. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda sukħ ji. [10.68] Suka ce: "Allah Ya riƙi ɗa." Tsarkinsa yã tabbata! Shi ne wadãtacce Yanã da mallakar abin da yake, a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, A wurinku bãbu wani dalĩli game da wannan! Shin, kunã faɗar abin da ba ku sani ba game da Allah? [10.69] Ka ce: "Haƙĩƙa waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, bã zã su ci nasara ba." [10.70] Jin dãɗi ne a cikin dũniya, sa´an nan kuma makõmarsu zuwa gare Mu take, sa´an nan Mu ɗanɗana musu azãba mai tsanani sabõda abin da suka kasance sunã yi na kãfirci. [10.71] Kuma ka karanta musu lãbãrin Nũhu, a lõkacin da ya ce wa mutãnensa, "Ya mutãnħna! Idan matsayĩna da tunãtarwata ame da ãyõyin Allah sun kasance sun yi nauyi a kanku, to, ga Allah na dõgara. Sai ku tãra al´amarinku, kũ da abũbuwan shirkinku, sa´annan kuma kada al´amarinku ya kasance rufaffe a kanku, sa´an nan kuma ku kashe ni, kada ku yi mini jinkiri." [10.72] "Kuma idan kuka jũya bãya, to, ban tambaye ku wata ijãra ba. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Allah, kuma an umurce ni da in kasance daga mãsu sallamãwa."(1) [10.73] Sai suka ƙaryata shi, sa´an nan Muka kuɓutar da shi da wanda yake tãre da shi, a cikin jirgi, kuma Muka sanya su mãsu mayħwa, kuma Muka nutsar da waɗanda suka ƙaryata ãyõyinMu. Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance. [10.74] Sa´an nan kuma Muka aika waɗansu Manzanni daga bãyansa zuwa ga mutãnensu, suka jħmusu da hujjõji bayyanannu, to, ba su kasance zã su yi ĩmãni ba sabõda sun ƙaryata shi a gabani. Kamar wannan ne Muke rufħwa a kan zukãtan mãsu ta´addi. [10.75] Sa´an nan kuma a bãyansu Muka aika Mũsa da Hãrũna zuwa ga Fir´auna da mashãwartansa, tãre da ãyõyinMu. Sai suka kangara kuma sun kasance mutãne mãsu laifi. [10.76] Sa´an nan a lõkacin da gaskiya ta jħ musu daga gare Mu, suka ce: "Wannan haƙĩƙa sihiri ne bayyananne." [10.77] Mũsã ya ce: " Shin, kunã cħwa ga gaskiya a lõkacin data zo muku? Shin, sihiri ne wannan? Lalle masihirci, bã ya cin nasara." [10.78] Suka ce: "Shin, ka zo mana ne dõmin ka jũyar da mu daga abin da muka iske ubanninmu a kansa, kuma girma ya kasance gare ku, ku biyu a cikin ƙasa? Bã zã mu zama mãsu ĩmãni ba sabõda ku." [10.79] Kuma Fir´auna ya ce: "Ku zo mini da dukan masihirci, masani." [10.80] To, a lõkacin da masihirta suka je, Mũsã ya ce musu,"Ku jħfa abin da kuke jħfãwa." [10.81] To, a lõkacin da suka jħfa, Mũsa ya ce: "Abin da kuka zo da shi sihiri ne. Lalle ne Allah zai ɓãta shi. Haƙĩƙa Allah bã Ya gyãra aikin maɓarnata. [10.82] "Kuma Allah Yanã tabbatar da gaskiya da kalmõminSa, kõ dã mãsu laifi sun ƙi." [10.83] Sa´an nan bãbu wanda ya yi ĩmãni da Mũsa fãce zuriya daga mutãnensa, a kan tsõron kada Fir´auna da shũgabanninsu su fitinħ su. Lalle, haƙĩƙa, Fir´auna marinjãyi ne a cikin ƙasa, kuma lalle shĩ haƙĩƙa, yanã daga mãsu ɓarna. [10.84] Kuma Mũsã ya ce: "Yã kũ mutãnena! Idan kun kasance kun yi ĩmãni da Allah, to, a gare Shi sai ku dõgara, idan kun kasance Musulmi." [10.85] Sai suka ce: "Ga Allah muka dõgara. Yã Ubangijinmu! Kada Ka sanyã mu fitina ga mutãne azzãlumai. [10.86] "Kuma Ka kuɓutar da mu dõmin RahamarKa, daga mutãne kãfirai." [10.87] Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã da ɗan´uwansa, cħwa: Kũ biyu, ku zaunar da mutãnenku a Masar a cikin wasu gidãje. Kuma ku sanya gidãjenku su fuskanci Alƙibla(1) , kuma ku tsayar da salla. Kuma ku bãyar da bushãra ga mãsu ĩmãni. [10.88] Sai MũSã ya ce: "Yã Ubangijinmu! Haƙĩƙa Kai ne Ka bai wa Fir´auna da majalisarsa ƙawa da dũkiyõyi a cikin rãyuwar dũniya, yã Ubangijinmu, dõmin su ɓatar (da mutãne) daga hanyarKa. Yã Ubangijinmu! Ka shãfe a kan dũkiyarsu kuma Ka yi ɗauri(2) a kan zukãtansu yadda bã zã su yi ĩmãni ba har su ga azãba mai raɗaɗi." [10.89] (Allah) Yã ce: "Lalle ne an karɓi addu´arku. Sai ku daidaitu kuma kada ku bi hanyar waɗanda ba su sani ba." [10.90] Kuma Muka ƙħtãrar da Banĩ Isrã´ila tħku sai Fir´auna da rundunarsa suka bĩ su bisa ga zãlunci da ƙħtare haddi, har a lõkacin da nutsħwa ta riske shi ya ce: "Nã yi(1) ĩmãni cħwa, haƙĩƙa, bãbu abin bautawa fãce wannan da Banũ Isrã´il suka yi ĩmãni da Shi, kumanĩ, ina daga Musulmi." [10.91] Ashe! A yanzu! Alhãli kuwa, haƙĩƙa ka sãɓa a gabãni, kuma ka kasance daga mãsu ɓarna? [10.92] To, a yau Munã kuɓutar(2) da kai game da jikinka, dõmin ka kasance ãyã ga waɗanda suke a bãyanka. Kuma lalle ne mãsu yawa daga mutãne, haƙĩƙa, gafalallu ne ga ãyõyinMu. [10.93] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun zaunar(3) da Banĩ Isrã´ila mazaunar gaskiya kuma Muka arzũta su daga abũbuwa mãsu dãɗi. Sa´an nan ba su sãɓa ba har ilmi ya jħ musu. Lalle ne Ubangijinka Yanã yin hukunci a tsakãninsu a Rãnar Kiyãma a cikin abin da suka kasance sunã sãɓa wa jũna. [10.94] To, idan ka kasance a cikin shakka daga abin da Muka saukar zuwa gare ka, sai ka tambayi waɗanda suke karatun Littãfi daga gabaninka. Lalle ne, haƙĩƙa, gaskiya tã jħ maka daga Ubangijinka dõmin haka kada ka kasance daga mãsu kõkanto. [10.95] Kuma kada ka kasance daga waɗanda suke ƙaryatãwa game da ãyõyin Allah, har ka kasance daga mãsu hasãra. [10.96] Lalle ne waɗanda kalmar Ubangijinka ta wajaba a kansu, bã zã su yi ĩmãni ba. [10.97] Kuma kõ dã kõwace ãyã ta jħ musu, sai sun ga azãba mai raɗaɗi. [10.98] To, dõmin me wata alƙarya ba ta kasance ta yi(1) ĩmãni ba har ĩmãninta ya amfãne ta, fãce mutãnen Yũnus? A lõkacin da suka yi ĩmãni, Mun janye azãbar wulãkanci daga gare su a cikin rãyuwar dũniya. Kuma Muka jiyar da su dãɗi zuwa wani lõkaci. [10.99] Kuma dã Ubangijinka Ya so, dã waɗanda suke a cikin ƙasa sun yi ĩmãni dukansu gabã ɗaya. Shin, kai kanã tĩlasta mutãne ne har su kasance mãsu ĩmãni? [10.100] Kuma ba ya kasancħwa ga wani rai ya yi ĩmãni fãce da iznin Allah, kuma (Allah) Yanã sanya ƙazanta a kan wa ɗanda bã su yin hankali. [10.101] Ka ce: "Ku dũbi abin da yake cikin sammai da ƙasa."Kuma ãyõyi da gargaɗi bã su wadãtarwa ga mutãne waɗanda bã su yin ĩmãni. [10.102] To, Shin sunã jiran wani abu fãce kamar misãlin kwãnukan waɗanda suka shũɗe daga gabãninsu? Ka ce: "Ku yi jira! Lalle nĩ tãre da ku, inã daga mãsu jira." [10.103] Sa´an nan kuma Munã kuɓutar da manzanninMu da waɗanda suka yi ĩmãni, kamar wannan ne, tabbatacce ne a gare Mu, Mu kuɓutar da mãsu ĩmãni. [10.104] Ka ce: "Yã kũ mutãne! Idan kun kasance a cikin kõkanto daga addinĩna, to bã ni bauta wa,waɗanda kuke, bautã wa, baicin Allah, kuma amma ina bauta wa Allah wanda Yake karɓar rãyukanku. Kuma an umurce ni da in kasance daga mãsu ĩmãni." [10.105] "Kuma (an ce mini ): Ka tsayar da fuskarka ga addini, kanã karkata zuwa ga gaskiya, kuma kada ka kasance daga mãsu shirka. [10.106] "Kuma kada ka kirãyi, baicin Allah, abin da bã ya amfãnin ka kuma bã ya cũtar ka. To, idan ka aikata haka, sa´an nan lalle kai, a lõkacin, kanã daga mãsu zãlunci." [10.107] Kuma idan Allah Ya shãfe ka da wata cũta, to, bãbu mai yãyħ ta fãce shi, kuma idan Yanã nufin ka da wani alhħri, to, bãbu mai mayar da falalarSa. Yanã sãmun wanda Yake so daga cikin bãyinSa da shi. Kuma Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin ƙai. [10.108] Ka ce: "Yã ku mutãne! Lalle ne gaskiya, ta zo muku daga Ubangijinku. To, wanda ya shiryu, yã shiryu ne dõmin kansa kawai, kuma wanda ya ɓace yana ɓacewa ne a kansa kawai. Kuma ban zama wakĩli a kanku ba." [10.109] Kuma ka bi abin da ake yin wahayinsa zuwa gare ka, kuma ka yi haƙuri har Allah Ya yi hukunci. Kuma Shĩ ne Mafi alhħrin mãsu hukunci. @HUD Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [11.1] A. L̃. R. Littãfi ne an kyautata ãyõyinsa, sa´an nan an bayyanã su daki-daki, daga wurin Mai hikima, Mai ƙididdigewa. [11.2] Kada ku bautã wa kõwa fãce Allah. Lalle ne ni a gare ku mai gargaɗi ne kuma mai bushãrã daga gare Shi. [11.3] Kuma ku nħmi gãfara gun Ubangijinku. Sa´an nan ku tũba zuwa gare Shi, Ya jiyar da ku dãɗi, jiyarwa mai kyau zuwa ga ajali ambatacce, kuma Ya bai wa dukkan ma´abucin, girma girmansa. Amma idan kun jũya, to, lalle nĩ, inã tsõron azãbar yini mai girma a kanku. [11.4] Zuwa ga Allah makõmarku take, kuma Shĩ a kan kõme Mai ĩkon yi ne. [11.5] To, lalle sũ sunã karkatar(1) da ƙirjinsu dõmin su ɓõye daga gare shi. To, a lõkacin da suke lulluɓħwa da tufãfinsu Yanã sanin abin da suke ɓoyewa da abin da suke bayyanãwa. Lalle Shi Masani ne ga abin da yake a cikin ƙirãzã. [11.6] Kuma bãbu wata dabba a cikin ƙasa fãce ga Allah arzikinta yake, kuma Yanã sanin matabbatarta(1) da ma´azarta, duka sunã cikin littãfi bayyananne. [11.7] Kuma shi ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwanaki shida, kuma Al´arshinSa ya kasance akan ruwa,(2) d?min Ya jarrab? ku, wanne ne daga cikinku mafi kyãwon aiki. Kuma haƙĩƙa idan ka ce: "Lalle kũ waɗanda ake tãyarwa ne a bãyan mutuwa," haƙĩƙa waɗanda suka kãfirta sunã cħwa: "Wannan bai zama ba fãce sihiri bayyananne." [11.8] Kuma lalle ne idan Mun jinkirta da azãba gare su zuwa ga wani lõkaci ƙidãyayye, haƙĩƙa sunãcħwa me yake tsare(3) ta? To, a rãnar da zã ta je musu, ba ta zama abin karkatarwa ba daga gare su. Kuma abin da suka kasance suna yin izgili da shi, yã wajaba a kansu. [11.9] Kuma lalle ne idan Mun ɗanɗana wa mutum wata rahama daga gare Mu, sa´an nan kuma Muka zãre ta daga gare shi, lalle ne shĩ, hakĩka, mai yanke tsammãni ne, mai yawan k?firci. [11.10] Kuma lalle ne idan Mun ɗanɗana masa ni´ima a bãyan cũta ta shãfe shi, Yana cħwa mũnanan halaye sun tafi daga wurina. Lalle shi mai farin ciki ne, mai alfahari. [11.11] Sai waɗanda suka yi haƙuri kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai. Waɗannan sunã da gãfara da lãda mai girma. [11.12] Sabõda haka tsammãninka kai mai barin sãshen abin da aka yi wahayi zuwa gare ka ne, kuma mai ƙuntata ƙirjinka da shi ne dõmin sun ce: "Dõmin me ba a saukar masa da wata taska ba, kõ kuma Malã´ika ya zo tãre da shi?"(4) Kai mai gargaɗi ne kawai. Kuma Allah ne Wakili a kan kõme. [11.13] Kõ sunã cewa: "Yã ƙirƙira(1) shi ne."Ka ce: "Sai ku zo da sũrõri gõma misãlinsa ƙirƙirarru, kuma ku kirãyi wanda kuke iyãwa, baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya." [11.14] To, idan ba su amsa muku ba, to, ku sani cħwa an saukar da shi kawai ne da sanin Allah, kuma cħwa bãbu abin bauta wa fãce Shi. To, shin, kũ mãsu sallamãwa ne?, [11.15] Wanda ya kasance yã yi nufin rãyuwar dũniya da ƙawarta, Munã cika musu ayyukansu zuwa gare su a cikinta, kuma a cikinta bã zã a rage su ba. [11.16] Waɗannan ne waɗanda bã su da kõme a cikin Lãhira fãce wuta, kuma abin da suka sanã´anta a cikinta (dũniya) yã ɓãci, kuma abin da suka kasance sunã aikatãwa ɓãtacce ne. [11.17] Shin, wanda ya kasance a kan hujja bayyananna daga Ubangijinsa, kuma wata shaida tanã biyar sa daga gare Shi, kuma a gabãninsa akwai littãfin Mũsã abin kõyi da rahama? Waɗannan sunã yin ĩmãni da shi, kuma wanda ya kãfirta da shi daga ƙungiyõyi, to, wutã ce makõmarsa. Sabõda haka kada ka kasance a cikin shakka daga gare shi. Lalle shi ne gaskiya daga Ubangijinka, amma kuma mafi yawan mutãne bã su yin ĩmãni. [11.18] Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah? Waɗannan anã gitta su ga Ubangijinsu, kuma mãsu shaida su ce: "Waɗannan ne suka yi ƙarya ga Ubangijinsu. To, la´anar Allah ta tabbata a kan azzãlumai." [11.19] Waɗanda suke kangħwa daga hanyar Allah kuma sunã nħman ta karkace, kuma sũ ga Lãhira sunã kãfirta. [11.20] Waɗannan ne ba su kasance mabuwãya ba a cikin ƙasa, kuma waɗansu masõya ba su kasance ba a gare su, baicin Allah. Anã ninka musu azãba, ba su kasance sunã iya ji ba, kuma ba su kasance sunã gani ba. [11.21] Waɗannan ne wɗanda suka yi hasãrar rãyukansu, kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙirawa ya ɓace musu. [11.22] Bãbu makawã cħwa, haƙĩƙa, sũ a lãhira, sũ ne mafi hasãra. [11.23] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka yi tawãlu´i zuwa ga Ubangijinsu, waɗannan ne abõkan Aljanna, sunã madawwama a cikinta. [11.24] Misãlin ɓangaren biyu kamar makãho ne da kurmã, da mai gani da mai ji. Shin, sunã daidaita ga misãli? Ashe, bã ku yin tunãni? [11.25] Kuma haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutanensa, (ya ce): "Lalle ne ni, a gare ku mai gargaɗi bayyananne ne." [11.26] "Kada ku bautã wa kõwa fãce Allah. Lalle nĩ, inã jin tsõron azãbar yini mai raɗaɗi a kanku." [11.27] Sai mashãwarta waɗanda suka kãfirta, daga mutãnensa, suka ce: "Bã mu ganin ka fãce mutum kake kamarmu, kuma ba mu ganin wani ya bĩ ka fãce waɗanda suke sũ ƙasƙantattunmu ne marasa tunani. Kuma bã mu ganin wata falalã agare ka a kanmu. ôa, Munã zaton ku maƙaryata ne." [11.28] Ya ce: "Ya mutãnena! Shin, kun gani idan na kasance a kan wata hujja bayyananna daga Ubangijina, kuma Yã bã ni wata Rahama daga wurinSa, Sa´an nan aka rufe ta (ita Rahamar) daga gare ku, shin, zã mu tĩlasta muku ita, alhãli kuwa kũ mãsu ƙi gare ta ne? [11.29] "Kuma yã mutãnena! Bã zan tambaye ku wata dũkiya ba akansa, ijãrata ba ta zama ba, fãce daga Allah, kuma ban zama mai kõrar waɗanda suka yĩ ĩmãni ba. Haƙĩƙa sũ, mãsu haɗuwa da Ubangijinsu ne, kuma amma ni, inã ganin ku mutãne ne jãhilai." [11.30] "Kuma ya mutãnena! Wãne ne yake taimakõna daga Allah idan na kõre su? Ashe, bã ku tunãni?" [11.31] "Kuma bã ni ce muku a wurĩna taskõkin Allah suke kuma bã inã sanin gaibi ba ne. Kuma ba inã cħwa ni Malã´ika ba ne. Kuma ba ni cħwa ga waɗanda idãnunku suke wulãkantãwa, Allah bã zai bã su alhħri ba. Allah ne Mafi sani ga abin da yake cikin zukatansu. Lalle ne ni, idan (nã yi haka) dã ina daga cikin azzalumai." [11.32] Suka ce: "Yã Nũhu, lalle ne kã yi jayayya da mu, sa´an nan kã yawaita yi mana jidãli, to, ka zõ mana da abin da kake yi mana wa´adi idan kã kasance daga mãsu gaskiya." [11.33] Ya ce: "Allah kawai ne Yake zo muku da shi idan Ya so. Kuma ba ku zama mabuwãya ba." [11.34] "Kuma nasĩhãta bã zã ta amfãne ku ba, idan nã yi nufin in yi muku nasĩha, idan Allah Ya kasance Yanã nufin Ya halaka ku. Shĩ ne Ubangijinku, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku." [11.35] Ko sunã cħwa: (Nũhu) ya ƙirƙira shi. Ka ce: "Idan nĩ (Nũhu) na ƙirƙira shi to, laifĩnã a kaina yake, kuma nĩ mai barrantã ne daga abin da kuke yi na laifi." [11.36] Kuma aka yi wahayi zuwa ga Nũhu cħwa: Lalle ne bãbu mai yin ĩmãni daga mutãnenka fãce wanda ya riga ya yi ĩmãnin, sabõda haka kada ka yi baƙin ciki da abin da suka kasance sunã aikatãwa. [11.37] Kuma ka sassaƙa jirgi da kyau bisa idanunMu da wahayinMu, kuma kada ka yi Mini magana a cikin sha´anin waɗanda suka kãfirta, lalle ne sũ, waɗanda ake nutsarwa ne. [11.38] Kuma Yanã sassaƙa jirgin cikin natsuwa, kuma a kõ yaushe waɗansu shugabanni daga mutãnensa suka shũɗe a gabansa, sai su yi izgili gare shi. Ya ce: "Idan kun yi izgili gare mu, to, haƙĩƙa mũ mã zã mu yi izgili gare ku, kamar yadda kuke yin izgili. [11.39] "Sa´an nan da sannu zã ku san wanda azãba zã ta zo masa, ta wulakantã shi (a dũniya), kuma wata azãba zaunanna ta sauka a kansa (a Lãhira)." [11.40] Har a lõkacin da umurninMu ya je, kuma tandã ta ɓulɓula. Muka ce: "Ka ɗauka, a cikinta, daga kõme, ma´aura biyu, da kuma iyalanka, fãce wanda magana ta gabãta a kansa,(1) da wanda ya yi ĩmãni." Amma kuma bãbu waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi fãce kaɗan." [11.41] Kuma ya ce: "Ku hau a cikinta, da sũnan Allah magudãnarta da matabbatarta. Lalle ne Ubangijĩna, haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai." [11.42] Kuma ita tanã gudãna da su a cikin tãguwar ruwa kamai duwãtsu, sai Nũhu ya kirãyi ɗansa alhãli, kuwa ya kasance can wuri mai nĩsa. "Yã ƙaramin ɗãnã! zo ka hau tãre da mu, kuma kada ka kasance tãre da kãfirai!" [11.43] Ya ce: "Zan tattara zuwa ga wani dũtse ya tsare ni daga ruwan." (Nũhu) ya ce: "Bãbu mai tsarħwa a yau daga umurnin Allah fãce wanda Ya yi wa rahama." Sai taguwar ruwa ta shãmakace a tsakãninsu, sai ya kasance daga waɗanda aka nutsar. [11.44] Kuma aka ce: "Yã ƙasa! Ki haɗiye ruwanki, kuma yã sama! Ki kãme."Kuma aka faƙar da ruwan kuma aka hukunta al´amarin, kuma Jirgin ya daidaita a kan Jũdiyyi, (2) kuma aka ce: "Nĩsa ya tabbata ga mutãne azzãlumai." [11.45] Kuma Nũhu ya kira Ubangijinsa, sa´an nan ya ce: "Yã Ubangijina! Lalle ne ɗãna na daga iyãlĩna! Kuma haƙĩƙa wa´adinKa gaskiya ne, kuma Kai ne Mafi hukuncin mãsu yin hukunci." [11.46] Ya ce: "Yã Nũhu! Lalle ne shi bã ya a ciki iyãlanka, lalle ne shĩ, aiki ne wanda ba na ƙwarai ba, sabõda haka kada ka tambaye Ni abin da bã ka da ilmi a kansa. Haƙĩƙa, Nĩ Inã yi maka gargaɗi kada ka kasance daga jãhilai." [11.47] Ya ce: "Yã Ubangijina! Lalle ne nĩ, inã nħman tsari gare Ka da in tambaye Ka abin da bã ni da wani ilmi a kansa. Idan ba Ka gãfarta mini ba, kuma Ka yi mini rahama, zan kasance daga mãsu hasãra." [11.48] Aka ce: "Ya Nũhu! Ka sauka da aminci daga gare Mu da albarka a kanka, kuma rahama ta tabbata a kan waɗansu al´ummõmi daga waɗanda suke tãre da kai. Da waɗansu al´ummõmi da zã Mu jiyar da su dãɗi, sa´an nan kuma azãba mai raɗaɗi ta shafe su daga gare Mu." [11.49] Waccan ƙissa tanã daga lãbãran gaibi, Munã yin wahayinsu zuwa gare ka (Muhammadu). Ba ka kasance kanã sanin su ba, haka kuma mutãnenka ba su sani ba daga gabãnin wannan. Sai ka yi haƙuri. Lalle ne ãƙiba tanã ga mãsu taƙawa, [11.50] Kuma zuwa ga Ãdãwa, (Mun aika) ɗan´uwansu Hũdu. Ya ce: "Yã kũ mutãnena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautãwa fãce Shi. Ba ku kasance ba fãce kunã mãsu ƙirƙirãwa. [11.51] "Yã ku mutãnena! Bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa, ijãrata ba ta zama ba, fãce ga wanda Ya ƙãga halittata. Shin fa, bã ku hankalta?" [11.52] "Kuma, ya mutãnena! Ku nħmi Ubangijinku gãfara, sa´an nan kuma ku tũba zuwa gare Shi, zai saki sama a kanku, tanã mai yawan zubar da ruwa, kuma Ya ƙãra muku wani ƙarfi ga ƙarfinku. Kuma kada ku jũya kunã mãsu laifi." [11.53] Suka ce: "Yã Hũdu! Ba ka zo mana da wata hujja bayyananna ba, kuma ba mu zama mãsu barin abũbuwan bautawarmu ba dõmin maganarka, kuma ba mu zama mãsu yin ĩmãni da kai ba." [11.54] "Bã mu cħwa, sai dai kurum sashen abũbuwan bautawarmu ya sãme ka da cũtar hauka." Yace: "Lalle ne nĩ, inã shaida wa Allah, kuma ku yi shaidar cħwa" lalle ne nĩ mai barranta ne daga abin da kuke yin shirki da shi." [11.55] "Baicin Allah: Sai ku yi mini kaidi gabã ɗaya, sa´an nan kuma kada ku yi mini jinkiri." [11.56] "Haƙĩƙa, ni na dõgara ga Allah, Ubangijĩna kuma Ubangijinku. Bãbu wata dabba fãce Shi ne Mai riko ga kwarkwaɗarta.(1) Haƙĩƙa, Ubangijĩna Yanã (kan) tafarki madaidaici." [11.57] "To! Idan kun jũya, haƙĩƙa, nã iyar muku abin da aka aiko ni da shi zuwa gare ku. Kuma Ubangijĩna Yanã musanya waɗansu mutãne, waɗansunku su maye muku. Kuma bã ku cũtar Sa da kõme. Lalle Ubangijina a kan dukkan kõme, Matsari ne." [11.58] Kuma a lõkacin da umurninmu ya je, Muka kuɓutar da Hũdu da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sabõda wata rahama daga gare Mu. Kuma Muka kuɓutar da su daga azãba mai kauri. [11.59] Haka Ãdãwa suka kasance, sun yi musun ãyõyin Ubangijinsu, kuma sun sãɓa wa ManzanninSa, kuma sun bi umurnin dukan mai girman kai, makangari. [11.60] Kuma an biyar musu da la´ana a cikin wannan dũniya da Rãnar Kiyãma. To! Lalle ne Ãdãwa sun kãfirta da Ubangijinsu. To, Nĩsa ya tabbata ga Ãdãwa, mutãnen Hũdu! [11.61] Kuma zuwa ga Samũdãwa (an aika) ɗan´uwansu Sãlihu. Ya ce: "Ya mutãnena! Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani abin bautãwa fãce Shi. Shĩ ne Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma Ya sanya ku mãsu yin kyarkyara a cikinta. Sai ku nħme Shi gãfara, sa´an nan kuma ku tũba zuwa gare Shi. Lalle Ubangijina Makusanci ne Mai karɓãwa." [11.62] Suka ce: "Ya Sãlihu! Haƙĩƙa, kã kasance a cikinmu, wanda ake fatan wani alhħri da shi a gabãnin wannan. Shin kana hana mu bauta wa abin da ubanninmu suke bauta wa? Kuma haƙĩƙa mũ, munã cikin shakka daga abin da kake kiran mu gare shi, mai sanya kõkanto." [11.63] Ya ce: "Ya mutãnħna! Kun gani? Idan na kasance a kan hujja bayyananna daga Ubangijina, kuma Ya bã ni rahama daga gare Shi, to, wane ne zai taimake ni daga Allah idan nã sãɓa Masa? Sa´an nan bã zã ku ƙãre ni da kõme ba fãce hasãra." [11.64] "Kuma ya mutãnena! wannan rãƙumar Allah ce, tanã ãyã a gare ku. Sai ku bar ta ta ci a cikin ƙasar Allah, kuma kada ku shãfe ta da wata cũta kar azãba makusanciya ta kãma ku." [11.65] Sai suka sõke ta. Sai ya ce: "Kuji dãɗi a cikin gidãjenku kwãna uku. Wannan wa´adi ne bã abin ƙaryatãwa ba." [11.66] To, a lõkacin da umurninMu ya je, muka kuɓutar da Sãlihu da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sabõda wata rahama daga gare Mu, kuma daga wulãkancin rãnar nan. Lalle ne Ubangijinka Shĩ neMai ƙarfi, Mabuwãyi. [11.67] Sai tsãwa ta kãma waɗanda suka yi zãlunci, sai suka wãyi gari sunã guggurfãne a cikin gidãjensu. [11.68] Kamar dai ba su zauna a cikinta ba. To! Lalle ne samũdãwa sun kãfirce wa Ubangijinsu. To, Nĩsa ya tabbata ga Samũdãwa. [11.69] Kuma haƙĩƙa, manzanninMu sun je wa Ibrãhim da bushãra suka ce: "Aminci." Ya ce: "Aminci (ya tabbata a gare ku)." Sa´an nan bai yi jinkiri ba ya je da maraƙi ƙawãtacce. [11.70] Sa´an nan a lõkacin da ya ga hannayensu bã su sãduwa zuwa gare shi (maraƙin), sai ya yi ƙyãmarsu, kuma ya ji tsõronsu. Suka ce, "Kada kaji tsõro lalle ne mũ, an aiko mu ne zuwa ga mutãnen Lũɗu" [11.71] Kuma mãtarsa tanã tsaye(1) . Ta yi dãriya. Sai Muka yi mata bushãra (da haihuwar) Is´hãƙa, kuma a bayan Is´hãƙa, Yãƙũbu. [11.72] Sai ta ce: "Yã kaitõna! Shin, zan haihu ne alhãli kuwa inã tsõhuwa, kuma ga mijĩna tsõho ne? Lalle wannan, haƙĩƙa, abu ne mai ban mãmãki." [11.73] Suka ce: "Shin kinã mãmaki ne daga al´amarin Allah? Rahamar Allah da albarkarSa su tabbata a kanku, ya mutãnen babban gida! Lalle ne Shĩ abin gõdewa ne, Mai girma." [11.74] To, a lõkacin da firgita ta tafi daga Ibrãhĩm, kuma bushãra tã je masa, Yanã mai jayayya a gare Mu, sabõda mutãnen Lũɗu! [11.75] Lalle Ibrãhĩm, haƙĩƙa mai haƙuri ne, mai yawan addu´a, mai tawakkali. [11.76] Ya Ibrãhĩm! Ka bijira daga wannan. Lalle shi, haƙĩƙa, umurnin Ubangijinka ne ya zo, kuma lalle ne sũ, abin da yake mai je musu azãba ce wadda bã a iya hanãwa. [11.77] Kuma a lõkacin da manzanninMu suka je wa Lũɗu aka ɓãta masa rai game da su, ya, ƙuntata rai sabõda su. Ya ce: "Wannan yini ne mai tsananin masĩfa." [11.78] Kuma mutãnensa suka je masa sunã gaggãwa zuwa gare shi, kuma a gabãni, sun kasance sunã aikatãwar mũnãnan ayyuka. Ya ce: "Yã mutãnħna! waɗannan, ´yã´yã na(1) sũ ne mafiya tsarki a gare ku. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku wulãkantã ni a cikin bãƙĩna. Shin, bãbu wani namiji shiryayye daga gare ku?" [11.79] Suka ce: "Lalle, haƙĩƙa kã sani, bã mu da wani hakki a cikin ´ya´yanka, kuma lalle kai haƙĩƙa, kanã sane da abin da muke nufi." [11.80] Ya ce: "Dã dai inã da wani ƙarfi game da ku, kõ kuwa inã da gõyon bãya daga wani rukuni(2) mai ƙarfi?" [11.81] (Manzannin) Suka ce: "Yã Lũɗu! Lalle mũ, manzannin Ubangijinka ne. Bã zã su iya sãduwa zuwa gare ka ba. Sai ka yi tafiyarka a wani yankin dare da iyãlinka, kuma kada wani daga gare ku ya waiwaya fãce mãtarka. Lalle ne abin da ya same su mai sãmunta ne. Lalle wa´adinsu lõkacin sãfiya ne. Shin lõkacin sãfiya bã kusa ba ne?" [11.82] Sa´an nan a lõkacin da umurninMu ya je, Muka sanya na samanta ya zama na ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu a kanta (ƙasar Lũɗu) daga taɓo cũrarre. [11.83] Alamtacce a wurin Ubangijinka. Kuma ita (ƙasar Lũɗu) ba ta zama mai nĩsa ba daga azzãlumai (Kuraishãwa). [11.84] Kuma zuwa ga Madyana (Mun aika) ɗan´uwansu(1) Shu´aibu. Ya ce: "Ya Mutãnena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautãwa fãce shi kuma kada ku rage mũdu da sikħli. Lalle nĩ, inã ganin ku da wadãta.(2) Kuma lalle inã ji muku tsõron azãbar yini mai kħwayħwa." [11.85] "Ya mutãnħna! Ku cika mũdu da sikħli da ãdalci, kuma kada ku naƙasta wa mutãne kãyansu, kuma kada ku yi ɓarnã a cikin ƙasa kunã mãsu fasãdi." [11.86] "Falalar Allah mai wanzuwa ita ce mafi alhħri a gare ku idan kun kasance muminai, kuma ni bã mai tsaro ne a kanku ba." [11.87] Suka ce: "Yã Shu´aibu! Shin sallarka ce take umurtar ka ga mu bar abin da ubanninmu suke bautãwa, kõ kuwa mu bar aikata abin da muke so a cikin dũkiyõyinmu? Lalle, haƙĩƙa kai ne mai haƙuri shiryayye!" [11.88] Ya ce: "Ya mutãnena! Kun gani idan na kasance a kan hujja bayyananniya daga Ubangijina, kuma Ya azurta nĩ da arziki mai kyãwo daga gare Shi? Kuma bã ni nufin in sãɓa muku zuwa ga abin da nake hana ku daga gare shi. Bã ni nufin kõme fãce gyãrã, gwargwadon da na sãmi dãma. Kuma muwãfaƙãta ba ta zama ba fãce daga Allah. A gare shi na dõgara, kuma zuwa gare Shi na wakkala." [11.89] "Kuma ya mutãnena! Kada sãɓa mini ya ɗauke ku ga misãlin abin da ya sãmi mutãnen Nũhu kõ kuwa mutãnen Hũdu kõ kuwa mutãnen Sãlihu ya sãme ku. Mutãnen Lũɗu ba su zama a wuri mai nĩsa ba daga gare ku." [11.90] "Kuma ku nħmi Ubangijinku gãfara, sa´an nan kuma ku tũba zuwa gare shi. Lalle Ubangijĩna Mai Jin ƙai ne, Mai nũna sõyayya." [11.91] Suka ce: "Yã Shu´aibu! Bã mu fahimta da yawa daga abin da kake faɗi, kuma munã ganin ka mai rauni a cikinmu. Kuma bã dõmin jama´arka ba dã mun jħfe ka, sabõda ba ka zama mai daraja a gunmu ba." [11.92] Ya ce: "Ya mutãnena! Ashe, jama´ãta ce mafi daraja a gare ku daga Allah, kuma kun riƙħ Shi a bãyanku abin jħfarwa? Lallene Ubangijĩna Mai kħwayħwa ne ga abin da kuke aikatãwa." [11.93] "Kuma ya mutãnena! Ku yi aiki a kan hãlinku. Lalle nĩ mai aiki ne. Da sannu zã ku san wãne ne azãba zã ta zo masa, ta wulakanta shi, kuma wãne ne maƙaryaci. Kuma ku yi jiran dãko, lalle ni mai dãko ne tãre da ku." [11.94] Kuma a lõkacin da umurninMu yã je, Muka kuɓutar da Shu´aibu da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sabõda wata rahama daga gare, Mu. Kuma tsãwa ta kama waɗanda suka yi zãlunci. Sai suka wãyi gari guggurfãne a cikin gidãjensu. [11.95] Kamar ba su zaunã ba a cikinsu. To, halaka ta tabbata ga Madyana kamar yadda Samũdãwa suka halaka. [11.96] Kuma haƙĩƙa Mun aiki Mũsã da ãyõyinMu, da dalĩli bayyananne. [11.97] Zuwa ga Fir´auna da majalisarsa. Sai suka bi umurnin Fir´auna, amma al´amarin Fir´auna bai zama shiryayye ba. [11.98] Yanã shũgabantar mutãnensa a Rãnar Kiyãma, har ya tuzgar da su a wuta. Kuma tir da irin tuzgãwarsu. [11.99] Kuma aka biyar musu da la´ana a cikin wannan dũniya da Rãnar Kiyãma. Tir da kyautar(1) da ake yi musu. [11.100] Wancan Yanã daga lãbãran alƙaryõyi. Munã bã ka lãbãrinsu, daga gare su akwai wanda ke tsaye da kuma girbabbe.(2) [11.101] Kuma ba Mu zãlunce su ba, amma sun zãlunci kansu sa´an nan abũbuwan bautawarsu waɗanda suke kiran su, baicin Allah, ba su wadãtar musu kõme ba a lõkacin da umurnin Ubangijinka ya je, kuma (gumãkan) ba su ƙãra musu wani abu ba fãce hasãra. [11.102] Kuma kamar wancan ne kãmun Ubangijinka, idan Ya kãma alƙaryõyi alhãli kuwa sunã mãsu zãlunci. Lalle kamũnSa mai raɗaɗi ne, mai tsanani. [11.103] Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga wanda ya ji tsõron azãbar Lãhira. Wancan yini ne wanda ake tãra mutãne a cikinsa kuma wancan yini ne abin halarta. [11.104] Ba Mu jinkirtã shi ba fãce dõmin ajali ƙidãyayye. [11.105] Rãnar da za ta zo wani rai ba ya iya magana fãce da izninSa. Sa´an nan daga cikinsu akwai shaƙiyyi da mai arziki. [11.106] To, amma waɗanda suka yi shaƙãwa, to, sunã a cikin wuta. Sunã mãsu ƙãra da shħka a cikinta. [11.107] Suna madawwama a cikinta matuƙar sammai da ƙasa sun dawwama, fãce abin da Ubangijinka Ya so. Lalle Ubangijinka Mai aikatãwa ne ga abin da Yake nufi. [11.108] Amma waɗanda suka yi arziki to, sunã a cikin Aljanna sunã madawwama, a cikinta, matuƙar sammai da ƙasa sun dawwama, fãce abin da Ubangijinka Ya so. Kyauta wadda bã ta yankħwa. [11.109] Sabõda haka kada ka kasance a cikin shakka daga abin da waɗannan suke bautawa. Bã su wata ibãda fãce kamar yadda ubanninsu ke aikatãwa a gabani. Kuma haƙĩƙa Mũ, Mãsu cika musu rabon su ne, bã tãre da nakasãwa ba. [11.110] Kuma haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã littãfi, sai aka sãɓã(1) wa jũna a cikinsa. Kuma bã dõmin wata kalma wadda ta gabãta daga Ubangijinka ba, haƙĩƙa, dã an yi hukunci a tsakãninsu. Kuma haƙĩƙa, sunã a cikin wata shakka, game da shi, mai sanya kõkanto. [11.111] Kuma lalle, haƙĩƙa, Ubangijinka Mai cika wa kõwa (sakamakon) ayyukansa ne. Lalle Shĩ, Mai ƙididdigewa ne ga abin da suke aikatãwa. [11.112] Sai ka daidaitu(2) kamar yadda aka umurce ka, kai da waɗanda suka tũba tãre da kai kunã bã mãsu ƙħtara haddi ba. Lalle shĩ, Mai gani ne ga abin da kuke aikatãwa. [11.113] Kada ku karkata(3) zuwa ga waɗanda suka yi zãlunci har wuta ta shãfe ku. Kuma bã ku da waɗansu majiɓinta baicin Allah, sa´an nan kuma bã zã a taimake ku ba. [11.114] Kuma ka tsai da salla a għfe guda biyu na yini da wani yanki daga dare. Lalle ne ayyukan ƙwarai sunã kõre mũnãnan ayyuka. Wancan(4) ne tunãtarwa ga mãsu tunãwa. [11.115] Kuma ka yi haƙuri. Allah bã Ya tõzartar da lãdar mãsu kyautatãwa.(5) [11.116] To, don me mãsu hankali ba su kasance daga mutãnen ƙarnõnin da suke a gabãninku ba, sunã hani daga ɓarna a cikin ƙasa? fãce kaɗan daga wanda Muka kuɓutar daga gare su (sun yi hanin). Kuma waɗanda suka yi zãlunci suka bi abin da aka ni´imtar da su a cikinsa, suka kasance mãsu laifi. [11.117] Kuma Ubangijinka bai kasance Yanã halakar da alƙaryu sabõda wani zãlunci ba, alhãli mutãnensu sunã mãsu gyãrãwa.(6) [11.118] Kuma dã Ubangijinka Ya so, dã Yã sanya mutãne al´umma guda. Kuma bã zã su gushe ba sunã mãsu sãɓã wa jũna. [11.119] Sai wanda Ubangijinka Ya yi wa rahama, kuma dõmin wannan(1) ne Ya halicce su. Kuma kalmar "Ubangijinka" Lalle ne zã Ni cika Jahannama da aljannu da mutãne gaba ɗaya" ta cika. [11.120] Kuma dũbi dai Munã bã da lãbãri a gare ka daga lãbarun Manzanni, abin da Muke tabbatar da zuciyarka da shi. Kuma gaskiya ta zo maka a cikin wannan da wa´azi da tunãtarwã ga mãsu ĩmãni. [11.121] Kuma kace wa waɗanda bã su yin ĩmãni, "Ku yi aiki a kan hãlinku, lalle mũ mãsu aiki ne. [11.122] "Kuma ku yi Jiran dãko, lalle mu mãsu Jiran dãko(2) ne." [11.123] Kuma ga Allah gaibin sammai da ƙasa yake. Kuma zuwa gare Shi ake mayar da dukan al´amari. Sabõda haka ku bauta Masa kuma ku dõgara a kanSa. Kuma Ubangijinka bai zama Mai gafala daga abin da kuke aikatãwa ba. @YUSUF Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [12.1] A. L̃. R. Waɗancan ãyoyin Littãfi mai bayyanãwa ne. [12.2] Lalle ne Mũ, Mun saukar da shi, yanã abin karantãwa na Lãrabci; tsammãninkũ, kunã hankalta. [12.3] Mũ, Munã bãyar da lãbãri a gare ka, mafi kyãwon lãbãri ga abin da Muka yi wahayin wannan Alƙur´ãni zuwa gare ka. Kuma lalle ne kã kasance a gabãninsa, haƙĩƙa, daga gafalallu. [12.4] A lõkacin da Yũsufu ya ce wa ubansa, "Yã bãba! Lalle ne nĩ, nã ga taurãri gõma shã ɗaya, da rãnã da watã. Na gan su sunã mãsu sujada a gare ni." [12.5] Ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Kada ka faɗi mafarkinka ga ´yan´uwanka, har su ƙulla maka wani kaidi. Lalle ne Shaidan ga mutum, haƙĩƙa, maƙiyi ne bayyanãnne.(1) [12.6] "Kuma kãmar wancan ne, Ubangijinka Yake zãɓen ka, kuma Ya sanar da kai daga fassarar lãbãrai, kuma ya cika ni´imõminSa a kanka, kuma a kan gidan Yãƙũba kãmar yadda ya cika su a kan ubanninka biyu, a gabãni, Ibrãhĩm da Is´hãƙa. Lalle Ubangijinka ne Masani, Mai hikima." [12.7] Lalle ne, haƙĩƙa, ãyõyi(2) sun kasance ga Yũsufu da ´yan´uwansa(3) dõmin mãsu tambaya. [12.8] A lõkacin da suka ce:(4) lalle ne Yũsufu da ɗan´uwansa ne mafiya sõyuwa ga ubanmu daga gare mu, alhãli kuwa mũ jama´a guda ne. Lalle ubanmu, haƙĩƙa, yanã cikin ɓata bayyananniya. [12.9] Ku kashe Yũsufu, kõ kuwa ku jħfa shi a wata ƙasa, fuskar ubanku ta wõfinta sabõda ku, kuma ku kasance a bãyansa mutãne sãlihai. [12.10] Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Kada ku kashe Yũsufu. Ku jħfa shi a cikin duhun rĩjiya, wasu matafiya su tsince shi, idan kun kasance mãsu aikatãwa ne." [12.11] Suka ce: "Yã bãbanmu!(5) Mħne ne a gare ka ba ka amince mana ba a kan Yũsufu, alhãli kuwa lalle ne mũ, haƙiƙa mãsu nashĩha muke a gare shi?" [12.12] "Ka bar shi tãre da mu a gõbe, ya ji dãɗi, kuma ya yi wãsa. Kuma lalle ne mu, a gare shi, mãsu tsaro ne." [12.13] Ya ce: "Lalle ne ni, haƙiƙa yanã ɓãta mini rai ku tafii da shi, Kuma inã tsõron kerkħci ya cinye shi, alhãli ku kuwa kunã mãsu shagala daga gare shi." [12.14] Suka ce: "Haƙĩƙa idan kerkħci ya cinye shi, alhãli kuwa munã dangin jũna, lalle ne mũ, a sa´an nan, hakĩka, mun zama mãsu hasãra." [12.15] To, a lõkacin(1) da suka tafi da shi, kuma suka yi niyyar su sanya shi a cikin duhun rĩjiya, Muka yi wahayi zuwa gare shi, "Lalle ne, kanã bã su lãbari game da wannan al´amari nãsu, kuma sũ ba su sani ba." [12.16] Kuma suka je wa ubansu da dare sunã kũka. [12.17] Suka ce: "Yã bãbanmu!(2) Lalle ne, mun tafi munã tsħre, kuma muka bar Yusufu a wurin kãyanmu, sai kerkħci ya cinye shi, kuma kai, bã mai amincħwa da mu ba ne, kuma kõ dã mun kasance mãsu gaskiya!"_ [12.18] Kuma suka je, a jikin rigarsa akwai wani jinin ƙarya. Ya ce: "ôa, zukatanku suka ƙawãta muku wani al´amari. Sai haƙuri mai kyau! Kuma Allah ne wanda ake nħman taimako (a gunSa) a kan abin da kuke siffantãwa." [12.19] Kuma wani ãyari(3) ya je, sai suka aika mai nħman musu rũwa, sai ya zura gugansa, ya ce: "Yã bushãrata! Wannan yãro ne." Kuma suka ɓõye shi yanã abin sayarwa. Kuma Allah ne Masani ga abin da suke aikatãwa. [12.20] Kuma suka sayar(4) da shi da ´yan kuɗi kaɗan, dirhamõmi ƙidãyayyu, Kuma sun kasance, a wurinsa, daga mãsu isuwa da abu kaɗan. [12.21] Kuma wanda ya saye shi daga Masar(5) ya ce wa mãtarsa, "Ki girmama mazauninsa, akwai tsammãnin ya amfãne mu, kõ kuwa mu riƙe shi ɗã."Kuma kamar wancan ne Muka tabbatar ga Yũsufu,a cikin ƙasa kuma dõmin Mu sanar da shi daga fassarar labaru, kuma Allah ne Marinjãyi a kan al´amarinSa, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba." [12.22] Kuma a lõkacin da ya isa mafi ƙarfinsa, Muka bã shi hukunci da ilmi. Kuma kamar wancan ne Muke sãka wa mãsu kyautatãwa. [12.23] Kuma wadda yake(1) a cikin ɗãkinta, ta nħme shi ga kansa, kuma ta kukkulle ƙõfõfi, kuma ta ce, "Yã rage a gare ka!" ya ce: "Ina neman tsarin Allah! Lalle shĩ ne Ubangijina. Yã kyautata mazaunina. Lalle ne shĩ, mãsu zãlunci ba su cin nasara!" [12.24] Kuma lalle ne, tã himmantu da shi. Kuma yã himmantu da ita in bã dõmin ya ga dalĩlin Ubangijinsa ba. Kãmar haka dai, dõmin Mu karkatar da mummũnan aiki da alfãsha daga gare shi. Lalle ne shi, daga bãyinMu zaɓaɓɓu yake. [12.25] Kuma suka yi tsħre(2) zuwa ga ƙõfa. Sai ta tsãge rigarsa daga bãya, kuma suka iske mijinta a wurin ƙõfar. Ta ce: "Mħnene sakamakon wanda ya yi nufin cũta game da iyãlinka? Fãce a ɗaure shi, ko kuwa a yi masa wata azãba mai raɗaɗi." [12.26] Ya ce: "Ita ce ta nħme ni a kaina."Kuma wani mai shaida daga mutãnenta ya bãyar da shaida:(3) "Idan rigarsa ta kasance an tsage ta daga gaba, to, tã yi gaskiya, kuma shĩ ne daga maƙaryata." [12.27] "Kuma idan rigarsa ta kasance an tsãge ta daga bãya, to, tã yi ƙarya, kuma shĩ ne daga mãsu gaskiya." [12.28] Sa´an nan a lõkacin da ya ga rĩgarsa an tsãge ta daga bãya, ya ce: "Lalle ne shi, daga kaidinku ne, mata! Lalle ne kaidinku mai girma ne!" [12.29] "Yusufu! Ka kau da kai daga wannan. Kuma ki nħmi gãfara(4) dõmin laifinki. Lalle ne ke, kin kasance daga mãsu kuskure." [12.30] Kuma waɗansu mãtã(5) a cikin Birnin suka ce: "Matar Azĩz tanã nħman hãdiminta daga kansa! Haƙĩƙa, yã rufe zũciyarta da so. Lalle ne mũ, Munã ganin ta a cikin ɓata bayyanãnna." [12.31] Sa´an nan a lõkacin da ta ji lãbãri game da mãkircinsu, sai ta aika kiran liyafa zuwa gare su, kuma ta yi tattalin abincin da ake dõgara wajen cinsa, kuma ta bai wa kõwace ɗaya daga cikinsu wuƙa, kuma ta ce: "Ka fito a kansu." To, a lõkacin da, suka gan shi, suka girmamã shi, kuma suka yanyanke hannãyensu, kuma suka ce: "Tsarki yanã ga Allah! Wannan bã mutum ba ne! Wannan bai zama ba fãce Malã´ika ne mai daraja!" [12.32] Ta ce: "To wannan ne fa wanda kuka, zarge(1) ni a cikinsa! Kuma lalle ne, haƙiƙa na nħme shi daga kansa, sai ya tsare gida, kuma nĩ inã rantsuwa, idan bai aikata abin da nake umurnin sa ba, haƙiƙa anã ɗaure shi. Haƙĩƙa, yanã kasancewa daga ƙasƙantattu." [12.33] Ya ce: "Yã Ubangijina! Kurkuku ne mafi sõyuwa a gare ni daga abin da suke kirã na zuwa gare shi. Kuma idan ba Ka karkatar da kaidinsu daga gare ni ba, zan karkata zuwa gare su, kuma in kasance daga jãhilai." [12.34] Sai Ubangijinsa Ya karɓa masa sabõda haka Ya karkatar da kaidinsu daga gare shi. Lalle Shĩ ne Mai jĩ, Masani. [12.35] Sa´an nan kuma ya bayyana a gare su a bãyan sun ga alãmõmin, lalle ne dai su ɗaure shi har zuwa wani lõkaci. [12.36] Kuma waɗansu samãri biyu suka shiga kurkuku tãre da shi.(2) Ɗayansu ya ce: "Lalle ne nĩ, nã yi mafarkin gã ni inã mãtsar giya." Kuma ɗayan ya ce: "Lalle ne nĩ, nã yi Mafarkin gã ni inã ɗauke da waina a bisa kaina, tsuntsãye sunã ci daga gare ta. Ka bã mu lãbãri game da fassararsu. Lalle ne mũ, Munã ganin ka daga mãsu kyautatãwa." [12.37] Ya ce: "Wani abinci bã zai zo muku ba wanda ake azurtã ku da shi fãce nã bã ku lãbãrin fassararsa(3) , kãfin ya zo muku. Wannan kuwa yanã daga abin da Ubangijĩna Ya sanar da ni. Lalle ne nĩ nã bar addinin mutãne waɗanda ba su yi ĩmãni da Allah ba, kuma game da lãhira, sũ kãfirai ne." [12.38] "Kuma na bi addinin iyayħna, Ibrãhĩm da Is´hãka da Yãƙũba. Bã ya yiwuwa a gare mu mu yi shirka da Allah da kõme. Wannan yana daga falalar Allah a kanmu da mutãne, amma mafi yawan mutãne bã su gõdewa." [12.39] "Yã abõkaina biyu na kurkuku! Shin iyãyen giji dabam-dabam ne mafiya alhħri kõ kuwa Allah Makaɗaici Mai tanƙwasãwa?" [12.40] "Ba ku bauta wa kõme, baicinSa, fãce waɗansu sũnãye waɗanda kuka ambace su, kũ da ubanninku. Allah bai saukar da wani dalĩli ba game da su. Bãbu hukunci fãce na Allah. Ya yi umurnin kada ku bauta wa kõwa fãce Shi. Wancan ne addini madaidaici, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba." [12.41] "Yã abõkaina biyu, na kurkuku! Amma ɗayanku, to, zai shãyar da uban gidansa giya, kuma gudan, to, zã a tsĩrħ shi, sa´an nan tsuntsãye su ci daga kansa. An hukunta al´amarin, wanda a cikinsa kuke yin fatawa." [12.42] Kuma ya ce da wanda ya tabbatar da cħwa shi mai kuɓuta ne daga gare su, "Ka ambacħ ni a wurin uban gidanka." Sai Shaiɗan ya mantar da shi tunãwar Ubangijinsa, sabõda haka ya zauna a cikin kurkuku ´yan shekaru. [12.43] Kuma sarki ya ce: "Lalle ne, nã yi mafarki;(1) nã ga shãnu bakwai mãsu ƙiba, waɗansu bakwai rãmammu, sunã cin su, da zangarku bakwai kõre-kõre da waɗansu ƙeƙasassu. Yã kũ jama´a! Ku yi mini fatawa a cikin mafarkĩna, idan kun kasance ga mafarki kunã fassarawa." [12.44] Suka ce: "Yãye-yãyen mafarki ne, kuma ba mu zamo masana ga fassarar yãye-yãyen mafarki ba." [12.45] Kuma wannan da ya kuɓuta daga cikinsu ya ce: a bãyan yã yi tunãni a lõkaci mai tsawo, "Nĩ, inã bã ku lãbãri game da fassararsa. Sai ku aike ni." [12.46] "Yã Yũsufu! Yã kai mai yawan gaskiya! Ka yi mana fatawa a cikin shãnu bakwai mãsu ƙiba, waɗansu bakwai rãmammu sunã cin su, da zangarku bakwai kõrãye da waɗansu ƙeƙasassu, tsammãnĩna in kõma ga mutãne, tsammãninsu zã su sani." [12.47] Ya ce: "Kunã shũka, shħkara bakwai tutur, sa´an nan abin da kuka girbe, sai ku bar shi, a cikin zanganniyarsa,(1) sai kaɗan daga abin da kuke ci." [12.48] "Sa´an nan kuma waɗansu bakwai mãsu tsanani su zo daga bãyan wancan, su cinye abin da kuka gabãtar dõminsu, fãce kaɗan daga abin da kuke ãdanãwa." [12.49] "Sa´an nan kuma wata shħkara ta zo daga bãyan wancan, a cikinta ake yi wa mutãne ruwa mai albarka, kuma a cikinta suke mãtsar abin sha." [12.50] Kuma sarkin ya ce: "Ku zo mini da shi." To, a lõkacin da manzo ya je masa (Yũsufu), ya ce: "Ka kõma zuwa ga uban gidanka, sa´an nan ka tambaye shi; Mħnene hãlin mãtãyen nan waɗanda suka yanyanke hannãyensu? Lalle ne Ubangijĩna ne Masani game da kaidinsu." [12.51] Ya ce: "Mħne ne babban al´amarinku, a lõkacin da kaka nħmi Yũsufu daga kansa?" Suka ce: "Tsarki ga Allah yake! Ba mu san wani mummũnan aiki a kan saba." Mãtar Azĩz ta ce: "Yanzu fa gaskiya(2) ta bayyana. Nĩ ce nã nħme shi daga kansa. Kuma lalle ne shĩ, haƙĩƙa, yanã daga mãsu gaskiya. [12.52] "Wancan ne, dõmin ya san cħwa lalle ne ni ban yaudare shi ba a ɓõye, kuma lalle Allah bã Ya shiryar da kaidin mayaudara." [12.53] "Kuma bã ni kuɓutar da kaina. Lalle ne rai, haƙĩƙa, mai yawan umurni ne da mummũnan aiki, fãce abin da Ubangjina Ya yi na rahama. Lalle Ubangjina Mai gãfara ne, Mai jin ƙai." [12.54] Kuma sarkin ya ce: "Ku zo mini da shi in kħɓe shi ga kaina." To, a lõkacin da Yũsufu ya yi masa magana sai ya ce: "Lalle ne kai a yau, a gunmu, mai daraja ne, amintacce."(1) [12.55] Ya ce: "Ka sanya ni a kan taskõkin ƙasa. Lalle ne nĩ, mai tsarħwa ne, kuma masani." [12.56] Kuma kamar wancan ne Muka bãyar da ĩko ga Yũsufu a cikin ƙasa(2) yanã sauka a inda duk yake so. Munã sãmun wanda Muke so da rahamar Mu, kuma bã Mu tõzartar da lãdar mãsu kyautatawa. [12.57] Kuma lalle lãdar Lãhira ce mafi alhħri ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka kasance mãsu taƙawa. [12.58] Kuma ´yan´uwan(3) Yũsufu suka jħ, sa´an nan suka shiga a gare shi, sai ya gãne su, alhãli kuwa su, sunã mãsu musunsa. [12.59] Kuma a lõkacin da ya yi musu tattali da tattalinsu, ya ce: "Ku zo mini da wani ɗan´uwa nãku daga ubanku. Ba ku gani ba cħwa lalle ne nĩ, inã cika ma´auni, kuma nĩ ne mafi alhħrin mãsu saukarwa?" [12.60] "Sa´an nan idan ba ku zo mini da shĩ ba, to, bãbu awo a gare ku a wurĩna, kuma kada ku, kasance ni." [12.61] Suka ce: "Zã mu nħme shi daga ubansa. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu aikatãwa ne." [12.62] Kuma ya ce wa yaransa, "Ku sanya hajjarsu a cikin kãyansu, tsammãninsu sunã gãne ta idan sun jũya zuwa ga mutãnensu, tsammãninsu, zã su kõmo." [12.63] To, a lõkacin da suka kõma zuwa ga ubansu, suka ce: "Yã bãbanmu! An hana mu awo sai ka aika ɗan´uwanmu tãre da mu. Zã mu yi awo. Kuma lalle ne, haƙĩƙa mũ, mãsu lũra da Shi ne." [12.64] Ya ce: "Ashe, zã ni amince muku a kansa? Fãce dai kamar yadda na amince muku a kan ɗan´uwansa daga gabãni, sai dai Allah ne Mafĩfĩcin mãsu tsari, kuma Shĩ ne Mafi rahamar mãsu rahama." [12.65] Kuma a lõkacin da suka bũɗe kãyansu, suka sãmi hajjarsu an mayar musu da ita, suka ce: "Yã bãbanmu! Ba mu zãlunci! Wannan hajjarmu ce an mayar mana da ita, kuma mu nħmo wa iyalinmu abinci, kuma mu kiyãye ɗan´uwanmu, kuma mu ƙãra awon kãyan rãƙumi guda, wancan awo ne mai sauki." [12.66] Ya ce: "Bã zan sake shi tãre da kũ ba, sai kun kawo mini alkawarinku baga Allah, haƙĩƙa, kunã dawo mini da shi, sai fa idan an kħwaye ku." To, a, lõkacin da suka yi mãsa alkawari, ya ce: "Allah ne wakĩli a kan abin da muke faɗa." [12.67] Kuma ya ce: "Yã ɗiyana! Kada ku shiga ta ƙõfa guda, ku shiga ta ƙõfõfi dabam-dabam,(1) kuma bã na wadãtar muku kõme daga Allah. Bãbu hukunci fãce daga Allah, a gare Shi na dõgara, kuma a gare Shi mãsu dõgara sai su dõgara." [12.68] Kuma a lõkacin da suka shiga daga inda ubansu ya umurce su wani abu bai kasance yanã wadãtarwa ga barinsu daga Allah ba fãce wata bukata ce a ran Yãƙũbu, ya bayyana ta. Kuma lalle ne shĩ, haƙĩƙa, ma´abũcin wani ilmi ne ga abin da Muka sanar da shi, kuma mafi yawan mutãne ba su sani ba. [12.69] Kuma a lõkacin da suka shiga wajen Yũsufu, ya tattara ɗan´uwansa zuwa gare shi, ya ce: "Lalle nĩ ne ɗan´uwanka, sabõda haka kada ka yi baƙin ciki da abin da suka kasance sunã aikatãwa." [12.70] Sa´an nan a lõkacin da ya yi musu tattali da tattalinsu, sai ya sanya ma´auni a cikin kãyan ɗan´uwansa sa´an nan kuma mai yħkuwa ya yi yħkuwa," Yã kũ ãyari! lalle ne, haƙĩƙa kũ ɓarãyi ne." [12.71] Suka ce: kuma suka fuskanta zuwa gare su: "Mħne ne kuke nħma?" [12.72] Suka ce: "Munã nħman ma´aunin sarki. Kuma wanda ya zo da shi, yanã da kãyan rãkumi ɗaya, kuma ni ne lãmuni game da shi." [12.73] Suka ce: "Tallahi! Lalle ne, haƙĩƙa, kun sani, ba mu zo don mu yi ɓarna a cikin ƙasa ba, kuma ba mu kasance ɓarãyi ba." [12.74] Suka ce: "To mħne ne sakamakonsa idan kun kasance maƙaryata?" [12.75] Suka ce: "Sakamakonsa, wanda aka same shi a cikin kãyansa, to, shi ne sakamakonsa,(1) kamar wancan ne muke sãka wa azzãlumai." [12.76] To, sai ya fãra (bincike) da jikunansu a gabãnin jakar ɗan´uwansa. Sa´an nan ya fitar da ita daga jakar ɗan´uwansa. Kamar wancan muka shirya wa Yũsufu. Bai kasance ya kãma ɗan´uwansa a cikin addinin (dõkõkin) sarki ba, fãce idan Allah Ya so. Munã ɗaukaka darajõji ga wanda Muka so, kuma a saman kõwane ma´abũcin ilmi akwai wani masani. [12.77] Suka ce: "Idan ya yi sãta, to, lalle ne wani ɗan´uwansa yã taɓa yin sãta a gabãninsa." Sai Yũsufu ya bõye(2) ta a cikin ransa. Kuma bai bayyana ta ba a gare su, ya ce: "Kũ ne mafi sharri ga wuri. Kuma Allah ne Mafi sani daga abin da kuke siffantãwa." [12.78] Suka ce: "Yã kai Azĩzu! Lalle ne yanã da wani ubã, tsoho mai daraja, sabõda haka ka kãma ɗayanmu amatsayinsa. Lalle ne mũ, muna ganin ka daga mãsu kyautatãwa." [12.79] Ya ce: "Allah Ya tsare mu daga mu kãma wani fãce wanda muka sãmi kãyanmu a wurinsa. Lalle ne mũ, a lõkacin nan, haƙĩƙa, azzãlumai ne." [12.80] Sabõda haka, a lõkacin da suka yanke tsammãni daga gare shi, sai suka fita sunã mãsu gãnãwa.(1) Babbansu ya ce: "Shin, ba ku sani ba cħwa lalle ne ubanku ya riƙi alkawari daga Allah a kanku, kuma daga gabanin haka akwai abin da kuka yi na sakaci game da Yũsufu? Sabõda haka, bã zan gushe daga ƙasar nan ba fãce ubana yã yi mini izni, kõ kuwa Allah Ya yi hukunci a gare ni, kuma Shĩ ne Mafi alhħrin mahukunta." [12.81] "Ku kõma zuwa ga ubanku, ku gaya masa: Yã bãbanmu, lalle ne ɗanka yã yi sãta, kuma ba mu yi shaida ba fãce da abin da muka sani, kuma ba mu kasance mun san gaibu ba." [12.82] "Kuma ka tambayi alƙarya wadda muka kasance a cikinta da ãyari wanda muka gabãto a cikinsa, kuma lalle ne haƙĩƙa, mũ mãsu gaskiya ne." [12.83] Ya ce: "ôa, zukatanku sun ƙawãta wani al´amari a gare ku. Sai haƙuri mai kyãwo, akwai tsammãnin Allah Ya zo mini da su gabã ɗaya ( Yũsufu da ´yan´uwansa). Lalle ne Shĩ ne Masani, Mai hikima." [12.84] Kuma ya jũya daga gare su, kuma ya ce: "Yã baƙin cikina a kan Yũsufu!" Kuma idãnunsa suka yi fari sabõda huznu sa´an nan yanã ta haɗħwar haushi. [12.85] Suka ce: "Tallahi! Bã zã ka gushe ba, kanã ambaton Yũsufu,(2) har ka kasance Mai rauni ƙwarai, kõ kuwa ka kasance daga mãsu halaka." [12.86] Ya ce: "Abin sani kawai, inã kai ƙarar baƙin cikĩna da sunõna zuwa ga Allah, kuma na san abin da ba ku sani ba daga Allah." [12.87] "Yã ɗiyãna! Sai ku tafi ku nħmo lãbãrin Yũsufu(1) da ɗan´uwansa. Kada ku yanke tsammãni daga rahamar Allah. Lalle ne, bãbu Mai yanke tsammãni daga rahamar Allah fãce mutãne kãfirai." [12.88] Sa´an nan a lõkacin da suka shiga gare shi suka ce: "Yã kai Azĩzu! Cũta ta shãfe mu, mũ da iyãlinmu, iuma mun zo da wata hãja maras kuma. Sai ka cika mana ma´auni, kuma ka yi sadaka a gare mu. Lalle ne Allah Yanã sãka wa mãsu yin sadaka.(2) " [12.89] Ya ce: "Shin, kun(3) san abin da kuka aikata ga Yũsufu da ɗan´uwansa a lõkacin da kuke jãhilai?" [12.90] Suka ce: "Shin kõ, lalle ne, kai ne Yũsufu?" Ya ce: "Nĩ ne Yũsufu, kuma wannan shĩ ne ɗan´uwãna. Haƙĩƙa Allah Yã yi falala a gare mu. Lalle ne, shi wanda ya bi Allah da taƙawa, kuma ya yi haƙuri, to, Lalle ne Allah bã Ya tõzarta lãdar mãsu kyautatãwa." [12.91] Suka ce: "Tallahi! Lalle ne haƙĩƙa, Allah Yã zãɓe ka a kanmu, kuma lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, mãsu kuskure." [12.92] Ya ce: "Bãbu zargi a kanku a yau, Allah Yanã gãfartã muku, kuma Shĩ ne Mafi rahamar mãsu rahama." [12.93] "Ku tafi da rĩgãta wannan, sa´an nan ku jħfa ta a kan fuskar mahaifina, zai kõma mai gani. Kuma ku zo mini da iyãlinku bãki ɗaya." [12.94] Kuma, a lõkacin da ãyari(4) ya bar (Masar) ubansa ya ce: "Lalle ne nĩ inã shãƙar iskar Yũsufu, bã dõmin kunã ƙaryata ni ba." [12.95] Suka ce: "Tallahi lalle ne, kai, haƙĩƙa, kanã a cikin ɓatarka daɗaɗɗa." [12.96] Sa´an nan a lõkacin da mai bãyar da bushãra ya je, sai ya jħfa ta a kan fuskarsa, sai ya kõma mai gani. Ya ce: "Shin, ban gaya muku ba, lalle ne, ni inã sanin abin da ba ku sani ba, daga Allah?" [12.97] Suka ce: "Yã ubanmu!(1) ka nħma mana gãfara ga zunubanmu, lalle ne mũ, mun kasance mãsu kuskure." [12.98] Ya ce: "Da sannu zã ni nħma muku gãfara daga Ubangijina. Shi ne Mai gãfara, Mai jin ƙai." [12.99] Sa´an nan a lõkacin(2) da suka shiga gun Yũsufu, yã tattara mahaifansa biyu a gare shi, kuma ya ce: "Ku shiga Masar in Allah Ya so, kuna amintattu." [12.100] Kuma ya ɗaukaka iyãyensa biyu a kan karaga, sa´an nan suka fãɗi a gare shi, suna mãsu sujada.(3) Kuma ya ce: "Ya bãbãna! Wannan ita ce fassarar mafarkin nan nãwa. Lalle ne Ubangijina Ya sanya shi ya tabbata sõsai, kuma lalle ne Ya kyautata game da ni a lõkacin da Ya fitar da ni daga kurkuku. Kuma Ya zo da ku daga ƙauye, a bãyan Shaiɗan yã yi fisgar ɓarna a tsakãnĩna da tsakãnin ´yan´uwana. Lalle ne Ubangijina Mai tausasawa ne ga abin da Yake so. Lalle ne Shĩ, Shĩ ne Masani, Mai hikima." [12.101] "Yã Ubangijina(4) lalle ne Kã bã ni daga mulki, kuma Kã sanar da ni daga fassarar lãbaru. Ya Mahaliccin sammai da ƙasa! Kai ne Majiɓincĩna a dũniya da Lãhira Ka karɓi raina inã Musulmi, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai." [12.102] Wannan daga(5) lãbarun gaibi ne, Munã yin wahayinsa zuwa gare ka, kuma ba ka kasance a wurinsu ba a lõkacin da suke yin niyyar zartar da al´amarinsu, alhãli sunã yin mãkirci. [12.103] Kuma mafi yawan mutãne ba su zama mãsu ĩmãni ba ,kõ da kã yi kwaɗayin haka. [12.104] Kuma bã ka tambayar su wata lãdã a kansa. Shĩ bai zama ba fãce ambato dõmin halittu. [12.105] Kuma da yawa, wata ãyã a cikin sammai da ƙasa sunã shũɗħwa a kanta kuma sũ, sunã bijirħwa daga gare ta. [12.106] Kuma mafi yawansu ba su yin ĩmãni da Allah fãce kuma sunã mãsu shirki. [12.107] Shin fa, sun amince cħwa wata masĩfa daga azãbar Allah ta zo musu ko kuwa Tãshin Ƙiyãma ta zo musu kwatsam, alhãli sũ ba su sani ba? [12.108] Ka ce: "Wannan ce hanyãta(1) ; inã kira zuwa ga Allah a kan basĩra, nĩ da waɗanda suka bĩ ni, kuma tsarki ya tabbata ga Allah! Nĩ kuma, ban zama daga mãsu shirki ba." [12.109] Kuma ba Mu aika ba a gabãninka fãce mazãje, Munã wahayi zuwa gare su, daga mutãnen ƙauyuka. Shin fa, ba su yi tafiya a cikin ƙasa ba, dõmin su dũba yadda ãƙibar waɗanda suka kasance daga gabãninsu ta zama? Kuma lalle ne gidan Lãhira shĩ ne mafi alhħri ga waɗanda suka yi taƙawa? Shin fa, bã ku hankalta? [12.110] Har a lõkacin da Manzanni suka yanke tsammãni, kuma suka yi zaton cħwa an jingina su ga ƙarya, sai taimakonMu ya je masu, sa´an nan Mu tsħrar da wanda Muke so, kuma bã a mayar da azãbarMu daga mutãne mãsu laifi. [12.111] Lalle ne haƙĩƙa abin kula yã kasance a cikin ƙissoshinsu ga masu hankali. Bai kasance wani ƙirƙiran lãbãri ba kuma amma shi gaskatãwa ne ga abin da yake a gaba gare shi, da rarrabħwar dukan abũbuwa, da shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suka yi ĩmãni. @AR RA'D Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [13.1] A. L̃. M̃. R. Waɗancan ayõyin littãfi ne, kuma abin da aka saukar gare ka daga Ubangijinka ne gaskiya, kuma amma mafi yawan mutãne bã su yin ĩmãni. [13.2] Allah Shi ne wanda Ya ɗaukaka sammai, bã da ginshiƙai ba waɗanda kuke ganin su. Sa´an nan kuma Ya daidaita a kan Al´arshi, kuma Ya hõre rãnã da watã, kõwane yanã gudãna zuwa ga ajali ambatacce. Yanã shirya al´amari, Yanã rarrabe ãyõyi daki-daki, mai yiwuwa ne ku yi yaƙĩni da haɗuwa da Ubangijinku. [13.3] Kuma shĩ, ne wanda Ya shimfiɗa kasa, kuma Ya sanya duwãtsu da kõguna a cikinta, kuma daga dukan ´ya´yan itãce Ya sanya ma´aura biyu cikinsu. Yanã sanya dare ya rufe yini. Lalle ne a cikin wancan, haƙĩƙa akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin tunãni. [13.4] Kuma a cikin ƙasa akwai yankuna mãsu maƙwabtaka, da gõnaki na inabõbi da shũka da dabĩnai iri guda, da waɗanda bã iri guda ba, anã shayar da su da ruwa guda. Kuma Munã fĩfĩta sãshensu a kan sãshe a wajen ci. Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga muiãne waɗanda suke hankalta. [13.5] Kuma idan ka yi mãmãki, to, mãmãkin kam shi ne maganarsu, "Shin, idan muka kasance turɓãya, zã mu zama a cikin wata halitta sãbuwa?" Waɗancan ne waɗanda suka kãfirta da Ubangijinsu, kuma waɗanda akwai ƙuƙumai a cikin wuyõyinsu, kuma waɗancan ne abõkan wuta. Sũ, a cikinta, mãsu dawwama ne. [13.6] Kuma sunã nħman ka da gaggãwa da azãba a gabãnin rahama, alhãli kuwa abũbuwan misãli sun gabãta a gabãninsu. Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Ma´abũcin gãfara ne ga mutãne a kan zãluncinsu, kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Mai tsananin uƙũba ne. [13.7] Kuma waɗanda suka kãfirta sunã cħwa don me ba a saukar da wata ãyã a gare shi ba daga Ubangijinsa? Abin sani kawai, kai dai mai gargaɗi ne kuma a cikin kõwaɗanne mutãne akwai mai shiryarwa. [13.8] Allah Yanã sanin abin da kõwace mace take ɗauke da shi a cikinta da abin da mahaifu suke ragħwa(1) da abin da suke ƙãrãwa. Kuma dukkan kõme, a wurinSa, da gwargwado yake. [13.9] Shi ne Masanin fake da bayyane, Mai girma, Maɗaukaki. [13.10] Daidai ne daga gare ku, wanda ya asirta magana da wanda ya bayyana game da ita, da wanda yake shi mai nħman ɓõyewa ne da dare, da mai bayyana a cikin ƙãwalwalniyar(2) rãna da rãna. [13.11] (Kowannenku) Yanã da waɗansu malã´iku mãsu maye wa jũna a gaba gare shi da bãya gare shi, sunã tsare shi daga umurnin Allah. Lalle ne Allah bã Ya canja abin da yake ga mutãne sai sun canja abin da yake ga zukatansu. Kuma idan Allah Ya yi nufin wata azãba game da mutãne, to, bãbu mai mayar da ita, kuma bã su da wani majiɓinci(3) baicin Shi. [13.12] Shĩ ne Wanda Yake nũna muku walƙiya dõmin tsõro da tsammãni, kuma Ya ƙãga halittar girãgizai mãsu nauyi. [13.13] Kuma arãdu tanã tasbĩhi game da gõde Masa, da malã´iku dõmin tsoronsa. Kuma Yanã aiko tsãwawwaki, sa´an nan Ya sãmi wanda Yake so da su alhãli kuwa sũ, sunã jãyayya a cikin (al´amarin) Allah kuma shĩ ne mai tsananin hĩla.(4) [13.14] Yanã da kiran gaskiya, kuma waɗanda (kãfirai) suke kira baicinsa, bã su karɓa musu da kõme fãce kamar mai shimfiɗa tãfukansa zuwa ga ruwa (na girgije) dõmin (ruwan) ya kai ga bãkinsa, kuma shi bã mai kaiwa gare shi ba. Kuma kiran kãfirai (ga wanin Allah) bai zama(1) ba fãce yanã a cikin ɓata. [13.15] Kuma sabõda Allah wanda yake a cikin sammai da ƙasa suke yin sujada, so da ƙi, kuma da inuwõyinsu, a sãfe da maraice. [13.16] Ka ce: "Wãne ne Ubangijin sammai da ƙasa?" Ka ce: "Allah". Ka ce: "Ashe fa, kun riƙi waɗansu masõya baicin Shi, waɗanda ba su mallaka wa kansu wani amfãni ba kuma haka bã su tũre wata cũta?" Ka ce: "Shin makãho da mai gani sunã daidaita? Kõ shin duhu da haske sunã daidaita? ko sun sanya ga Allah waɗansu abõkan tãrayya waɗanda suka yi halitta kamar halittarSa sa´an nan halittar ta yi kama da jũna a gare su?" Ka ce: "Allah ne Mai halitta kõme kuma Shĩ ne Maɗaukaki, Marinjãyi." [13.17] Ya saukar da ruwa daga sama(2) , sai magudanai suka gudãna da gwargwadonsu. Sa´an nan kõgi ya ɗauki kumfa mai ƙãruwa, kuma daga abin da suke zuga a kansa (azurfa ko zinari kõ ƙarfe) a cikin wuta dõmin nħman ado kõ kuwa kãyan ɗãki akwai kumfa misãlinsa (kumfar ruwa). Kamar wancan ne Allah Yake bayyana gaskiya da ƙarya. To, amma kumfa, sai ya tafi ƙħƙasasshe, kuma amma abin da yake amfãnin mutãne sai ya zauna a cikin ƙasa. Kamar wancan ne Allah Yake bayyana misãlai. [13.18] Ga waɗanda(3) suka karɓa wa Ubangijinsu akwai abu mafi kyau a gare su, kuma waɗanda suke ba su karɓa Masa ba, to, lalle dã sunã da abin da yake a cikin ƙasa gaba ɗaya da misãlinsa tãre da shi, haƙĩƙa, dã sun yi fansa da shi. Waɗancan sunã da mummunan bincike kuma matabbatarsu Jahannama ce, kuma tir da ita ta zama shimfida. [13.19] Shin, fa, wanda yake sanin cħwa lalle abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka ne gaskiya yanã zama kamar wanda yake makãho? Abin sani kawai masu hankali sũ ke yin tunãni. [13.20] Sũ ne waɗanda suke cikãwa da alkawarin Allah, kuma bã su warware alkawari. [13.21] Kuma sũ ne waɗanda suke sãdar da abin da Allah Ya yi umurni da shi dõmin a sãdar da shi kuma sunã tsõron Ubangijinsu, kuma sunã tsõron mummũnan bincike. [13.22] Kuma waɗanda suka yi haƙuri dõmin nħman yardar Ubangijinsu, kuma suka tsayar da salla, kuma suka ciyar da abin da Muka azurta su da shi, a asirce da bayyane, kuma sunã tunkuɗe mummunan aiki da mai kyau. Waɗancan sunã da ãƙibar gida mai kyau. [13.23] Gidãjen Aljannar zama sunã shigarsu, sũ da waɗanda suka kyautatu daga iyãyensu, da mãtansu da zũriyarsu. Kuma malã´iku sunã shiga zuwa gunsu ta kõwace kõfa. [13.24] "Aminci(1) ya tabbata a kanku sabõda abin da kuka yi wa haƙuri. Sãbõda haka madalla da ni´imar ãƙibar gida." [13.25] Kuma waɗanda(2) suka warware alkawarin Allah daga bãyan ƙulla shi, kuma sunã yanke abin da Allah Ya yi umurni da shi dõmin a sãdar da shi kuma sunã ɓarna a cikin ƙasar. Waɗancan sunã da wata la´ana, kuma sunã da mũnin gida. [13.26] Allah ne Yake(3) shimfiɗa arziki ga wanda Yake so, kuma Yanã ƙuntatãwa. Kuma sun yi farin ciki da rãyuwar dũniya, alhali kuwa rãyuwar dũniya ba ta zama ba dangane ga ta Lãhira fãce jin dãɗi kaɗan. [13.27] Kuma Waɗanda suka kãfirta, sunã cħwa, "Don me ba a saukar da wata ãyã ba a kansa daga Ubangijinsa?" Ka ce: "Lalle ne Allah Yanã ɓatar da wanda Yake so kuma Yanã shiryar da wanda ya tũba zuwa gare shi." [13.28] Waɗanda suka yi ĩmãni kuma zukãtansu sukan natsu da ambaton Allah.(4) To, da ambaton Allah zukãta suke natsuwa. [13.29] Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata aiki nagari, farin ciki yã tabbata a gare su, da kyakkyawar makõma. [13.30] Kamar wancan ne Muka aika ka a cikin al´umma wanda take waɗansu al´ummai sun shũɗe daga gabaninta, dõmin ka karanta musu abin da Muka yi wahayi zuwa a gare ka, alhãli kuwa sũ, sunã kãfirta da Rahaman.(1) Ka ce: "Shi ne Ubangijĩna, bãbu abin, bautãwa fãce Shi, a gare Shi na dõgara, kuma zuwa gare Shi tũbãta take." [13.31] Kuma dã lalle an saukar da wani littafi abin karatu wanda ake tafiyar da duwãtsu game da shi, kõ kuma aka yanyanke ƙasa da shi, ko kuwa aka yi magana da matattu da shi (dã ba su yi ĩmãni ba). ôa ga Allah al´amari yake gabã ɗaya! Shin fa, waɗanda suka yi ĩmãni ba su yanke tsammãni ba da cħwa da Allah Yã so, dã Yã shiryar da mutãne gabã ɗaya? Kuma waɗanda suka yi kãfirci ba zã su gushe ba wata masĩfa tanã samun su sabõda abin da suka aikata, kõ kuwa ka saukã(2) kusa da gidãjħnsu, har wa´adin Allah ya zo. Kuma lalle ne Allah bã ya sãɓã wa lõkacin alkawari. [13.32] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili da Manzanni kãfinka, sai Na yi jinkiri ga waɗanda suka kãfirta, sa´an nan Na kãma su. To, yãya uƙũbãta take? [13.33] Shin fa, wanda shĩ Yake tsaye a kan kõwane rai game da abin da ya tanada (zai zama kamar wanda ba haka ba)? Kuma suka sanya abõkan tãrayya ga Allah! Ka ce: "Ku ambaci sũnãyensu."Ko kunã bai wa Allah lãbãri ne game da abin da bai sani ba a cikin ƙasa? Kõ da bayyananniyar magana kuke yin shirka, (banda a cikin zũciya)? ôa, an dai ƙawãta wa waɗanda suka kafirta mãkircinsu kuma an kange su daga hanya. Kuma wanda Allah Ya ɓatar to, bãbu wani mai shiryarwa a gare shi!" [13.34] Sunã da wata azãba a cikin rãyuwar dũniya, kuma haƙĩƙa azãbar Lãhira ce mafi tsanani kuma bãbu wani mai tsare su daga Allah. [13.35] Misãlin Aljanna wadda aka yi alkawarinta ga mãsu taƙawa, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinta. Abincinta yana madawwami da inuwarta. Waccan ce ãƙibar waɗanda suka yi taƙawa, kuma ãƙibar kãfirai, ita ce wuta, [13.36] Kuma waɗanda Muka bã su Littãfi sunã farin ciki da abin da aka saukar zuwa gare ka, kuma daga ƙungiyõyi akwai mai musun sãshensa. Ka ce: "Abin sani kawai, an umurce ni da in bauta wa Allah kuma kada in yi shirka da Shi, zuwa gare Shi nake kira, kuma zuwa gare Shi makõmata take." [13.37] Kuma kamar wancan ne Muka saukar da shi,(1) Hukunci a cikin Lãrabci. Kuma lalle ne idan kã bi son zuciyõyinsu a bãyan abin da ya zo maka na ilmi, bãbu wani masõyi a gare ka mai kãre ka daga Allah, kuma bãbu matsari. [13.38] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika waɗansu manzanni, daga gabãninka, kuma Muka sanya mãtan aure a gare su da zũriyya, kuma ba ya kasancħwa ga wani Manzo ya zo da wata ãyã, sai da iznin Allah. Ga kõwane ajali(2) akwai littãfi. [13.39] Allah Yanã shafe abin da Yake so, kuma Yanã tabbatarwa kuma a wurinsa asalin Littãfin yake. [13.40] Kuma imma lalle Mu nũna(3) maka sãshen abin da Muke yi musu wa´adi, kõ kuwa lalle Mu karɓi ranka to abin sani kawai iyarwa ce a kanka, kuma hisãbi yana gare Mu. [13.41] Shin, kuma ba su gani ba cħwa lalle ne, Muna jħ wa ƙasar (su), Munã rage ta daga għfunanta? Kuma Allah ne Yake yin hukuncinsa. Babu mai bincike ga hukuncinsa. Kuma shĩ ne Mai gaggãwar sakamako.(4) [13.42] Kuma lalle ne waɗanda suke a gabãninsu sun yi mãkirci. To, ga Allah mãkircin yake gabã ɗaya. Ya san abin da kõwane rai yake tãnada. Kuma kãfirai zã su sani, ga wane ãƙibar gida take. [13.43] Kuma waɗanda suka kãfirta sunã cħwa: "Ba a aiko ka ba." Ka ce, "Allah Yã isa zama shaida a tsakãnina da tsakãninku da wanda yake a wurinsa akwai ilmin(1) Littãfi." @IBRAHIM Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [14.1] A. L̃. R. Littãfi ne mun saukar da shi zuwa gare ka dõmin ka fitar da mutãne daga duhunhuna zuwa ga haske, da iznin Ubangijinsu, zuwa ga tafarkin Mabuwãyi,Abin gõdħwa. [14.2] Allah wanda Yake Yanã da abin da ke cikin sammai da cikin ƙasa. Kuma bone yã tabbata ga kãfirai daga azãba mai tsanani. [14.3] Waɗanda suka fi son rãyuwar dũniya fiye da ta Lãhira, kuma sunã kangħwa daga hanyar Allah, kuma sunã nħman ta karkace. Waɗancan na a cikin ɓata mai nĩsa. [14.4] Kuma ba Mu aika wani Manzo ba fãce da harshen mutãnensa dõmin ya bayyanã musu. Sa´an nan Allah Ya ɓatar da wanda Yake so kuma Ya shiryar da wanda Yake so, kuma shĩ ne Mabuwãyi, Mai hikima. [14.5] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika Mũsã game, da ãyõin Mu cħwa, "Ka fitar da mutãnenka daga duhu zuwa ga haske. Kuma ka tunar musu da kwãnukan (masĩfun) Allah." Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi dõmin dukan mai yawan haƙuri, mai gõdiya. [14.6] Kuma a lõkacin da Mũsã yace wa mutãnensa, "Ku tuna ni´imar Allah a kanku a lõkacin da Ya tsĩrar da ku daga mutãnen Fir´auna, sunã yi muku mummunar azãba, kuma sunã yanyanka ɗiyanku, kuma sunã rãyar da mãtanku. Kuma a cikin wancan akwai jarrabãwa mai girmã daga Ubangijinku." [14.7] Kuma a lõkacin da Ubangijinku Ya sanar, "Lalle ne idan kun gõde, haƙĩƙa, Inã ƙãra muku, kuma lalle ne idan kun kãfirta haƙĩƙa azãbãta, tabbas, mai tsanani ce." [14.8] Kuma Mũsã ya ce: "Idan kun kãfirta kũ da waɗanda suke a cikin ƙasa, gabã ɗaya, to, lalle ne Allah haƙĩƙa Mawadãci ne, Mai yawan gõdiya." [14.9] Shin lãbãrin waɗanda suke a gabãninku, mutãnen Nũhu da Ãdãwa da Samũdawa bai zomuku ba? Kuma da waɗanda suke daga bãyansu bãbu wanda yake sanin su fãce Allah? Manzanninsu sun jħ musu da hujjõji mabayyana, sai suka mayar da hannayensu a cikin bãkunansu, kuma suka ce: "Lalle ne mũ, mun kãfirta da abinda aka aiko ku da shi. Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa munã a cikin shakka da abin do kuke kiran mu zuwa gare shi, mai sanya kõkanto." [14.10] Manzanninsu suka ce "Ashe, akwai shakka a cikin (sha´anin) Allah, Mai ƙãga halittar sammai da ƙasa Yanã kiran ku dõmin Ya gãfarta muku zunubanku, kuma Ya jinkirtã muku zuwa ga ajali ambatacce?" Suka ce: "Ba ku zama ba fãce mutãne misãlinmu kuma nufinku ku kange mu daga abin da iyãyenmu suka kasance sunã bautãwa sai ku zo mana da dalĩli mabayyani." [14.11] Manzanninsu suka ce musu, "Bã mu zama ba fãce mutãne misãlinku, kuma amma Allah Yanã yin falala a kan wanda Yake so daga bãyinsa, kuma bã ya kasancħwa a gare mu, mu zo muku da wani dalĩli fãce da iznin Allah. Kuma ga Allah sai mũminai su dõgara. [14.12] "Kuma mħne ne a gare mu, bã zã mu dõgara ga Allah ba, alhãli kuwa haƙĩƙa Yã shiryar da mu ga hanyõyinmu? Kuma lalle ne munã yin haƙuri a kan abin da kuka cũtar da mu, kuma ga Allah sai mãsu dõgaro su dõgara." [14.13] Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce wa Manzanninsu, "Lalle ne munã fitar da ku daga ƙasarmu, kõ kuwa haƙĩƙa, kunã kõmowã a cikin addininmu." Sai Ubangijinsu Ya yi wahayi zuwa gare su, "Lalle ne, Munã halakar da azzãlumai." [14.14] Kuma haƙĩƙa, Munã zaunar da ku ga ƙasa a bãyansu. Wancan ne abin gargaɗi ga wanda ya ji tsõron matsayiNa, kuma ya ji tsõron ƙyacħwãTa. [14.15] Kuma suka yi addu´ar alfãnu.(1) Kuma kõwane kangararre mai tsaurin kai ya tãɓe. [14.16] Daga bãyansa akwai Jahannama, kuma anã shãyar da shi daga wani ruwa, surkin jini. [14.17] Yanã kwankwaɗarsa, kuma bã ya jin sauƙin haɗiyarsa, kuma mutuwa ta jħ masa daga kõwane wuri kuma bai zama mai mutuwa ba, kuma daga bãyansa akwai azãba mai kauri. [14.18] Misãlin waɗanda suka kãfirta da Ubangijinsu, ayyukansu sun yi kama da tõka wadda iska ta yi tsananin bugãwa da ita a cikin yini mai gũguwa. Ba su iya amfãni daga abin da suka yi tsirfa a kan kõme.Wancan ita ce ɓata mai nĩsa. [14.19] Shin, ba ka gani ba cħwa lalle ne Allah Yã halicci sammai bakwai da ƙasa da mallakarSa.(1) Idan Yã so zai tafiyar da ku, kuma Ya zo da wata halitta sãbuwa. [14.20] Kuma wancan bai zama mabuwãyi ba ga Allah. [14.21] Kuma suka bayyana ga Allah gabã daya, sai mãsu rauni suka ce wa waɗanda suka kangara, "Lalle ne mũ, mun kasance mãsu bi a gare ku, to, shin, kũ mãsu kãrewa ga barinmu ne daga azãbar Allah daga wani abu?"(2) Suka ce: "Dã Allah Ya shiryar da mu, dã mun shiryar da ku, daidai ne a kanmu, mun yi rãki ko mun yi haƙuri ba mu da wata mafaka." [14.22] Kuma Shaiɗan ya ce a lõkacin da aka ƙãre al´amarin, "Lalle ne Allah Ya yi muku wa´adi, wa´adin gaskiyã, kuma na yi muku wa´adi, sa´an nan na sãɓã muku. Kuma bãbu wani dalĩli a gare ni a kanku fãce na kirã ku, sa´an nan kun karɓã mini. Sabõda haka kada ku zarge ni, kuma ku zargi kanku. Ban zama mai amfaninku ba, kuma ba ku zama mãsu amfãnĩna ba. Lalle na barranta da abin da kuka haɗã ni da shi gabanin wannan (matsayi). Lalle azzãlumai sunã da azãba mai raɗaɗi."(3) [14.23] Kuma aka shigar da waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, a gidãjen Aljanna, kõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu sunã madawwamã a cikinsu da iznin Ubangijinsu, gaisuwarsu a cikinta "Salãm", (wãtau Aminci). [14.24] Shin, ba ka ganĩ ba, yadda Allah Ya buga wani mĩsali, kalma mai kyau(4) kamar itãciya ce mai kyau, asalinta yanã tabbatacce, kuma rħshenta yanã cikin sama? [14.25] Tanã bãyar da abincinta a kõwane lõkaci da iznin Ubangijinta! Kuma Allah Yanã buga misãli ga mutãne, mai yiwuwã ne, sunã tunãwa. [14.26] Kuma misalin kalma mummũnã(1) kamar itãciya mummũnã ce, an tumɓuke ta daga bisa ga ƙasa, bã ta da wata tabbata. [14.27] Allah Yanã tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni da magana tabbatacciya a cikin rãyuwar dũniya, da cikin Lãhira, Kuma Allah Yanã ɓatar da azzãlumai, kuma Allah Yanã aikata abin da Yake so. [14.28] Shin ba ka lura ba da waɗanda suka musanya(2) ni´imar Allah da kãfirci kuma suka saukar da mutãnensu a gidan halakã? [14.29] Sunã ƙõnuwa a wutar jahannama, kuma tir da matabbatarsu. [14.30] Kuma suka sanya wa Allah kĩshiyõyi, dõmin ɓatarwa daga hanyarSa, Ka ce: "Ku ji dãɗi, sa´an nan, lalle ne, makõmarku Wutar ce." [14.31] Ka ce wa bãyĩNa waɗanda suka yi ĩmãni su tsayar da salla kuma su ciyar daga abin da Muka azurtã su, a asirce da bayyane, daga gabãnin wani wuni ya zo, bãbu ciniki a ciki, kuma bãbu abõtaka. [14.32] Allah ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Ya fitar game da shi, daga ´ya´yan itãce arziki dõminku kuma Ya hõrħ jirgin ruwa dõmin ya yi gudu a cikin tħku da umurninSa, kuma Ya hõrħ muku kõguna. [14.33] Kuma Ya hõrħ muku rãnã da watã sunã madawwama biyu, kuma Ya hõrħ muku dare da wuni. [14.34] Kuma Ya bã ku dukkan abin da kuka rõƙe Shi kuma idan kun ƙidaya, ni´imar Allah bã zã ku lissafe ta ba. Lalle ne mutum, haƙĩƙa, mai yawan zãlunci ne, mai yawan kãfirci. [14.35] Kuma a lõkacin da Ibrãhĩm ya ce: "Yã Ubangijina! Ka sanyã wannan gari(1) amintacce kuma Ka nĩsanta ni, nĩ da ɗiyãna daga bauta wa gumãka. [14.36] "Yã Ubangijina! Lalle ne sũ, sun ɓatar da mãsu yawa daga mutãne sa´an nan wanda ya bĩ ni, to, lalle shi, yanã daga gare ni, kuma wanda ya sãɓa mini, to, lalle ne Kai Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [14.37] "Yã Ubangijinmu! Lalle ne ni, na zaunar da zuriyata ga rãfi wanda ba ma´abũcin shũka ba, a wurin Ɗãkinka mai alfarma. Yã Ubangijinmu! Dõmin su tsayar da salla. Sai Ka sanya zukãta daga mutãne sunã gaggãwar bħgenzuwa gare su, kuma ka azurtã su daga ´ya´yan itãce, mai yiwuwã ne sunã gõdħwã." [14.38] "Yã Ubangijinmu! Lalle ne Kai Kanã sanin abin da muke ɓõyħwa, da abin da muke bayyanãwa. Kuma bãbu abin da yake ɓõyħwa ga A1lah, daga wani abu a cikin ƙasa, kuma bãbu a cikin sama." [14.39] "Gõdiyã ta tabbata ga Allah wanda Yake Ya bã ni inã a cikin tsufa Ismã´ila da Is´hãƙa. Lalle ne Ubangijina, haƙĩƙa, Mai jin addu´a ne." [14.40] "Yã Ubangijina! Ka sanyã ni mai tsayar da salla. Kuma daga zũriyyata. Yã Ubangijinmu! Kuma Ka karɓi addu´ata." [14.41] "Yã Ubangijinmu! Ka yi gãfara gare ni, kuma ga mahaifãna, kuma da mũminai, a rãnar da hisãbi yake tsayãwa." [14.42] "Kuma kada ka yi zaton Allah Mai shagalã ne daga abin da azzalumai suke aikatãwã. Abin sani kawai, Yanã jinkirta musu ne zuwa ga wani wuni, wanda idãnuwa suke fita turu-turu a cikinsa." [14.43] "Sunã mãsu gaggãwa, mãsu ɗaukaka kãwunansu zuwa sama ƙiftawar ganinsu ba ta kõmãwa gare su. Kuma zukãtansu wõfintattu."(1) [14.44] Kuma ka yi gargaɗi ga mutãne ga rãnar da azãba take jħ musu, sai waɗanda suka yi zãlunci su ce: "Yã Ubangijinmu! Ka yi mana jinkiri zuwa ga wani ajali makusanci, mu karɓa wa kiranKa, kuma mu bi Manzanni."(Allah Ya ce musu) "Ashe, ba ku kasance kun yi rantsuwã ba daga gabãni, cħwa bã ku da wata gushħwa? [14.45] "Kuma kuka zaunã a cikin gidãjen waɗanda suka zãlunci kansu, kuma ya bayyana a gare ku yadda Muka aikatã game da su, kuma Muka buga muku misãlai." [14.46] Kuma lalle sun yi mãkirci irin makircinSu kuma a wurin Allah makircinsu, yake, kuma lalle ne makircinsu yã kasance, haƙĩƙa, duwãtsu sunã gushħwã sabõda shi. [14.47] Sabõda haka, kada ka ƙarfafa zaton Allah Mai sãɓa wa´adinSa ne ga ManzanninSa. Lalle ne Allah ne Mabuwãyi, Ma´abũcin azãbar rãmuwa. [14.48] A rãnar da ake musanya ƙasa(2) bã ƙasar nan ba, da sammai kuma su bayyana ga Allah Makaɗaici, Mai tanƙwasãwa. [14.49] Kuma kana ganin mãsu laifi, a rãnar nan, sunã waɗanda aka yi wa ciri daidai a cikin marũruwa. [14.50] Rigunansu daga farar wutã ne, kuma wuta ta rufe fuskõkinsu. [14.51] Dõmin Allah Ya sãkã wa kõwane rai da abin da ya tsuwurwurta. Lalle ne, Allah Mai gaggãwar hisãbi ne. [14.52] Wannan iyarwa ce ga mutãne, kuma dõmin a yi musu gargaɗi da shi, kuma dõmin su sani cħwa, abin sani kawai, shĩ ne abin bautawa guda. Kuma dõmin masu hankali su riƙa tunãwa. @AL HIJR Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [15.1] A. L̃. R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa. [15.2] Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.(1) [15.3] Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa´an nan da sannu zã su sani. [15.4] Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne. [15.5] Wata al´umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba. [15.6] Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur´ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne." [15.7] "Dõmin me bã zã ka zo mana da malã´ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?" [15.8] Bã Mu sassaukar da malã´iku fãce da gaskiya,(2) bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba. [15.9] Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur´ãni), kuma lalle Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayħwane gare shi. [15.10] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka. [15.11] Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi. [15.12] Kamar wancan ne Muke shigar da shi(3) a cikin zukãtan mãsu laifi. [15.13] Bã su yin ĩmãni da shi,(4) kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige. [15.14] Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa. [15.15] Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. ôa, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce." [15.16] Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo. [15.17] Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa. [15.18] Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi. [15.19] Kuma ƙasa Mun mĩkħ ta kuma Mun jħfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikħli. [15.20] Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã(1) da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba. [15.21] Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne. [15.22] Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa´an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacħwa a gare shi ba. [15.23] Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashħwa kuma Mũ ne magada. [15.24] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri. [15.25] Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani. [15.26] Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja. [15.27] Kuma Aljani Mun haliccħ shi daga gabãni, daga wutar (2) iskar zafi. [15.28] Kuma a l?kacin da Ubangijinka ya ce wa mal?´iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙeƙasasshen yumɓu wanda ya canja." [15.29] "To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa(3) a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada." [15.30] Sai malã´iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya. [15.31] Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancħwa daga mãsu yin sujadar. [15.32] Ya ce: "Yã Iblĩs mħne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?" [15.33] Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja." [15.34] Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne." [15.35] "Kuma lalle ne akwai la´ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako." [15.36] Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su." [15.37] Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri." [15.38] "Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne." [15.39] Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya." [15.40] "Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake." [15.41] Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici." [15.42] "Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu." [15.43] Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma´alkawartarsu gabã ɗaya. [15.44] Tanã da ƙõfõfi bakwai,(1) ga kõwace ƙõfa akwai wani juz´i daga gare su rababbe. [15.45] Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa. [15.46] "Ku shigħ ta da aminci, kunã amintattu." [15.47] Kuma Muka ɗħbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama ´yan´uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã. [15.48] Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga cikinta ba. [15.49] Ka bai wa bãyiNa lãbari cħwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai. [15.50] Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi. [15.51] Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm. [15.52] A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne." [15.53] Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi maka bushãra game da wani yãro masani." [15.54] Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra(1) ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?" [15.55] Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni." [15.56] Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?" [15.57] Ya ce: "To, mħne ne babban al´amarinku? Yã kũ manzanni!" [15.58] Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi." [15.59] "Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya." [15.60] "Fãce mãtarsa mun ƙaddara cħwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka." [15.61] To, a lõkacin da mazannin suka jħ wa mutãnen Lũɗu, [15.62] Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba." [15.63] Suka ce: "ôa, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa." [15.64] "Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne." [15.65] "Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka umurce ku." [15.66] Kuma Muka hukunta wancan al´amarin zuwa gare shi cħwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankħwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba. [15.67] Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra. [15.68] Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni." [15.69] "Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki." [15.70] Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?" [15.71] Ya ce: "Ga waɗannan ´ya´yãna (1) idan kun kasance mãsu aikatãwa ne." [15.72] Rantsuwa da(2) rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa. [15.73] Sa´an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã. [15.74] Sa´an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu. [15.75] Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali. [15.76] Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a għfen wata hanyã tabbatacciya.(3) [15.77] Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni. [15.78] Kuma lalle ne ma´abũta Al´aika(4) sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci! [15.79] Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a għfen wani tafarki mabayyani. [15.80] Kuma lalle ne haƙĩƙa ma´abũta Hijiri(5) sun ƙaryata Manzanni. [15.81] Kuma Muka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirħwa daga gare su. [15.82] Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu. [15.83] Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba. [15.84] Sa´an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba. [15.85] Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã´a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau. [15.86] Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani. [15.87] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu(6) da Alƙur´ãni mai girma. [15.88] Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau´i-nau´i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni. [15.89] Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne." [15.90] Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,(7) [15.91] Waɗanda suka sanya Alƙur´ãni tãtsuniyõyi. [15.92] To, rantsuwa da Ubangijinka! (1) Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya. [15.93] Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa. [15.94] Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki. [15.95] Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu(2) izgili. [15.96] Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa´an nan da sannu zã su sani. [15.97] Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cħwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili). [15.98] Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada. [15.99] Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka. @AN NAHL Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [16.1] Al´amarin Allah yã zo, sabõda haka kada ku nħmi hanzartãwarsa. Tsarkin Allah ya tabbata, kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke yi na shirka. [16.2] Yanã sassaukar da malã´iku da Rũhi(3) daga umurninSaa kan wanda Yake so daga bãyinSa, cħwa ku yi gargaɗi cħwa: Lalle ne shĩ, bãbu abin bautãwa fãce Ni, sabõda haka ku bĩ Ni da taƙawa. [16.3] Ya halicci sammai da ƙasa da gaskiya. Ya ɗaukaka daga abin da suke yi na shirka. [16.4] Ya halicci mutum daga maniyyi, sai gã shi yanã mai husũma bayyananniya. [16.5] Da dabbõbin ni´ima, Ya halicce su dõminku. A cikinsu akwai abin yin ɗumi da waɗansu amfãnõni, kuma daga gare su kuke ci. [16.6] Kuma kunã da kyau a cikinsu a lõkacin da suke kõmõwa daga kĩwo da maraice da lõkacin da suke sakuwã. [16.7] Kuma sunã ɗaukar kãyanku mãsu nauyi zuwa ga wani gari, ba ku kasance mãsu isa gare shi ba, fãce da tsananin wahalar rãyuka, Lalle ne Ubangijinka ne, haƙĩƙa, Mai tausayi, Maijin ƙai. [16.8] Kuma da dawãki(1) da alfadarai da jãkuna, dõmin ku hau su, kuma da ƙawa. Kuma Yana halitta abin da ba ku sani ba. [16.9] Kuma ga Allah madaidaiciyar hanya take kuma daga gare ta akwai mai karkacħwa. Kuma da Yã so, dã Ya shiryar da ku gabã ɗaya. [16.10] Shĩ ne Wanda Ya saukar da ruwa daga sama dõminku, daga gare shi akwai abin sha, kuma daga gare shi itãce yake, a cikinsa kuke yin kĩwo. [16.11] Yanã tsirar da shũka game da shi, dõminku zaitũni da dabĩnai da inabai, kuma daga dukan ´yã´yan itãce. Lalle ne a cikin wancan haƙĩƙa, akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke yin tunãni. [16.12] Kuma Ya hõrħ muku dare da wuni da rãnã da watã kuma taurãri hõrarru ne da umurninSa. Lalle ne a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke hankalta. [16.13] Kuma abin da Ya halitta muku a cikin ƙasa, yana mai sãɓãnin launukansa. Lalle ne a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke tunãwa. [16.14] Kuma Shĩ ne Ya hõrħ tħku dõmin ku ci wani nama sãbõ daga gare shi, kuma kunã fitarwa, daga gare shi, ƙawã wadda kuke yin ado da ita. Kuma kuna ganin jirãge sunã yankan ruwa a cikinsa kuma dõmin ku yi nħman (fatauci) daga falalarSa. Kuma mai yiwuwa ne kuna gõdħwa. [16.15] Kuma Ya jħfa, a cikin ƙasa, tabbatattun duwatsu dõmin kada ta karkata da ku, da kõguna da hanyõyi, ɗammãninku kunã shiryuwa. [16.16] Kuma da waɗansu alãmõmi, kuma da taurãri sunã mãsu nħman shiryuwa (ga tafiyarsu ta fatauci). [16.17] Shin, wanda Yake yin halitta yanã yin kama da wanda ba ya yin halitta? Shin fa, bã ku tunãwa? [16.18] Kuma idan kun ƙidãya ni´imar Allah, bã ku iya lissafa ta. Lalle ne Allah, haƙĩƙa, Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [16.19] Kuma Allah Yanã sanin abin da kuke asirtãwa da abin da kuke bayyanãwa. [16.20] Kuma waɗanda suke kira, baicin Allah, ba su halicci kõme ba, kuma sũ ne ake halittawa. [16.21] Matattũ ne, bã su da rai, kuma ba su san a wane lõkaci ake tãyar da su ba. [16.22] Abin bautawarku, abin bautãwa ne guda, to, waɗanda ba su yin ĩmãni da Lãhira, zukãtansu mãsu musu ne, kuma su makangara ne. [16.23] Haƙĩƙa, lalle ne, Allah Yanã sanin abin da suke asirtãwa da abin da suke bayyanãwa. Lalle ne Shi, bã Ya Son mãsu girman kai. [16.24] Idan aka ce musu: "Mħne ne Ubangijinku Ya saukar?" Sai su ce: "Tãtsũniyõyin mutãnen farko." [16.25] Dõmin su ɗauki zunubansu cikakku a Rãnar Ƙiyãma, kuma daga zunuban waɗanda suke ɓatarwa bã da wani ilmi ba. To, abin da suke ɗauka na zunubi ya mũnana. [16.26] Lalle ne waɗanda suke a gabãninsu sun yi mãkirci, sai Allah Ya je wa gininsu daga harsãshensa,(1) sai rufi ya fãɗa a kansu daga bisansu, kuma azãba ta jħ musu daga inda ba su sani ba. [16.27] Sa´an nan a Rãnar Ƙiyãma (Allah) Yanã kunyatã su, kuma Yanã cħwa: "Inã abõkan tãrayyaTa, waɗanda kuka kasance kunã gãbã a cikin ɗaukaka sha´aninsu?" Waɗanda aka bai wa ilmi suka ce: "Lalle ne wulãkanci a yau da cũta sun tabbata a kan kãfirai." [16.28] Waɗanda malãiku suke karɓar rãyukansu sunã mãsu zãluntar kansu. Sai suka jħfa nħman sulhu (suka ce) "Ba mu kasance muna aikata wani mummũnan aiki ba." Kayya! Lalle Allah ne Masani ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa. [16.29] Sai ku shiga ƙõfõfin Jahannama, kunã madawwama a cikinta. Sa´an nan tir da mazaunin mãsu girman kai. [16.30] Kuma aka ce wa waɗanda suka yi taƙawa, "Mħne ne Ubangijinku Ya saukar?" Suka ce, "alhħri Ya saukar, ga waɗanda suka kyautata a cikin wannan dũniya akwai wani abu mai kyau, kuma haƙĩƙa, Lãhira ce mafi alhħri." Kuma haƙĩƙa, mãdalla da gidan mãsu taƙawa. [16.31] Gidãjen Aljannar zama sunã shigarsu, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã da abin da suke so a cikinsu. Kamar haka Allah ke sãkã wa mãsu taƙawa. [16.32] Waɗanda malã´iku suke karɓar rãyukansu sunã mãsu jin dãɗin rai, malã´ikun sunã cħwa. "Aminci ya tabbata a kanku. Ku shiga Aljanna sabõda abin da kuka kasance kuna aikatãwa." [16.33] Shin sunã jiran wani abu? Fãce malã´iku su jħ musu kõ kuwa umurnin Ubangijinka. Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu, suka aikata. Kuma Allah bai zãlunce su ba, kuma amma kansu suka kasance sunã zãlunta. [16.34] Sai mũnãnan abũbuwan da suka aikata ya sãme su, kuma abin da suka kasance sunã yi na izgili ya wajaba a kansu. [16.35] Kuma waɗanda suka yi shirki suka ce: "Dã Allah Yã so, dã bamu bautã wa kõme ba, baicinSa, mũ ko ubannimmu kuma dã ba mu haramta kõme ba, baicin abin da Ya haramta." Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu suka aikata. To, shin, akwai wani abu a kan Manzanni, fãce iyarwa bayyananniyã? [16.36] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwace al´umma da wani Manzo (ya ce): "Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci Ɗãgũtu." To, daga gare su akwai wanda Allah Ya shiryar, kuma daga cikinsu akwai wanda ɓata ta wajaba a kansa. Sai ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa´an nan ku dũba yadda ãƙibar mãsu ƙaryatãwa ta kasance. [16.37] Idan ka yi kwaɗayi a kan shiryuwarsu, to, lalle ne, Allah bã Ya shiryar da wanda yake ɓatarwa, kuma bã su da waɗansu mataimaka. [16.38] Kuma suka rantse da Allah iyãkar rantsuwarsu (cħwa) Allah bã ya tãyar da wanda yake mutuwa! Na´am, Yanã tãyarwa. Wa´adi ne (Allah) Ya yi a kanSa tabbatacce, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba. [16.39] Dõmin Ya bayyana musu abin da suke sãɓã wa jũna a cikinsa, kuma dõmin waɗanda suka kãfirta su sani cħwa lalle sũ ne suka kasance maƙaryatã. [16.40] Abin sani kawai, MaganarMu ga wani abu idan Mun nufe shi, Mu ce masa, "Ka kasance; sai yanã kasancħwa. [16.41] Kuma waɗanda suka yi hijira a cikin sha´anin Allah daga bãyan an zãlunce su, haƙĩƙa Munã zaunar da su a cikin dũniya da alhħri kuma lalle lãdar Lãhira ce mafi girmã, dã sun kasance sunã sani. [16.42] Waɗanda suka yi haƙuri, kuma ga Ubangijinsu suke dõgara. [16.43] Kuma ba Mu aika daga gabaninka ba, fãce waɗansu mazãje Muna yin wahayi zuwa gare su. Sai ku tambayi mutãnen Ambato idan kun kasance ba ku sani ba. [16.44] Da hujjõji bayyanannu da littattafai kuma Mun saukar da Ambato zuwa gare ka, dõmin ka bayyana wa mutãne abin da aka sassaukar zuwa gare su, kuma don ɗammãninsu su yi tunãni. [16.45] Shin fa, waɗanda suka yi mãkircin mũnãnan ayyuka sun amince da Allah, bã zai shafe ƙasa da su ba ko kuwa azãba bã zã ta je musu daga inda ba su sani ba? [16.46] Ko kuwa Ya kama su a cikin jujjuyawarsu? Sabõda haka ba su zama masu buwãya ba. [16.47] Ko kuwa Ya kama su a kan naƙasa? To, lalle ne Ubangijinka haƙĩƙa Mai tausayi ne, Mai jin ƙai. [16.48] Shin, ba su Iura ba da abin da Allah Ya halitta kõ mene ne inuwõyinsu suna karkata daga dãma da wajãjen hagu, suna masu sujada ga Allah, alhãli suna masu ƙasƙantar da kai? [16.49] Kuma ga Allah, abin da yake a cikin sammai da ƙasa na dabba da mala´iku, suke yin sujada, kuma bã su kangara. [16.50] Suna tsõron Ubangijinsu daga bisansu, kuma suna aikata abin da ake umuruin su. [16.51] Kuma Allah Ya ce: "Kada ku riƙi abũbuwan bautãwa biyu. Abin sani kawai, wanda ake bautãwa guda ne, sa´an nan sai kuji tsõroNa, Ni kawai." [16.52] Kuma Yana da abin da yake a cikin sammai da ƙasa, kuma Yana da addini wanda yake dawwamamme. Shin fa, wanin Allah kuke bĩ da taƙãwa? [16.53] Kuma abin da yake a gare ku na ni´ima, to, daga Allah ne. Sa´an nan kuma idan cũta ta shãfeku, to, zuwa gare Shi kuke hargõwa. [16.54] sa´an nan idan Ya kuranye cũtar daga gare ku, sai gã wani ɓangare daga gare ku game da Ubangijinsu sunã shirki. [16.55] Dõmin su kãfirta da abin da Muka bã su. To, ku ji dãɗi, sa´an nan da sannu zã ku sani. [16.56] Kuma sunã sanya rabõ(1) ga abin da ba su sani ba daga abin da Muka azurtã su. Ranstuwa da Allah! Lalle ne zã a tambaye ku daga abin da kuka kasance kunã ƙirƙirãwa. [16.57] Kuma sunã danganta ´ya´ya mãta ga Allah. Tsarkinsa yã tabbata! Kuma sũ ne da abin da suke sha´awa. [16.58] Kuma idan aka yi wa ɗayansu bushãra da mace(2) sai fuskarsa ta wuni baƙa ƙirin, alhãli kuwa yanã mai cike da baƙin ciki. [16.59] Yanã ɓõyħwa daga mutãne dõmin mũnin abin da aka yimasa bushãra da shi. Shin, zai riƙe shi a kan wulãkanci kõ zai turbuɗe shi a cikin turɓãya To, abin da suke hukuntãwa ya mũnana. [16.60] Ga waɗanda ba su yi ĩmãni (3) da Lãhira ba akwai sifar cũta kuma ga Allah akwai sifa mafi ɗaukaka. Kuma shi ne Mabuwãyi, Mai hikima. [16.61] Kuma dã Allah Yanã kãma mutãne da zãluncinsu,(4) dã bai bar wata dabba ba a kan ƙasa. Kuma amma Yanã jinkirta musu zuwa ga ajali ambatacce. Sa´an nan idan ajalinsu ya zo, bã zã a yi musu jinkiri ba kõ da sa´a guda, kuma bã zã su gabãta ba. [16.62] Kuma sunã sanyã wa Allah abin da suke ƙi, kuma harsunansu na siffanta ƙarya cħwa lalle ne sunã da abũbuwa mãsu kyau. Bãbu shakka lalle ne sunã da wuta, kuma lalle sũ, waɗanda ake ƙyãlħwa ne (a cikinta) . [16.63] Rantsuwar Allah! Lalle ne haƙĩƙa Mun aika zuwa ga al´ummomi daga gabãninka, sai Shaiɗan ya ƙawãce musu ayyukansu, sabõda haka shĩ ne majiɓincinsu, a yau, kuma sunã da azãba mai raɗaɗi. [16.64] Lalle ba Mu saukar da Littafi ba a kanka, fãce dõmin ka bayyanã musu abin da suka sãɓã wa jũna a cikinsa, kuma dõmin shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni. [16.65] Kuma Allah Yã saukar da ruwa daga sama, sa´an nan Ya rãyar da ƙasa da shi a bãyan mutuwarta. Lalle ne a cikin wannan haƙĩƙa akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke saurãre. [16.66] Kuma lalle ne, kunã da abin lũra a cikin dabbõbin ni´ima;Munã shãyar da ku daga abin da yake a cikin cikunansu, daga tsakãnin tukar tumbi da jini nõno tsantsan mai sauƙin haɗiya ga mãsu shã. [16.67] Kuma daga ´ya´yan itãcen dabĩno da inabi. Kunã sãmudaga gare shi, abin mãye(1) da abinci mai kyau. Lalle a cikin wannan, haƙĩƙa, akwai ãyã ga mutãne waɗanda suke hankalta. [16.68] Kuma Ubangjinka Yã yi wahayi(2) zuwa ga ƙudan zuma cħwa: "Ki riƙi gidãje daga duwãtsu, kuma daga itãce, kuma daga abin da suke ginãwa." [16.69] "Sa´an nan ki ci daga dukan ´ya´yan itãce, sabõda haka ki shiga hanyõyin Ubangijinka, sunã hõrarru." Wani abin shã yanã fita daga cikunanta, mai sãɓãwar launukansa a cikinsa akwai wata warkewa ga mutãne. Lalle ne, a cikin wannan, haƙĩƙa, akwaiãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin tunãni. [16.70] Kuma Allah ne Ya halicce ku, sa´an nan Yanã karɓar rãyukanku, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwã zuwa ga mafi ƙasƙncin rãyuwa, dõmin kada ya san kõme a bãyan dã ya zama mai ilmi. Lalle Allah ne Masani Mai ĩkon yi. [16.71] Kuma Allah Ya fifita sãshenku(3) a kan sãshe a arziki. Sa´an nan waɗanda aka fĩfĩta ba su zama mãsu mayar da arzikinsu a kan abin da hannãyensu na dãma suka mallaka ba, har su zama daidai a cikinsa. Shin fa, da ni´imar Allah suke musu? [16.72] Kuma Allah Yã sanya muku mãtan aure daga kãwunanku, kuma Ya sanya muku daga mãtan aurenku ɗiyã da jĩkõki, kuma Ya arzũta ku daga abũbuwa mãsu dãɗi. Shin fa, da ƙarya suke yin ĩmãni, kuma da ni´imar Allah sũ, suke kãfirta? [16.73] Kuma sunã bautã wa, baicin Allah, abin da yake bã ya mallakar wani arziki dõminsu, daga sammai da ƙasa game da kõme, kuma bã su iyawa (ga aikata kõme) . [16.74] Sa´an nan kada ku bãyar da waɗansu misãlai ga Allah. Lalle ne Allah Yanã sani, kuma kũ, ba ku sani ba. [16.75] Allah Yã buga wani misali da wani bãwa wanda bã ya iya sãmun ĩko a kan yin kõme, da (wani bãwa) wanda Muka azurtã shi daga gare Mu da arziki mai kyau. Sa´an nan shĩ yanã ciyarwa daga arzikin, a asirce da bayyane. Shin sunã daidaita? Gõdiya ta tabbata ga Allah. ôa mafi yawansu ba su sani ba. [16.76] Kuma Allah Ya buga wani misãli, maza biyu, ɗayansu bħbe ne, ba ya iya sãmun ikon yin kõme, kuma shi nauyi ne a kan mai mallakarsa, inda duk ya fuskantar da shi, bã ya zuwa da wani alhħri. Shin, yanã daidaita, shi da (namiji na biyu) wanda yake umurni da a yi ãdalci kuma yanã a kan tafarki madaidaici? [16.77] Kuma ga Allah gaibin(1) sammai da ƙasa yake, kuma al´amarin Sã´a bai zama ba fãce kamar walƙãwar gani, kõ kuwa shĩ ne mafi kusa! Lalle Allah a kan dukan kõme Mai ikon yi ne. [16.78] Kuma Allah ne Ya fitar da ku daga cikunan iyãyenku, ba da kunã sanin kõme ba, kuma Ya sanya muku ji da gannai da zukãta, tsammãninku zã ku gõde. [16.79] Shin ba su ga tsuntsãye(2) ba sunã hõrarru cikin sararin sama bãbu abin da yake riƙe su fãce Allah? Lalle ne a cikin wancan haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni. [16.80] Kuma Allah ne Ya sanya muku daga gidajenku wurin natsuwa, kuma Ya sanya muku daga fatun dabbõbin ni´ima wasu gidãje kunã ɗaukar su da sauƙi a rãnar tafiyarku da rãnar zamanku, kuma daga sũfinsu(1) da gãshinsu da għzarsu (Allah) Ya sanya muku kãyan ɗãki da na jin dãɗi zuwa ga wani lõƙaci. [16.81] Kuma Allah ne Ya sanyã muku inuwa daga abin da Ya halitta, kuma Ya sanyã muku ɗãkuna daga duwãtsu, kuma Ya sanyã muku waɗansu riguna(2) sunã tsare muku zãfi, da waɗansu rĩguna sunã tsare muku makãminku. Kamar wancan ne (Allah) Yake cika ni´imarSa a kanku, tsammãnin ku, kuna sallamawa. [16.82] To, idan sun jũya, to, abin da ya wajaba a kanka, shi ne iyarwã kawai, bayyananniyã. [16.83] Suna sanin ni´imar Allah, sa´an nan kuma sunã musunta, kuma mafi yawansu kãfirai ne. [16.84] Kuma a rãnar da Muke tãyar da mai shaida daga kõwace al´umma, sa´an nan kuma bã zã a yi izni ba ga waɗanda suka kãfirta, kuma ba su zama ana nħman kõmawarsu ba. [16.85] Kuma idan waɗanda suka yi zãlunci suka ga azãba, sa´an nan bã za a saukake ta daga gare su ba, kuma bã su zama anã yi musu jinkiri ba. [16.86] Kuma idan waɗanda suka yi shirka suka ga abũbuwan shirkarsu sai su ce: "Yã Ubangijinmu! Waɗannan ne abũbuwan shirkarmu waɗanda muka kasance munã kira baicinKa". Sai su jħfa magana zuwa gare su, "Lalle ne ku, haƙĩƙa, maƙaryata ne." [16.87] Kuma su shiga nħman sulhu zuwa ga Allah a rãnar nan, kuma abin da suka kasance sunã ƙirƙirãwa ya ɓace daga gare su. [16.88] Waɗanda suka kãfirta kuma suka kange daga hanyar, Alla, Mun ƙãra musu wata azãba bisa ga azãbar, sabõda abin da suka kasance sunã yi na fasãdi. [16.89] Kuma a rãnar da Muke tãyar da shaidu a cikin kõwace al´umma a kansu daga kãwunansu, kuma Muka zo da kai kanã mai bãyar da shaida a kan waɗannan, kuma Mun saussaukar da Littãfi a kanka dõmin yin bãyani ga dukkan kõme da shiriya da rahama da bushãra ga mãsu mĩƙa wuya (Musulmi). [16.90] Lalle Allah nã yin umurni da ãdalci da kyautatãwa, da bai wa ma´abũcin zumunta, kuma yanã hani ga alfãsha da abin da aka ƙi da rarrabe jama´a. Yanã yi muku gargaɗi, ɗammãnin ku, kunã tunãwa. [16.91] Kuma ku cika da alkãwarin(1) Allah idan kun yi alkawari, kuma kada ku warware rantsuwõyinku a bãyan ƙarfafa su, alhãli kuma haƙĩƙa kun sanya Allah Mai lãmuncħwa a kanku. Kuma lalle Allah ne Yake sanin abin da kuke aikatãwa. [16.92] Kuma kada ku kasance kamar wadda ta warware zarenta a bãyan tukka, ya zama warwararku, kunã riƙon rantsuwõyinku dõmin yaudara a tsakãninku, dõmin kasancħwar wata al´umma tãfi rĩba daga wata al´umma! Abin sani kawai Allah Yanã jarrabar ku da shi, kuma lalle ne yanã bayyana muku a Rãnar Ƙiyãma, abin da kuka kasance, a cikinsa, kunã sãɓã wa jũna. [16.93] Kuma dã Allah Ya so, haƙĩ ƙa, dã Ya sanya ku al´umma gudã, kuma Yanã ɓatar da wanda Ya so. Kuma Yanã shiryar da wanda Ya so. Lalle ne anã tambayarku abin da kuka kasance kunã aikatãwa. [16.94] Kada ku riƙi rantsuwõyinku dõmin yaudara a tsakãninku, har ƙafa ta yi sulɓi a bãyan tabbatarta, kuma ku ɗanɗani azãba sabõda abin da kuka kange daga hanyar Allah. Kuma kunã da wata azãba mai girma.(1) [16.95] Kada ku sayi ´yan kuɗi kaɗan da alkawarin Allah. Lalle ne abin da yake a wurin Allah shi ne mafi alhħri a gare ku, idan kun kasance kunã sani. [16.96] Abin da yake a wurinku yanã ƙãrħwa, kuma abin da yake a wurin Allah ne mai wanzuwã. Kuma lalle ne, Munã sãka wa waɗanda suka yi haƙuri da lãdarsu da mafi kyãwun abin da suka kasance sunã aikatãwa. [16.97] Wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji kõ kuwa mace, alhãli yanã mũmini, to, haƙĩƙa Munã rãyar da shi, rãyuwa mai dãɗi. Kuma haƙĩƙa Munã sãkã musu lãdarsu da mafi kyãwun abin da suka kasance sunã aikatãwa. [16.98] Sa´an nan idan ka karantã(2) Alƙur´ãni, sai ka nħmi tsari ga Allah daga shaiɗan jħfaffe. [16.99] Lalle ne shi, bã shi da wani ƙarfi a kan waɗanda suka yi ĩmãni, kuma sunã dõgara ga Ubangijinsu. [16.100] Abin sani kawai ƙarfinsa yanã a kan waɗanda suke jiɓintar sa, kuma waɗanda suke sũ, game da shi, mãsu shirki ne. [16.101] Kuma idan Muka musanya wata ãyã a matsayin wata ãyã, kuma Allah ne Mafi sani ga abin da Yake saukarwa sai su ce: "Abin sani kawai, kai, maƙirƙiri ne." ôa, mafi yawansu bã sa sani. [16.102] Ka ce: "Rũhul Ƙudusi(3) ne ya sassaukar da shi, daga Ubangijinka da gaskiya, dõmin ya tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni, kuma(dõmin) shiriya da bushãra ga Musulmi." [16.103] Kuma lalle ne, haƙĩƙa Munã sanin (cħwa) lalle ne sũ, sunã cħwa, "Abin sani kawai wani mutum ne yake karantar da shi." Harshen wanda suke karkatar da maganar zuwa gare shi, Ba´ajame (1) ne, kuma wannan (Alƙur´ãni) harshe ne Balãrabe bayyananne. [16.104] Lalle ne waɗanda bã su yin ĩmãni da ãyõyin Allah, Allah bã zai shiryar da su ba, kuma sunã da azãba mai raɗaɗi. [16.105] Abin sani kawai waɗanda bã su yin ĩmãni da ãyõyin Allah, sũ ne suke ƙirƙira ƙarya. Kuma waɗannan sũ ne maƙaryata. [16.106] Wanda ya kãfirta da Allah daga bãyan ĩmãninsa,(2) fãce wanda aka tĩlasta alhãli kuwa zũciyarsa tanã natse da ĩmãni kuma wanda ya yi farin ciki da kãfirci, to, akwai fushi a kansa daga Allah, kuma sunã da wata azãba mai girma. [16.107] Waɗancan ne kãfirai dõmin sun fĩfĩta son dũniya a kan Lãhira, kuma lalle ne Allah bã Ya shiryar da mutãne kãfirai. [16.108] Waɗancan ne waɗanda Allah Ya bice hasken zukãtansu da jinsu da gannansu. Kuma waɗancan sũ ne gafalallu. [16.109] Bãbu shakka lalle ne a Lãhira sũ ne mãsu hasãra. [16.110] Sa´an nan kuma lalle ne Ubangijinka ga waɗanda suka yi hijirã daga bãyan an fitine su, sa´an nan kuma suka yi jihãdi, kuma suka yi haƙuri, lalle ne Ubangijinka, daga bãyanta(3) haƙĩƙa Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [16.111] A rãnar da kõwane rai zai je yanã jãyayyar tunkuɗħwa daga kansa, kuma a cika wa kõwane rai (sakamakon) abin da ya aikata, kuma sũ bã zã a zãlunce su ba. [16.112] Kuma Allah Ya buga misãli,(1) wata alƙarya ta kasance amintacciyã, natsattsiyã, arzikinta yanã je mata a wadãce daga kõwane wuri sai ta kãfirta da ni´imõmin Allah, sabõda haka Allah ya ɗanɗana mata tufãfin yunwa da tsõro, sabõda abin da suka kasance sunã sanã´antãwa. [16.113] Kuma lalle ne haƙĩƙa wani Manzo daga gare su, ya jħmusu, sai suka ƙaryata shi, sabõda haka azãba ta kãma su, alhãli kuwa sũ ne mãsu zãlunci. [16.114] Sa´an nan ku ci daga(2) abin da Allah Ya azurta ku da shi, halas, kuma mai dãɗi, kuma ku gõde wa ni´imar Allah idan kun kasance shi kuke bautãwa. [16.115] Abin sani kawai (Allah) Ya haramta(3) muku mussai da jini da nãman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah game da shi. Sa´an nan wanda aka tĩlasta a kan jama´a kuma baicin mai zãlunci, to, lalle Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai. [16.116] Kuma kada ku ce, dõmin abin da harsunanku suke siffantawa da ƙarya, "Wannan halas ne, kuma wannan harãmun ne." Dõmin ku ƙirƙira ƙarya ga Allah. Lalle ne, waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah bã zã su ci nasara ba. [16.117] Jin dãɗi ne kaɗan. Kuma sunã da wata azãba mai raɗaɗi. [16.118] Kuma kan waɗanda suka tũba (Yãhũdu) Mun haramta abin da Muka bãyar da lãbari a gare ka daga gabãni,(4) kuma ba Mu zãlunce su ba, amma sun kasance kansu suke zãlunta. [16.119] Sa´an nan kuma lalle ne Ubangijinka ga waɗanda suka aikata mummunan aiki(1) da jãhilci, sa´an nan suka tũba daga bãyan wancan, kuma suka gyãra, lalle ne Ubangijinka, daga bãyanta haƙĩƙa Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. [16.120] Lalle ne Ibrãhĩm(2) ya kasance shũgaba, mai ƙasƙantar da kai ga Allah, mai karkatã zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba. [16.121] Mai gõdiya(3) ga ni´imominSa (Allah), Ya zãɓe shi, kuma Ya shiryar da shi zuwa ga tafarki madaidaici. [16.122] Kuma Muka ba shi alhħri a cikin dũniya. Kuma lalle shĩ, a Lãhira, yanã daga sãlihai. [16.123] Sa´an nan kuma Muka yi wahayi zuwa gare ka (cħwa), "Ka(4) bi aƙĩdar Ibrahĩm, mai karkatã zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba.´ [16.124] Abin sani kawai, an sanya Asabar a kan waɗanda suka sãɓã wa jũna a cikin sha´aninsa.(5) Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa,Yanã yin hukunci a tsakaninsu a Rãnar Ƙiyãma a cikin abin da suka kasance a cikinsa sunã sãɓã wa jũnã. [16.125] Ka yi kira zuwa ga hanyar Ubangijinka da hikima(6) da wa´azi mai kyau kuma ka yi jãyayya da su da magana wadda take mafi kyau. Lalle ne Ubangijinka Shĩ neMafi sani ga wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa. [16.126] Kuma idan kuka sãka(7) wa uƙũba to ku sãka wa uƙũba da misãlin abin da aka yi muku uƙũbar da shi. Kuma idan kun yi haƙuri, lalle shĩ ne mafi alhħri ga mãsu haƙuri. [16.127] Kuma ka yi haƙuri, kuma haƙurinka bã zai zama ba fãce dõmin Allah, kuma kada ka yi baƙin ciki sabo da su, kuma kada ka kasance a cikin ƙuncin rai daga abin da suke yi na mãkirci. [16.128] Lalle Allah Yanã tãre da waɗanda suka yi taƙawa da waɗanda suke sũ mãsu kyautatãwa ne. @AL ISRAA' Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [17.1] Tsarki ya tabbata ga wanda Ya yi tafiyar dare(1) da bãwanSa da dare daga Masallaci mai alfarma zuwa ga Masallaci mafi nĩsa(2) wanda Muka sanya albarka a gefensa dõmin Mu nũna masa daga ãyõyinMu. Lalle ne Shi shĩ ne Mai ji, Mai gani. [17.2] Kuma Mun bai wa Mũsã(3) littafi, kuma Mun sanya shi shiriya ga Banĩ Isrã´ila, cħwa kada ku riƙi wani wakĩli baiciNa. [17.3] Zuriyar waɗanda Muka ɗauka tãre da Nũhu. Lalle ne shi ya kasance wani bãwa mai gõdiya. [17.4] Kuma Mun hukunta zuwa ga Bani Isrã´ĩla a cikin Littãfi, cewa lalle ne, kunã yin ɓarna a cikin ƙasa sau biyu, kuma lalle ne kunã zãlunci, zãlunci mai girma. [17.5] To idan wa´adin na farkonsu yajħ, za Mu aika, a kanku waɗansu bãyi(4) Nãmu, ma´abũta yãƙi mafĩ tsanani, har su yi yãwo a tsakãnin gidãjenku, kuma yã zama wa´adi abin aikatawa. [17.6] Sa´an nan kuma Mu mayar da ɗauki a gare ku a kansu, kuma Mu taimake ku da dũkiyõyi da ɗiya kuma Mu sanya ku mafiya yawan mãsu fita yãƙi. [17.7] Idan kun kyautata, kun kyautata dõmin kanku, kuma idan kun mũnana to dõmĩnsu. Sa´an nan idan wa´adin na ƙarshe(5) ya jħ, (za su je) dõmin su baƙanta fuskokinku, kuma su shiga masallaci kamar yadda suka shige shi a farkon lõkaci, kuma dõmin su halakar da abin da suka rinjaya a kansa, halakarwa. [17.8] Akwai tsammãnin Ubangijinku Ya yi muku rahama. Kuma idan kun sãke Mu sãke. Kuma Mun sanya Jahannama matsara ga kãfirai. [17.9] Lalle ne wannan Alƙur´ãni yanã shiryarwa ga (hãlaye) waɗanda suke mafi daidaita(1) kuma yanã bãyar da bushãra ga mũminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cħwa) "Lalle ne sunã da wata ijãra. mai girma." [17.10] Kuma lalle ne, waɗanda ba su yin ĩmãni da Lãhira, Mun yi musu tattalin wata azãba mai raɗaɗi. [17.11] Kuma mutum yanã(2) yin addu´a da sharri kamar addu´arsa da alhħri, kuma mutum ya kasance mai gaggãwa. [17.12] Kuma Mun sanya dare da rãna, ãyõyi biyu, sa´an nan Muka shãfe ãyar dare, kuma Muka sanya ãyar rãna mai sanyãwa a yi gani, dõmin ku nħmi falala daga Ubangijinku, kuma dõmin ku san ƙidãyar shħkara da lissafi. Kuma dukan kõme Mun bayyana shi daki-dakin bayyanãwa. [17.13] Kuma kõwane mutum Mun lazimta masa abin rekõdinsa a cikin wuyansa, kuma Mu fitar masa a Rãnar Ƙiyãma da littãfi wanda zai haɗu da shi buɗaɗɗe. [17.14] "Karanta Littãfinka. Ranka ya isa ya zama mai hisãbi a kanka a yau." [17.15] Wanda ya nħmi shiryuwa, to, ya nħmi shiryuwa ne dõmin kansa kawai kuma wanda ya ɓace, to, ya ɓace ne a kansa kawai kuma rai mai ɗaukar nauyi bã ya ɗaukar nauyin wani ran, kuma ba Mu zama mãsu yin azãba ba, sai Mun aika wani Manzo. [17.16] Kuma idan Mun yi nufin Mu halakar da wata alƙarya, sai Mu umurci mawadãtanta, har su yi fãsikanci a cikinta, sa´an nan maganar azãba ta wajaba a kanta, sa´an nan Mu darkãke ta, darkãkħwa. [17.17] Kuma da yawa Muka halakar da al´ummomi a bãyan Nũhu. Kuma Ubangijinka Ya isa ya zama Mai ƙididdigewa ga zunubban bãyinSa, Mai gani. [17.18] Wanda ya kasance yanã nufin mai gaggãwa,(1) sai Mu gaggauta masa a cikinta, abin da Muke so ga wanda Muke nufi, sa´an nan kuma Mu sanya masa Jahannama, ya ƙõnu da ita, yanã abin zargi kuma abin tunkuɗewa. [17.19] Kuma wanda ya nufi Lãhira, kuma ya yi aiki sabõda ita irin aikinta alhãli kuwa yanã mũmĩni, to, waɗannan aikinsu ya kasance gõdadde. [17.20] Dukkansu Munã taimakon waɗannan da waɗancan daga kyautar Ubangijinka, kuma kyautar Ubangijinka ba ta kasance hananna ba. [17.21] Ka duba yadda Muka fĩfĩtar da sãshensu a kan sãshe! Kuma lalle ne Lãhira ce mafi girman darajõji, kuma mafi girman fĩfĩtãwa. [17.22] Kada ka sanya wani abin bautawa na dabam tãre da Allah har ka zauna kana abin zargi, yarɓaɓɓe. [17.23] Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi, kuma game da mahaifa biyu ku kyautata kyautatawa, ko dai ɗayansu ya kai ga tsũfa a wurinka ko dukansu biyu, to, kada ka ce musu ´tir´ kuma kada ka tsãwace su kuma ka faɗa musu magana mai karimci. [17.24] Kuma ka sassauta musu fikãfikan tausasãwa na rahama. Kuma ka ce: "Ya Ubangijina! Ka yi musu rahama, kamar yadda suka yi rħnõna, ina ƙarami." [17.25] Ubangijinku ne Mafi sani ga abin da yake a cikin rãyukanku. Idan kun kasance sãlihai to lalle ne shĩ Ya kasance ga mãsu kõmawa gare Shi, Mai gãfara. [17.26] Kuma ka bai wa ma´abũcin zumunta hakkinsa(2) da miskĩni da ɗan hanya. Kuma kada ka bazzara dũkiyarka, bazzarãwa. [17.27] Lalle ne mubazzarai sun kasance ´yan´uwan shaiɗanu. Kuma Shaiɗan ya kasance ga Ubangijinsa, mai yawan kãfirci. [17.28] Ko dai ka kau da kai daga gare su dõmin nħman rahama daga Ubangijinka, wadda kake fãtanta, to sai ka gaya musu magana mai laushi. [17.29] Kuma kada ka sanya hannunka ƙuƙuntacce zuwa ga wuyanka, kuma kada ka shimfiɗa shi dukan shimfiɗãwa har ka zama abin zargi, wanda ake yanke wa.(1) [17.30] Lalle ne Ubangijinka Yanã shimfiɗa arzĩki ga wanda Yake so, kuma Yanã ƙuƙuntãwa. Lalle Shi, Yã kasance Mai sani ga bãyinSa, Mai gani. [17.31] Kuma kada ku kashe ´yã´yanku dõmin tsõron talauci. Mu ne ke arzũta su, su da ku. Lalle ne kashe su yã kasance kuskure babba. [17.32] Kuma kada ku kusanci zina. Lalle ne ita ta kasance alfãsha ce kuma tã mũnãna ga zama hanya. [17.33] Kuma kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da haƙƙi, kuma wanda aka kashe, yanã wanda aka zãlunta to, haƙĩƙa Mun sanya hujja ga waliyyinsa, sai dai kada ya ƙħtare haddi a cikin kashħwar. Lalle shĩ ya kasance wanda ake taimako. [17.34] Kuma kada ku kusanci dũkiyar marãya fãce dai da sifa wadda take ita ce mafi kyau, har ya isa ga mafi ƙarfinsa. Kuma ku cika alkawari. Lalle alkawari yã kasance abin tambayãwa ne. [17.35] Kuma ku cika mũdu idan kun yi awo, kuma ku auna nauyi da sikħli madaidaici. Wancan ne mafi alhħri, kuma mafi kyau ga fassara. [17.36] Kuma kada ka bi abin da bã ka da ilmi game da shi. Lalle ne jĩ da gani da zũciya, dukan waɗancan (mutum) yã kasance daga gare shi wanda ake tambaya. [17.37] Kuma kada ka yi tafiya a cikin ƙasa da alfahari. Lalle kai bã zã ka hũda ƙasa ba kuma bã zã ka kai a duwãtsu ba ga tsawo. [17.38] Dukan wancan mai mũninsa yã kasance abin ƙyãma a wurin Ubangijinka. [17.39] Wancan yãnã daga abin da Ubangijinka Ya yi wahayi zuwa gare ka na hikima. Kuma kada ka sanya wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah har a jħfa ka a cikin Jahannama kanã wanda ake zargi, wanda ake tunkuɗħwa(1) [17.40] Shin fa, Ubangijinku Ya zãɓe ku da ɗiya maza ne, kuma Ya riƙi ´ya´ya mãta daga malã´iku?(2) Lalle ne kũ, haƙĩƙa, kunã faɗar magana mai girma! [17.41] Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun sarrafa bayãni a cikin wannan Alƙur´ãni dõmin su yi tunãni, kuma bã ya ƙãra musu kõme fãce gudu. [17.42] Ka ce: "Dã akwai waɗansu abũbuwan bautãwa tãre da shi, kamar yadda suka faɗa, a lõkacin, dã (abũbuwan bautãwar) sun nħmi wata hanya(3) zuwa ga Ma´abũcin Al´arshi." [17.43] TsarkinSa yã tabbata kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke faɗã, ɗaukaka mai girma. [17.44] Sammai bakwai da ƙasa da wanda yake a cikinsu sunã yi Masa tasbĩhi. Kuma bãbu wani abu fãce yanã tasbĩhi game da gõde Masa, kuma amma ba ku fahimtar tasbĩhinsu. Lalle ne shĩ, Ya kasance Mai haƙuri ne, Mai gãfara. [17.45] Kuma idan ka karanta Alƙur´ani,(4) sai Mu sanya a tsakãninka da tsakanin waɗanda bã su yin ĩmãni da Lãhira wani shãmaki mai suturcħwa. [17.46] Kuma Mu sanya marufai a kan zukãtansu dõmin kada su fahimce shi, da, wani nauyi a cikin kunnuwansu, kuma idan ka ambaci Ubangijinka, a cikin Alƙur´ãni shĩ kaɗai, sai su jũya a kan bayayyakinsu dõmin gudu. [17.47] Mũ ne Mafi sani game da abin da suke saurãre da shi a lõkacin da suke yin saurãren zuwa gare ka, kuma a lõkacin da suke mãsu gãnãwa a tsakãninsu a lõkacin da azzãlumai suke cħwa, "Bã ku biyar kõwa fãce wani namiji sihirtacce." [17.48] Ka dũba yadda suka buga maka misãlai, sai suka ɓace bã su iya sãmun hanya. [17.49] Kuma suka ce: "Shin, idan mun kasance ƙasũsuwa da, niƙaƙƙun gaɓãɓuwa ashe, lalle ne mũ haƙĩƙa, waɗanda ake tãyarwa ne a wata halitta sãbuwa?" [17.50] Ka ce: "Ku kasance duwãtsu ko kuwa baƙin ƙarfe." [17.51] "Kõ kuwa wata halitta daga abin da yake da girma a cikin ƙirazanku." To zã su ce "Wãne ne zai mayar da mu?" Ka ce: "Wanda Ya ƙaga halittarku a farkon lõkaci." To, zã su gyaɗa kansu zuwa gare ka, kuma sunã cħwa, "A yaushe ne shi?" Ka ce: "Akwai tsammãninsa ya kasance kusa." [17.52] "A rãnar da Yake kiran ku, sa´an nan ku riƙa karɓãwa game dã gõde Masa, kuma kunã zaton ba ku zauna ba fãce kaɗan." [17.53] Kuma ka cħ wa bãyiNa, su faɗi kalma(1) wadda take mafi kyau. Lalle ne Shaiɗan yanã sanya ɓarna a tsakãninsu. Lalle ne Shaiɗan ya kasance ga mutum, maƙiyi bayyananne. [17.54] Ubangijinku ne Mafi sani game da ku. Idan Ya so, zai yi muku rahama, kõ kuwa idan Yã so zai azabtãku. Kuma ba Mu aika ka kanã wakĩli a kansu ba. [17.55] Kuma Ubangijinka ne Mafi sani game da wanda yake a cikin sammai da ƙasa. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun fĩfĩta sãshen Annabãwa a kan sãshe kuma Mun bai wa Dãwũda Zabũra.(2) [17.56] Ka ce: "Ku kirãyi waɗanda kuka riya, baicinSa." To, ba su mallakar kuranyħwar cũta daga gare ku, kuma haka jũyarwa."(3) [17.57] Waɗancan, waɗanda suke kiran,(4) sunã nħman tsãni zuwa ga Ubangijinsu. Waɗanne ne suke mafĩfĩta a kusanta? Kuma sunã fãtan sãmun rahamarSa, kuma sunã tsõron azãbarSa. Lalle ne azãbar Ubangijinka ta kasance abar tsõro ce. [17.58] Kuma bãbu wata alƙarya fãce, Mu ne mãsu halaka ta a gabãnin Rãnar Ƙiyãma kõ kuwa Mũ mãsu azãbta ta ne da azãba mai tsanani. Wancan ya kasance a cikin littãfi rubũtacce. [17.59] Kuma bãbu abin da ya hana Mu, Mu aika da ãyõyi fãce sabõda mutãnen farko sun ƙaryata game da su. Kuma Mun bai wa Samũdãwa tãguwa, ãyã bayyananna, sai suka yi zãlunci game da ita. Kuma bã Mu aikãwa da ãyõyi fãce dõmin tsõratarwa. [17.60] Kuma a lõkacin da Muka ce maka, "Lalle ne Ubangijinka Yã kħwaye mutãne." Kuma ba Mu sanya abin da ka gani wanda(1) Muka nũna maka ba, fãce dõmin fitina ga mutãne, da itãciya wadda aka la´anta a cikin Alƙur´ani. Kuma Munã tsõratar da su, sa´an nan (tsõratarwar) bã ta ƙãra su fãce da kangara mai girma. [17.61] Kuma a lõkacin(2) da Muka cħ wa malã´iku, "Ku yi sujada ga Ãdamu," sai suka yi sujada, fãce Ibilĩsa, ya ce: "shin, zan yi sujada ga wanda ka(3) halitta shi yanã lãka?" [17.62] Ya ce: "Shin, kã gan ka(4) ! Wannan wanda ka girmama a kaina, lalle ne idan ka jinkirtã mini zuwa ga Rãnar Ƙiyãma lalle ne, zan tumɓuke zuriyarsa, fãce kaɗan." [17.63] Ya ce: "Ka tafi. Sa´an nan wanda ya bĩ ka daga gare su, to, Jahannama ce sakamakonku, (Mu ba ku shi) sakamako cikakke." [17.64] "Kuma ka rikitar da wanda ka sãmi ĩko a kansa, daga gare su, da sautinka, kuma ka yi hari a kansu da dawãkinka da dãkãrunka kuma ka yi tãrħwa da su a cikin dũkiyõyi da ɗiyã, kuma ka yi musu wa´adi. Alhãli kuwa Shaiɗan bã ya yi musu wa´adin kõme fãce da ruɗi." [17.65] "Lalle ne bãyiNa, bã ka da wani ƙarfi a kansu. Kuma Ubangijinka Ya isa Ya zama wakĩli." [17.66] Ubangijinku ne Yake gudãnar da jirgi a cikin tħku, dõmin ku nema daga falalarSa. Lalle ne Shĩ, Yã kasance a gare ku Mai jin ƙai. [17.67] Kuma idan cũta ta shãfe ku, a cikin tħku, sai wanda kuke kira ya ɓace fãce Shi. To, a lõkacin da Ya tsirar da ku zuwa, ga tudu sai kuka bijire. Kuma mutum ya kasance mai yawan butulci. [17.68] Shin fa kun amince cħwa (Allah) bã Ya shãfe għfen ƙasa game da ku kõ kuwa Ya aika da iska mai tsakuwa a kanku, sa´an nan kuma bã zã ku sãmi wani wakĩli ba dõminku? [17.69] Ko kun amince ga Ya mayar da ku a cikin tħkun a wani lõkaci na dabam, sa´an na Ya aika wata gũguwa mai karya abũbuwa daga iska, har ya nutsar da ku sabõda abin da kuka yi na kãfirci? Sa´an nan kuma bã ku sãmun mai bin hakki sabõda ku, a kanMu, game da Shi. [17.70] Kuma lalle ne Mun girmama ´yan Adam,(1) kuma Muka ɗauke su a cikin ƙasa da tħku kuma Muka azurta su daga abũbuwa mãsu dãɗi kuma Muka fĩfĩta su a kan mãsu yawa daga waɗanda Muka halitta, fĩfĩtãwa. [17.71] A rãnar da Muke kiran(2) kõwane mutãne da lĩmãminsu to, wanda aka bai wa littafinsa a dãmansa, to, waɗannan sunã karãtun littãfinsu, kuma bã a zãluntar su da zaren bãkin gurtsin dabĩno. [17.72] Kuma wanda ya kasance makãho(3) a cikin wannan sabõda haka shi a Lãhira makãho ne kuma mafi ɓata ga hanya. [17.73] Kuma lalle ne sun yi kusa haƙĩƙa, su fitinħ ka daga abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, dõmin ka ƙirƙira waninsa a gare Mu, a lõkacin, haƙĩƙa, dã sun riƙe ka masoyi. [17.74] Kuma bã dõmin(4) Mun tabbatar da kai ba, lalle ne, haƙĩƙa, dã kã yi kusa ka karkata zuwa gare su ta wani abu kaɗan. [17.75] A lõkacin, lalle ne, dã Mun ɗanɗana maka ninkin azãbar rãyuwa da ninkin azãbar mutuwa, sa´an nan kuma bã zã ka sãmi mataimaki ba a kanMu. [17.76] Kuma lalle ne, sun(1) yi kusa, haƙĩƙa, su tãyar da hankalinka daga ƙasar, dõmin su fitar da kai daga gare ta. Kuma a lõkacin, bã zã su zauna ba a kan sãɓãninka fãce kaɗan. [17.77] Hanyar waɗanda, haƙĩƙa, Muka aika a gabãninka, daga ManzanninMu, kuma bã zã ka sãmi jũyarwa ba ga hanyarMu. [17.78] Ka tsayar da salla(2) a karkatar rãnã zuwa ga duhun dare da lõkacin fitar alfijir lalle ne karãtun fitar alfijir(3) ya kasance wanda ake halarta. [17.79] Kuma da dare, sai ka yi hĩra(4) da shi (Alƙur´ãni) akan ƙãri gare ka. Akwai tsammãnin Ubangijinka Ya tãyar da kai a wani matsayi gõdadde. [17.80] Kuma ka ce: "Yã Ubangijĩna!(5) Ka shigar, da ni shigar gaskiya, kuma Ka fitar da ni fitar gaskiya. Kuma Ka sanya mini, daga gunKa, wani ƙarfi mai taimako." [17.81] Kuma ka ce: "Gaskiya tã zo, kuma ƙarya ta lãlãce. Lalle ne ƙarya ta kasance lãlãtacciya." [17.82] Kuma Munã sassaukarwa daga Alƙur´ãni, abin da yake waraka ne da rahama ga mũminai. Kuma bã ya ƙãra wa azzãlumai (kõme) fãce hasãra. [17.83] Kuma idan Muka yi ni´ima a kan mutum,(6) sai ya hinjire, kuma ya nĩsanta da gefensa, kuma idan sharri ya shãfe shi, sai ya kasance mai yanke ƙauna. [17.84] Ka ce: "Kõwa ya yi aiki a kan hanyarsa. Sa´an nan Ubangijinka ne Mafi sani ga wanda yake mafi shiryuwa ga hanya." [17.85] Sunã tambayar ka ga rũhi. Ka ce: "Rũhi daga al´amarin Ubangijina ne, kuma ba a bã ku (kõme) ba daga ilmi fãce kaɗan." [17.86] Kuma lalle ne idan Mun so, haƙĩƙa, Munã tafiya da abinda Muka yi wahayi zuwa gare ka. Sa´an nan kuma bã za ka sãmi wani wakĩli ba dõminka game da shi a kanMu. [17.87] Fãce da rahama daga Ubangijinka. Lalle ne falalarSa ta kasance mai girma a kanka. [17.88] Ka ce: "Lalle ne idan mutãne da aljannu sun tãru a kan su zo da misãlin wannan Alƙur´ãni bã zã su zo da misãlinsa ba, kuma kõ dã sãshinsu yã kasance, mataimaki ga sãshi." [17.89] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun caccanza dõmin mutãne, a cikin wannan Alƙur´ãni, daga kõwane misãli sai mafi yawan mutãne suka ƙi (kõme) fãce kãfirci, [17.90] Kuma suka ce: "Bã zã mu yi ĩmãni ba dõminka sai kã ɓuɓɓugar(1) da idan ruwa daga ƙasa. [17.91] "Kõ kuma wata gõna daga dabĩnai da inabi ta kasance a gare ka. Sa´an nan ka ɓuɓɓugar da ƙõramu a tsakãninta ɓuɓɓugarwa." [17.92] "Kõ kuwa ka kãyar da sama a kanmu kaɓukka kõ kuwa ka zo da Allah, da malã´iku banga-banga." [17.93] "Kõ kuwa wani gida na zĩnãriya ya kasance a gare ka, kõ kuwa ka tãka a cikin sama. Kuma bã zã mu yi ĩmãni ba ga tãkawarka, sai ka sassaukõ da wani littãfi a kanmu, munã karantã shi." Ka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijĩna! Ban kasance ba fãce mutum, Manzo." [17.94] Kuma bãbu abin da ya hana mutãne su yi ĩmãni, a lõkacin da shiriya ta jħ musu, fãce sun ce, "Shin, Allah zai aiko mutum ya zamo yana Manzo." [17.95] Ka ce: "Dã malã´iku sun kasance a cikin ƙasa, kuma sunã tafiya, sunã masu natsuwa, lalle ne dã mun saukar da malã´ika daga sama ya zama manzo a kansu." [17.96] Ka ce: "Allah Yã isa zama shaida a tsakãnina da ku. Lalle Shi Ya kasance ga bãyinsa, mai ƙididdigewa ne Mai gani." [17.97] Kuma wanda Allah Ya shiryar, to, shĩ ne shiryayye, kuma wanda Ya ɓatar to bã zã ka sãmi waɗansu masõya gare su ba baicinSa. Kuma Munã tãra su a Rãnar Ƙiyãma a kan fuskõkinsu, sunã makãfi, kuma bħbãye da kurãme. Matattararsu Jahannama ce, kõ da yaushe ta bice, sai Mu ƙãra musu wata wuta mai tsanani. [17.98] Wancan ne sãkamakonsu sabõda lalle sũ, sun kãfirta da ãyõyinMu, kuma suka ce: "Shin idan muka kasance ƙasũsuwa da nĩƙaƙƙun gaɓũɓuwa, shin lalle mũ, haƙĩka, waɗanda ake tãyarwa ne a cikin wata halitta sãbuwa?" [17.99] Shin, kuma ba su ganĩ(1) ba (cħwa) lalle ne Allah, wandaYa halicci sammai da ƙasa, Mai ikon yi ne a kan Ya halicci misãlinsu? Kuma Ya sanya wani ajali wanda bãbu kõkwanto a cikinsa? Sai azzãlumai suka ƙi fãce kãfirci. [17.100] Ka ce: "Dã dai kũ, kunã mallakar(2) taskõkin rahamar Ubangijĩna, a lõkacin, haƙĩƙa dã kun kãme dõmin tsõron ƙãrħwar taskõkin. Kuma mutum yã kasance mai ƙwauro ne." [17.101] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun bai wa Mũsã ãyõyi(3) guda tara bayyanannu, sai ka tambayi Banĩ Isrã´ila, a lõkacin da ya jħ musu, sai Fir´auna ya ce masa, "Lalle nĩ, inã zaton ka, ya Mũsã, sihirtacce." [17.102] Ya ce: "lalle ne haƙĩƙa ka sani bãbu wanda ya saukar da waɗannan, fãce Ubangijin sammai da ƙasa dõmĩn su zama abũbuwan lũra. Kuma lalle ne ni, haƙĩƙa, ina zaton ka, yã Fir´auna, halakakke." [17.103] Sai ya yi nufin fitar da su daga ƙasar, sai Muka nutsar da shi, shi da wanda yake tãre da shi gabã ɗaya. [17.104] Kuma Muka ce: daga bãyansa ga Banĩ Isrã´ĩla, "Ku zauni ƙasar. Sa´an nan idan wa´adin ƙarshe ya zo, zã Mu jħ da ku jama´a-jama´a."(4) [17.105] Kuma da gaskiya Muka saukar da shi, kuma da gaskiya ya sauka. Kuma ba Mu aike ka ba fãce kanã mai bãyar da bushãra kuma mai gargaɗi. [17.106] Kuma yanã abin karãtu Mun rarraba shi dõmin ka karanta shi ga mutane a kan jinkiri kuma Mun sassaukar da shi sassaukarwa.(1) [17.107] Ka ce: "Ku yi ĩmãni(2) da Shi, ko kuwa kada ku yi ĩmãni, lalle ne waɗanda aka bai wa ilmi daga gabãninsa, idan anã karãtunsa a kansu, sunã fãɗuwa ga haɓõɓinsu, sunã mãsu sujada." [17.108] "Kuma sunã cħwa: Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle ne wa´adin Ubangijinmu ya kasance, haƙĩƙa ,abin aikatãwa." [17.109] Kuma sunã fãɗuwa ga haɓõɓinsu sunã kũka, kuma yanã ƙara musu tsõro. [17.110] Ka ce: "Ku kirayi Allah(3) kõ kuwa ku kirãyi Mai rahama. Kõwane kuka kira to Yanã da sũnãye mafi kyau. Kuma, kada ka bayyana(4) ga sallarka, kuma kada ka ɓõye ta. Ka nħmi hanya a tsakãnin wancan." [17.111] Kuma ka ce: "Gõdiyã(5) ta tabbata ga Allah wanda bai riƙi ɗã ba kuma abõkin tãrayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa, kuma wani masõyi sabõda wulãkancin bai kasance a gare Shi ba." Kuma ka girmama Shi, girmamãwa. @AL KAHFI Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [18.1] Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya saukar da Littafi a kan bãwansa kuma bai sanya karkata ba a gare shi. [18.2] Madaidaici, dõmin Ya yi gargaɗi da azãba mai tsanani daga gare shi, kuma Ya yi bushãra ga mũminai, waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai da (cħwa) sunã da wata lãdã mai kyau. [18.3] Sunã mãsu zama a cikinta har abada. [18.4] Kuma Ya yi gargaɗi ga waɗanda(6) suka ce: "Allah yanã da ɗa." [18.5] Ba su da wani ilmi game da wannan magana, kuma iyãyensu bã su da shi, abin da ke fita daga bãkunansu ya girma ga ya zama kalmar faɗa! Ba su faɗan kõme fãce ƙarya. [18.6] To, kã yi kusa ka halaka ranka a gurabbansu, wai dõmin ba su yi ĩmãni da wannan lãbãri ba sabõda baƙin ciki. [18.7] Lalle ne Mũ, Mun sanya abin da ke kan ƙasa wata ƙawa(1) ce gare ta, dõmin Mu jarraba su; wanne daga cikinsu zai zama mafi kyau ga aiki. [18.8] Kuma lalle Mũ, Mãsu sanya abin da ke a kanta (ya zama) turɓãya ƙeƙasasshiya ne. [18.9] Ko kuwa kã yi zaton cħwa ma´abũta kõgo(2) da allo sun kasance abin mãmãki daga ãyõyin Allah? [18.10] A lõkacin da samarin suka tattara zuwa ga kõgon, sai suka ce: "Ya Ubangijinmu!(3) Ka bã mu wata rahama daga gare Ka, kuma Ka sauƙaƙe mana (sãmun) shiriya daga al´amarinmu." [18.11] Sai Muka yi dũka a kan kunnunwansu,(4) a cikin kõgon, shħkaru mãsu yawa. [18.12] Sa´an nan Muka tãyar da su, dõmin Mu san wane ɗayan ƙungiyõyin biyu suka fi lissãfi ga abin da suka zauna na lõkacin. [18.13] Mu ne ke jħranta maka lãbãrinsu da gaskiya. Lalle ne sũ, waɗansu samãri ne. Sun yi ĩmãni da Ubangijinsu, kuma Muka ƙãra musu wata shiriya. [18.14] Kuma Muka ɗaure a kan zukãtansu, a lõkacin da suka tsayu, sa´an nan suka ce: "Ubangijinmu Shĩ ne Ubangijin sammai daƙasa. Bã zã mu kirãyi waninSa abin bautawa ba. (Idan mun yi haka) lalle ne, haƙĩƙa, mun faɗi abin da ya ƙħtare haddi a sa´an nan." [18.15] "Ga waɗannan mutãnenmu sun riƙi waninSa abin bautãwa! Don me bã su zuwa da wata hujja bayyananna a kansu (waɗanda ake bautawar) ? To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙãga ƙarya ga Allah?" [18.16] "Kuma idan kun nĩsance su sũ da abin da suke bautãwa, fãce Allah, to, ku tattara zuwa ga kõgon sai Ubangijinku Ya watsa muku daga rahamarSa kuma Ya sauƙaƙe muku madõgara daga al´amarinku." [18.17] Kuma kanã ganin rãnã idan ta fito tanã karkata daga kõgonsu wajen dãma kuma idan ta fãɗi tanã gurgura su wajen hagu, kuma su, sunã a cikin wani fili daga gare shi. Wannan abu yanã daga ãyõyin Allah. Wanda Allah Ya shiryar, to shĩ ne mai shiryuwa, kuma wanda Allah Ya ɓatar to bã zã ka sãmar masa wani majiɓinci mai shiryarwa ba. [18.18] Kuma kanã zaton su farkakku ne, alhãli kuwa sũ mãsu barci ne. Munã jũya su wajen dãma da wajen hagu, kuma karensu yanã shimfiɗe da zirã´õ´in ƙafãfuwansa ga farfãjiya (ta kõgon). Dã ka lħka (a kan) su (dã) lalle ne, ka jũya daga gare su a guje kuma (dã) lalle ne ka cika da tsõro daga gare su. [18.19] Kuma kamar wannan ne Muka tãyar da su, dõmin(1) su tambayi jũna a tsakãninsu. Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Mħne ne lõkacin da kuka zauna?" Suka ce: "Mun zauna yini ɗaya ko sãshen yini." Suka ce: "Ubangijinku ne Mafi sani ga abin da kuka zauna. To, ku aika da ɗayanku, game da azurfarku wannan, zuwa ga birnin.(2) Sai ya dũba wanne ne mafi tsarki ga abin dafãwa, sai ya zo muku da abinci daga gare shi. Kuma sai ya yi da hankali, kada ya sanar da ku ga wani mutum." [18.20] "Lalle ne sũ idan sun kãmã ku, zã su jħfħ ku, kõ kuwa su mayar da ku a cikin addininsu kuma bã zã ku sãmi babban rabo ba, a sa´an nan har abada." [18.21] Kuma kamar wancan ne, Muka nũna su (gare su) dõmin su san lalle wa´adin Allah gaskiya ne, kuma lalle ne Sa´a bãbu shakka a cikinta. A lõkacin da suke jãyayyar al´amarinsu a tsakãninsu(1) sai suka ce: "Ku gina wani gini a kansu, Ubangijinsu ne Mafi sani game da su." Waɗanda suka rinjãya a kan al´amarinsu suka ce: "Lalle mu riƙi masãllãci a kansu." [18.22] Zã su ce: "Uku ne da na huɗunsu karensu."Kuma sunã cħwa, "Biyar ne da na shidansu karensu," a kan jĩfa a cikin duhu. Kuma sunã cħwa, "Bakwaine da na takwas ɗinsu karensu. "Ka ce: "Ubangijĩna(2) ne Mafi sani ga ƙidãyarsu, bãbu wanda ya san su fãce kaɗan. "Kada ka yi jãyayya a cikin al´amarinsu, sai jayayya bayyananna. Kuma kada ka yi fatawa(3) ga kõwa daga gare su a cikin al´amarinsu. [18.23] Kuma kada lalle ka ce ga wani abu, "Lalle ni, mai aikatãwa ne ga wancan a gõbe." [18.24] Fãce idan Allah Ya so. Kuma ka ambaci Ubangijinka idan ka manta, kuma ka ce: "Ɗammãni ga Ubangijĩna, Ya shiryar da ni ga abin da yake shi ne mafi kusa ga wannan na shiriya." [18.25] Kuma suka zauna a cikin kõgonsu shħkaru ɗarĩ uku kuma suka daɗa tara. [18.26] Ka ce: "Allah ne Mafi sani ga abin da suka zauna. Shĩ ne da (sanin) gaibin sammai da ƙasa. Mene ne ya yi ganinSa da jinSa! Bã su da wani majiɓinci baicinSa kuma bã Ya tãrayya da kõwa a cikin hukuncinsa." [18.27] Ka karanta abin da aka yi wahayi zuwa gare ka, na littãfin Ubangijinka. Bãbu mai musanyãwa ga kalmõminSa kuma bã zã kã sãmi wata madõgara ba daga waninsa. [18.28] Ka haƙurtar da ranka tãre da waɗanda ke kiran Ubangijinsu, sãfe da maraice, sunã nufin yardarSa. Kuma kada idãnunka su jũya daga barinsu, kanã nufin ƙawar rãyuwar dũniya.(1) Kuma kada ka bi wanda Muka shagaltar da zũciyarsa daga hukuncinMu, kuma ya bi son zuciyarsa, alhãli kuwa al´amarinsa ya kasance yin ɓarna. [18.29] Kuma ka ce: "Gaskiya daga Ubangijinku take." Sabõda haka wanda ya so, to, ya yi ĩmãni, kuma wanda ya so, to, ya kãfirta. Lalle ne Mũ, Mun yi tattali dõmin azzãlumai wata wuta wadda shãmakunta, sun ƙħwaye da su. Kuma idan sun nħmi taimako sai a taimake su da wani ruwa kamar dabzar mai, yanã sõye fuskõki. Tir da abin shansu, kuma wutar ta yi mũnin zama mahũtarsu. [18.30] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai lalle ne Mũ bã Mu tõzartar da lãdar wanda ya kyautata aiki. [18.31] Waɗannan sunã da gidãjen Aljannar zama, ƙõramu na gudãna daga ƙarƙashinsu, anã sanya musu ƙawa, a cikinsu, daga mundãye na zinariya, kuma sunã tufantar waɗansu tũfãfi kõre, na alharĩni raƙĩƙi da alharini mai kauri sunã kishingiɗe a cikinsu, a kan, karagu. Mãdalla da sakamakonsu. Kuma Aljanna ta kyautatu da zama wurin hutãwa. [18.32] Kuma ka buga musu misãli(2) da waɗansu maza biyu. Mun sanya wa ɗayansu gõnaki biyu na inabõbi, kuma Muka kħwayesu da itãcen dabĩnai, kuma Muka sanya shũka a tsakãninsu (sũ gõnakin). [18.33] Kõwace gõna daga biyun, tã bãyar da amfãninta, kuma ba ta yi zãluncin kõme ba daga gare shi. Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙoramu a tsakãninsu. [18.34] Kuma ɗan ĩtãce ya kasance gare shi. Sai ya ce wa abõkinsa, alhali kuwa yanã muhãwara da shi, "Nĩ ne mafĩfĩci daga gare ka a wajen dũkiya, kuma mafi izza a wajen jama´a." [18.35] Kuma ya shiga gõnarsa, alhãli yanã mai zãlunci ga kansa, ya ce: "Bã ni zaton wannan zã ta halaka har abada." [18.36] "Kuma bã ni zaton sa´a mai tsayuwa ce, kuma lalle ne, idan an mayar da ni zuwa ga Ubangijiĩna, to, lalle ne, zan sãmi abin da yake mafi alhħri daga gare ta ya zama makõma." [18.37] Abõkinsa ya ce masa, alhãli kuwa yanã muhãwara da shi, "Ashe kã kãfirta da wanda Ya halitta ka daga turɓaya, sa´an nan daga ɗigon maniyi, sa´an nan Ya daidaita ka, ka zama mutum?" [18.38] "Amma ni, shĩ ne Allah Ubangijina, kuma bã zan tãra kõwa da Ubangijina ba" [18.39] "Kuma don me, a lõkacin da ka shiga gõnarka, ka ce, ´Abin da Allah ya so (shi ke tabbata) bãbu wani ƙarfi fãce game da Allah.´ Idan ka gan ni, ni ne mafi ƙaranci daga gare ka a wajen dũkiya da ɗiya." [18.40] "To, akwai fãtan Ubangijĩna Ya ba ni abin da yake mafi alhħri daga gõnarka, kuma ya aika azãba a kanta (ita gõnarka) daga sama, sai ta wãyi gari turɓãya mai santsi." [18.41] "Kõ kuma ruwanta ya wãyi gari faƙaƙƙe, sabõda haka, bã zã ka iya nħmo shi ba dõminta." [18.42] Kuma aka halaka dukan ´ya´yan itãcensa, sai ya wãyi gari yanã jũyar da tãfunansa biyu, sabõda abin da ya kashe a cikinta, alhãli kuwa ita tanã kwance a kan rassanta, kuma yanã cħwa, "Kaitõna, dã dai ban tãra(1) wani da Ubangijina ba!" [18.43] Kuma wata jama´a ba ta kasance a gare shi ba, waɗanda ke taimakon sa, baicin Allah, kuma bai kasance mai taimakon kansa ba. [18.44] A can taimako da jiɓinta ga Allah yake. Shĩ ne kawai Gaskiya, shĩ ne Mafĩfĩci ga lãda kuma Mafĩfĩci ga ãƙiba. [18.45] Ka buga musu misãlin rãyuwar dũniya, kamar ruwa ne wanda Muka saukar da shi daga sama sa´an nan tsirin ƙasa ya garwaya da shi, sa´an nan ya wãyi gari dudduga, iska tanã shiƙar sa. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan ĩkon yi ne a kan dukan kõme. [18.46] Dũkiya da ɗiya,(1) sũ ne ƙawar rãyuwar dũniya, kuma ayyuka mãsu wanzuwa na ƙwarai sun fi zama alhħri a wurin Ubangijinka ga lãda kuma sun fi alhħri ga bũri. [18.47] Kuma a rãnar da Muke tafiyar da duwãtsu, kuma ka ga ƙasa bayyane, kuma Mu tãra su har ba Mu bar kõwa ba daga gare su. [18.48] Kuma a gittã(2) su ga Ubangijinka sunã sahu guda, (Mu ce musu), "Lalle ne haƙĩƙa kun zo Mana, kamar yadda Muka halitta ku a farkon lõkaci. ôa, kun riya cħwa bã zã Mu sanya muku wani lõkacin haɗuwa ba." [18.49] Kuma aka aza littãfin ayyuka, sai ka ga mãsu laifi sunã mãsu jin tsõro daga abin da ke cikinsa, kuma sunã cħwa "Kaitonmu! Mħne ne ga wannan littãfi, bã ya barin ƙarama, kuma bã ya barin babba, fãce yã ƙididdige ta?" Kuma suka sãmi abin da suka aikata halarce. Kuma Ubangijinka bã Ya zãluntar kõwa. [18.50] Kuma a lõkacin da Muka ce wa malãiku, "Ku yi sujada ga Ãdamu." Sai suka yi sujada fãce Iblĩsa, yã kasance daga aljannu sai ya yi fãsiƙanci ga barin umurnin Ubangijinsa. To fa, ashe, kunã riƙon sa, shi da zũriyarsa, su zama majiɓinta baicin Ni, alhãli kuwa su maƙiya ne a gare ku? Tir da ya zama musanya ga azzãlumai.(3) [18.51] Ban shaida musu halittar sammai da ƙasa ba, kuma ban (shaida musu) halittar rãyukansu ba kuma ban kasance mai riƙon mãsu ɓatarwa (da wani) su zama mataimaka ba. [18.52] Kuma da rãnar da Allah Yake cħwa, "Ku kirãyi abõkan tarayyãTa, waɗanda kuka riya." Sai su kirãye su, sai bã zã su karɓa musu ba, kuma Mu sanya Maubiƙa(4) (Mahalaka) a tsakãninsu, [18.53] Kuma mãsu laifi suka ga wutã suka tabbata lalle ne, sũ Mãsu auka mata ne, kuma ba su sãmi majũya ba daga gare ta. [18.54] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun jujjũya, a cikin wannan Alƙur´ãni, daga kõwane irin misãli ga mutãne (dõmin su gãne, su bi sharĩ´a), kuma mutum yã kasance mafi yawan abu ga jidãli.(1) [18.55] Kuma bãbu abin da ya hana mutãne su yi ĩmãni a lõkacin da shiriya ta zo musu, kuma su nħmi gãfara daga Ubangijinsu, fãce hanyar farko(2) ta je musu kõ kuma azãba ta jħ musu nau´i-nau´i. [18.56] Kuma ba Mu aika Manzanni ba fãce sunã mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi, kuma waɗanda suka kãfirta sunã jidãli da ƙarya dõmin su ɓãta gaskiya da ita, kuma suka riƙi ãyõyiNa da abin da aka yi musu gargaɗi da shi abin izgili. [18.57] Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda aka tunãtar game da ãyõyin Ubangijinsa, sai ya bijire daga barinsu, kuma ya manta abin da hannãyensa suka gabãtar? Lalle ne Mũ, Mun sanya abũbuwan rufi a kan zukãtansu dõmin kada su fahimcħ shi, kuma a cikin kunnuwansu (Mun sanya) wani nauyi, kuma idan kã kĩrayħ su zuwa ga shiriya, to, bã zã su shiryu ba, a sa´an nan, har abada. [18.58] Kuma Ubangijinka Mai gãfara ne, Ma´abũcin rahama. Dã Yanã kãma su sabõda abin da suka sanã´anta, lalle ne, dã Ya gaggauta azãba a gare su. ôa, sunã da lõkacin alkawari, (wanda) bã zã su sãmi wata makõma ba, baicinSa.(3) [18.59] Kuma waɗancan alƙaryu(4) Mun halaka su, a lõkacin da suka yi zãlunci, kuma Muka sanya lõkacin alkawarin, ga halaka(5) su. [18.60] Kuma a lõkacin da Mũsã(6) ya ce wa yãronsa, "Bã zan gushe ba sai na isa mahaɗar tħku biyu, kõ in shũɗe da tafiya shekara da shħkaru." [18.61] To, a lõkacin da suka isa mahaɗar tsakãninsu sai suka manta kĩfinsu, sai ya kãma tafarkinsa a cikin tħku kamar bĩga. [18.62] To, a lõkacin da suka wuce ya ce wa yãronsa, "Ka kãwo mana kãlãcinmu. Lalle ne haƙĩƙa mun haɗu da wahala daga tafiyarmu wannan." [18.63] (Yãron) ya ce: "Kã gani! A lõkacin da muka tattara zuwa ga falalen nan to, lalle nĩ, na manta kĩfin, kuma bãbu abin da ya mantar da nĩ shi, fãce Shaiɗan, dõmin kada in tuna shi, sai ya kama tafarkinsa a cikin tħku, da mãmãki!" [18.64] Ya ce: "Wancan ne abin da muka kasance munã biɗã." Sai suka kõma a kan gurãbunsu, sunã bĩbiya. [18.65] Sai suka sãmi wani bãwa daga bãyinMu, Mun bã shi wata rahama(1) daga wurinMu, kuma Mun sanar da shi wani ilmi daga gunMu. [18.66] Mũsã ya ce masa, "Ko in bĩ ka a kan ka sanar da ni daga abin da aka sanar da kai na shiriya?" [18.67] Ya ce: "Lalle ne kai bã zã ka iya yin haƙuri tãre da nĩ, ba." [18.68] "Kuma yãya zã ka yi haƙuri a kan abin da ba ka kħwayeda shi ba ga jarrabãwa?" [18.69] Ya ce: "Za ka sãme ni, in Allah Yã so mai haƙuri kuma bã zan sãɓa maka ba ga wani umurni." [18.70] Ya ce: "To idan ka bĩ ni to kada ka tambaye ni daga kõme sai na lãbarta maka ambato(2) daga gare shi." [18.71] Sai suka tafi har a lõkacin da suka hau a cikin jirgi, ya hũje shi, ya ce, "Kã hũje shi dõmin ya nutsar da mutãnensa? Lalle ne, haƙĩƙa, kã zo da wani babban abu!" [18.72] Ya ce: "Ashe ban ce, lalle kai, bã za ka iya yin haƙuri tãre da ni ba?" [18.73] Ya ce: "Kada ka kãma ni da abin da na manta kuma kada ka kallafa mini tsanani ga al´amarĩna." [18.74] Sai suka tafi, har suka haɗu da wani yãro, sai ya kashe shi. Ya ce: "Ashe kã kashe rai tsarkakakke, bã da wani rai ba? Lalle ne haƙĩƙa ka zo da wani abu na ƙyãma." [18.75] Ya ce: "Shin, ban ce maka ba, lalle ne kai bã zã ka iya yin haƙuri tãre da nĩ ba?" [18.76] Ya ce: "Idan na tambaye(1) ka daga wani abu a bãyanta, to, kada ka abũce ni. Lalle ne, kã isa ga iyakar uzuri daga gare ni." [18.77] Sai suka tafi, har a lõkacin da suka je wa mutãnen wata alƙarya, suka nħmi mutãnenta da su bã su abinci, sai suka ƙi su yi musu liyãfa. Sai suka sãmi wani bango a cikinta yanã nufin ya karye, sai (Halliru) ya tãyar da shi mĩƙe. (Mũsã) ya ce: "Dã kã so, lalle ne dã kã karɓi ijãra a kansa." [18.78] Ya ce: "Wannan shi ne rabuwar tsakanina da tsakaninka. Zã ni gaya maka fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa." [18.79] "Amma Jirgin, to, ya zama na waɗansu matalauta ne sunã aiki(2) a cikin tħku, sai na yi niyyar in aibanta shi, alhãli kuwa wani sarki ya kasance a gaba gare su, yanã karɓħwar kõwane jirgi (lãfiyayye) da ƙwãce. [18.80] "Kuma amma yaron, to, uwãyensa sun kasance mũminai, to, sai muka ji tsõron ya kallafa musu kangara da kãfirci." [18.81] "Sai muka yi nufin Ubangijinsu Ya musanya musu mafi alhħri daga gare shi ga tsarkakuwa, kuma mafi kusantar tausayi." [18.82] "Kuma amma bangon, to, yã kasance na waɗansu yãra biyu ne, marãyu a cikin birnin, kuma akwai wata taska tãsu a ƙarƙashinsa, kuma ubansu ya kasance salĩhin mutum(3) ne, dõmin haka Ubangijinka Ya yi nufin su isa iyãkar ƙarfinsu, kuma sũ, su fitar da taskarsu, sabõda rahama ne daga Ubangijinka. Kuma ban yi shi ba daga umurnĩna. Wancan shĩ ne fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa." [18.83] Kuma suna tambayar ka daga Zulƙarnaini,(4) ka ce: "Zan karanta muku ambato daga gare shi." [18.84] Lalle ne Mũ Mun bã shi mulki a cikin ƙasa kuma Muka bã shi daga kõwane abu, hanya (zuwa ga murãdinsa). [18.85] Sai ya bi hanya. [18.86] Har a lõkacin da ya isa ga mafãɗar rãnã, kuma ya sãme ta tanã ɓacħwa a cikin wani ruwa mai baƙar lãkã, kuma ya sãmi waɗansu mutãne a wurinta. Muka ce: "Yã Zulƙarnaini imma dai ka azabtar kuma imma ka riƙi kyautatãwa a cikinsu." [18.87] Ya ce: "Amma wanda ya yi zãlunci, to zã mu azabta shi, sa´an nan a mayar da shi zuwa ga Ubangijinsa, sai kuma Ya yi masa azãba, azãba abar ƙyãma." [18.88] "Kuma amma wanda ya yi ĩmãni kuma ya aikata aikin ƙwarai to, zã mu yi sakamako a gare shi (watau kyauta) mai kyau,(1) kuma zã mu gaya masa sauƙi daga umurninmu." [18.89] Sa´an nan kuma ya bi hanya. [18.90] Har a lõkacin da ya isa ga mafitar rãnã, ya sãme ta tanã fita a kan waɗansu mutãne (waɗanda) ba Mu sanya musu wata kãriya ba daga barinta. [18.91] Kamar wancan alhãli kuwa haƙĩƙa, Mun kħwaye da jarrabãwa ga abin da ke gunsa. [18.92] Sa´an nan kuma ya bi hanya. [18.93] Har a lõkacin da ya isa a tsakãnin duwãtsu biyu, ya sãmi waɗansu mutãne daga gabãninsu. Ba su yi kusa su fahimci magana ba. [18.94] Suka ce: "Yã Zulƙarnaini! Lalle ne Yãjũja da Majũja mãsu ɓarna ne a cikin ƙasa. To, ko zã mu sanya harãji sabõda kai, a kan ka sanya wani danni a tsakãninmu da tsakãninsu?" [18.95] Ya ce: "Abin da Ubangijĩna Ya mallaka mini, a cikinsa yã fi zama alhħri. Sai ku taimakeni da ƙarfi, in sanya babbar katanga a tsakãninku da tsakãninsu." [18.96] "Ku kãwo mini guntãyen baƙin ƙarfe". (Suka kai masa) har a lõkacin da ya daidaita a tsakãnin duwãtsun biyu (ya sanya wutã a cikin ƙarfen) ya ce: "Ku hũra (da zugãzugai)." Har a lõkacin da ya mayar da shi wutã, ya ce: "Ku kãwo mini gaci (narkakke) in zuba a kansa." [18.97] Dõmin haka bã za su iya hawansa ba, kuma bã zã su iya hujħwa gare shi ba. [18.98] Ya ce: "Wannan wata rahama ce daga Ubangijĩna. Sai idan wa´adin(1) Ubangijĩna ya zo, ya mayar da shi niƙaƙƙe. Kuma wa´adin Ubangijĩna ya kasance tabbatacce." [18.99] Kuma Muka bar sãshensu a rãnar nan, yanã garwaya a cikin sãshe, kuma aka bũsa a cikin ƙaho sai muka tãra su, tãrãwa.(2) [18.100] Kuma Muka gitta Jahannama, a rãnar nan ga kãfirai gittãwa. [18.101] Waɗanda idãnunsu suka kasance a cikin rufi daga tunã(3) Ni, kuma sun kasance bã su iya saurãrãwa. [18.102] Shin fa, waɗanda suka kãfirta sun yi zaton (daidai ne) su riƙi waɗansu bãyĩNa,(4) majiɓinta baiciNa? Lalle ne, Mun yi tattalin Jahannama ta zama liyãfa ga kãfirai. [18.103] Ka ce: "Kõ mu gaya muku game da mafĩfita hasãra ga ayyuka?" [18.104] "Waɗanda aikinsu ya ɓace a cikin rãyuwar dũniya, alhãli kuwa sunã zaton lalle ne sũ, sunã kyautata, (abin da suke gani) aikin ƙwarai?" [18.105] Waɗancan ne waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Ubangijinsu, da kuma haɗuwa da Shi, sai ayyukansu suka ɓãci. Sabõda haka bã zã Mu tsayar musu da awo(5) ba a Rãnar Ƙiyãma. [18.106] Wancan ne sakamakonsu shĩ ne Jahannama, sabõda kãfircinsu, kuma suka riƙi ãyõyiNa da ManzanniNa abin izgili. [18.107] Lalle ne, waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, Aljannar Firdausi ta kasance ita ce liyãfa a gare su. [18.108] Suna madawwama a cikinta, bã su nħman makarkata daga barinta. [18.109] Ka ce: "Dã tħku(6) ta kasance tawada ga (rubũtun) kalmõmin Ubangijina, lalle ne dã tħkun ta ƙãre a gabãnin kalmõmin Ubangijĩna su ƙãre, kuma kõda mun jħ da misãlinsa dõmin ƙari." [18.110] Ka ce: "Nĩ, mutum ne kawai kamarku, anã yin wahayi zuwa gare ni cewa: Lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa Guda ne, sabõda haka wanda ya kasance yanã fãtan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kõwa ga bauta wa Ubangijinsa."(7) @MARYAM Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [19.1] K̃. H. Y. I . Ṣ̃. [19.2] Ambaton rahamar Ubangijinka ne ga BawanSa Zakariyya. [19.3] A lõkacin da ya kirãyi Ubangijinsa, kira ɓõyayye. [19.4] Ya ce: "Yã Ubangijina! Lalle ne nĩ, ƙashi na daga gare ni ya yi rauni, kuma kaina ya kunnu da furfura, kuma ban kasance marashin arziki ba game da kiranKa, yã Ubangiji!" [19.5] "Kuma lalle nĩ, na ji tsõron(1) dangi a bãyãna, kuma mãtãta ta kasance bakarãriya! Sai ka bã ni wani mataimaki daga wajenKa." [19.6] "Ya gãjħ ni, kuma ya yi gãdo daga gidan Yãƙũba. Kuma Ka sanya shi yardajje, yã Ubangiji!" [19.7] (Allah Ya karɓa) "Yã zakariyya! Lalle ne Mũ, Munã yi maka bushãra da wani yãro, sunansa Yahaya. Ba Mu sanya masa wani takwara ba a gabãni." [19.8] Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Yãya wani yãro zai kasance a gare ni, alhãli kuwa mãtãta ta kasance bakarãriya, kuma gã shi nã kai ga matuƙa ta tsũfa?" [19.9] Ya ce: "Kamar wancan Ubangijinka Ya ce. Shĩ, a gare Ni mai sauƙi ne, kuma haƙĩƙa Na halitta ka a gabãnin haka, alhãli ba ka kasance kõme ba." [19.10] Ya ce: "Yã Ubangijina! Ka sanya mini alãma." Ya ce: "Alamarka ita ce ka kãsa yi wa mutãne magana a darũruwa uku daidai." [19.11] Sai ya fita a kan mutãnensa daga masallãci, sa´an nan ya yi ishãra zuwa gare su da cħwa, "Ku yi tasbĩhi sãfe da yamma." [19.12] Yã Yahaya! Ka kãma littãfi da ƙarfi. Kuma Muka bã shi hukunci yanã yãro.(1) [19.13] Kuma (Muka sanya shi) abin girmamãwa daga gunMu, kuma mai albarka, kuma ya kasance mai ɗã´ã da taƙawa. [19.14] Kuma mai biyayya ga mahaifansa biyu, kuma bai kasance mai girman kai mai sãɓo ba. [19.15] Kuma aminci ya tabbata a gare shi a rãnar da aka haife shi da rãnar da yake mutuwa da rãnar da ake tãyar da shi yanã mai rai. [19.16] Kuma ka ambaci Maryamu(2) a cikin Littãfi, a lõkacin da ta tsallake daga mutãnenta a wani wuri, a għfen gabas. [19.17] Sa´an nan ta riƙi wani shãmaki daga barinsu. Sai Muka aika rũhinMu zuwa gare ta. Sai ya bayyana a gare ta da siffar mutum madaidaci. [19.18] Ta ce: "Lalle nĩ inã nħman tsari ga Mai, rahama daga gare ka, idan ka kasance mai tsaron addini!" [19.19] Ya ce: "Abin sani kawai, ni Manzon Ubangijinki ne dõmin in bãyar da wani yãro tsarkakke gare ki." [19.20] Ta ce: "A inã yãro zai kasance a gare ni alhãli kuwa wani mutum bai shãfe ni ba, kuma ban kasance kãruwa ba?" [19.21] Ya ce: "Kamar wancan Ubangijinki Ya ce. Shĩ, a gare Ni mai sauƙi(3) ne. Kuma dõmin Mu sanya shi wata alãma ga mutãne, kuma wata rahama ce daga gare Mu.´ Kuma abin yã kasance wani al´amari hukuntacce." [19.22] Sai ta yi cikinsa, sai ta tsallake da shi ga wani wuri mai nĩsa. [19.23] Sai nãƙuda ta kai ta zuwa ga wani kututturen dabĩniya, ta ce "Kaitona, dã dai na mutu a gabãnin wannan kuma na kasance wani abu wulakantacce wanda aka manta!" [19.24] Sai (yãron da ta haifa) ya(4) kira ta daga ƙarƙashinta, "Kada ki yi baƙin ciki! Haƙĩƙa Ubangijinki Ya sanya wani marmaro a ƙarƙashinki. [19.25] "Kuma ki girgiza zuwa gare ki game da kututturen dabĩnon ya zuba a kanki yanã ´ya´yan dabĩno, ruɗabi nunannu." [19.26] "Sai ki ci kuma ki sha kuma ki ji sanyi ga idãnunki.(1) To, idan kin ga wani aya daga mutãne, sai ki ce, ´Lalle nĩ, na yi alwãshin azumi dõmin Mai rahama sabõda haka bã zan yi wa wani mutum magana ba." [19.27] Sai ta je wa mutãnenta tanã auke da shi. Suka ce: "Yã Maryamu! Lalle ne, haƙĩƙa kin zo da wani abu mai girma! [19.28] "Yã ´yar´uwar Hãrũna! Ubanki bai kasance mutumin alfãsha ba, kuma uwarki ba ta kasance kãruwa ba." [19.29] Sai ta yi ishãra zuwa gare shi, suka ce: "Yãya zã mu yi magana da wanda ya kasance a cikin shimfiar tsumma yanã jãrĩri?" [19.30] Ya ce: "Lalle ne, nĩ bãwan Allah ne Allah Yã bã ni Littãfi kuma Ya sanya ni Annabi."(2) [19.31] "Kuma Yã sanya ni mai albarka a inda duk na kasance kuma Ya umurce ni da yin salla da zakka matuƙar inã da rai." [19.32] "Kuma mai biyayya ga uwãta, kuma bai sanya ni mai kaushin zũciya ba marashin alhħri." [19.33] "Kuma aminci ya tabbata a gare ni a rãnar da aka haife ni da rãnar da nake mutũwa da rãnar da ake tãyar da ni inã mai rai." [19.34] Wancan ne Ĩsã ɗan Maryamu, maganar gaskiya wadda suke shakka a cikinta. [19.35] Bã ya kasancħwa ga Allah Ya riƙi wani ɗã.(3) Tsarki ya tabbata a gare shi! Idan Yã hukunta wani al´amari sai kawai Ya ce masa, "Kasance." Sai ya dinga kasan cħwa. [19.36] "Kuma lalle Allah ne Ubangijina(4) kuma Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Wannan shi ne tafarki madaidaici." [19.37] Sai ƙungiyõyin(5) suka sãɓã wa jũna a tsakãninsu. To, bõne ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta daga halartar yini mai girma. [19.38] Mħne ne ya yi jinsu,(6) kuma mħne ne ya yi ganinsu a rãnar da suke zo Mana! Amma azzãlumai sunã a cikin ɓata bayyananna. [19.39] Kuma ka yi musu gargaɗi da rãnar nadãma a lõkacin da aka hukunta al´amari alhãli kuwa sunã a cikin ɓãta, kuma sũ bã su yin ĩmãni. [19.40] Lalle ne Mũ, Mũ ne ke gãdon ƙasa da wanda yake a kanta, kuma zuwa gare Mu ake mayar da su. [19.41] Kuma ambaci Ibrãhĩm(2) a cikin Littafi. Lalle shi ya kasance mai yawan gaskatãwa, Annabi. [19.42] A lõkacin da ya ce wa ubansa, "Yã bãba! Don me kake bauta wa abin da bã ya ji, kuma bã ya ga ni, kuma ba ya wadãtar da kõme daga barinka?" [19.43] "Yã bãba! Lalle ni, haƙĩƙa abin da bai je maka ba na ilmi ya zo mini, sabõda haka ka bĩ ni in shiryar da kai wani tafarki madaidaici." [19.44] "Yã bãba! Kada ka bauta wa Shaiɗan. Lalle Shaiɗan ya kasance mai saɓãwa ga Mai rahama." [19.45] "Yã bãba! Lalle ne ni inã tsõron wata azãba daga Mai rahama ta shãfe ka, har ka zama masõyi ga Shaiɗan." [19.46] Ya ce: "Ashe, mai gudu ne kai daga gumãkãna? Yã Ibrãĩm! Lalle ne, idan ba ka hanu ba, haƙĩ ƙa, zan jħfe ka. Kuma ka ƙaurace mini tun kanã mai mutunci." [19.47] Ya ce: "Aminci(3) ya tabbata a gare ka! zan nħmi Ubangijina Ya gãfarta maka. Lalle Shi Ya kasance Mai girmamãwa gare ni." [19.48] "Kuma inã nĩsantar ku da abin da kuke kira, baicin Allah kuma inã kiran Ubangijina, tsammãnin kada in zama marashin arziki game da kiran Ubangijina." [19.49] To, sa´ad da ya nĩsance su da abin da suke bautãwa baicin Allah, Muka bã shi Is´hãƙa da Ya´aƙuba alhãli kuwa kõwanensu Mun mayar da shi Annabi. [19.50] Kuma Muka yi musu kyauta daga RahamarMu, kuma Muka sanya musu harshen gaskiya(4) maɗaukaki. [19.51] Kuma ka ambaci Mũsã a cikin Littãfi. Lalle ne shi, yã kasance zãɓaɓɓe, kuma yã kasance Manzo, Annabi. [19.52] Kuma Muka kira shi daga għfen dũtse na dãma kuma Muka kusanta shi yanã abõkin gãnãwa. [19.53] Kuma Muka yi masa kyauta daga RahamarMu da ɗan´uwansa Hãrũna, ya zama Annabi. [19.54] Kuma ka ambaci Ismã´ila a cikin Littãfi. Lalle shi, yã kasance mai gaskiyar alkawari, kuma yã kasance Manzo, Annabi. [19.55] Kuma yã kasance yanã umurnin mutãnens(1) da salla da zakka. Kuma yã kasance yardajje a wurin Ubangijinsa. [19.56] Kuma ka ambaci Idrĩsa a cikin Littãfi. Lalle shi, ya kasance mai yawan gaskatãwa, Annabi. [19.57] Muka ɗaukaka shi a wuri maɗaukaki. [19.58] Waɗancan sũ ne waɗanda Allah Ya yi wa ni´ima daga Annabãwa daga zurriyar Ãdamu, kuma daga waɗanda muka ɗauka tãre da Nũhu, kuma daga zurriyar Ibrãhĩm da Isrã´ila, kuma daga waɗanda Muka shiryar kuma Muka zãɓe su. Idan anã karãtun ãyõyin Mai rahama a kansu, sai su fãɗi sunã mãsu sujada kuma mãsu kũka. [19.59] Sai waɗansu ´yan bãya(2) suka maye a bãyansu suka tõzarta salla, kuma suka bi sha´awõwinsu. To, da sannu zã su hau da wani sharri. [19.60] Fãce wanda ya tũba, kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aiki na ƙwarai. To, waɗannan sunã shiga Aljanna, kuma bã a zãluntar su da kõme. [19.61] Gidãjen Aljannar zama wadda Mai rahama ya yi alkawarin bãyarwa ga bãyinSa (mãsu aikin ĩmãni) a fake. Lalle ne shĩ, alkawarin ya kasance abin riskuwa. [19.62] Bã su jin yasassar magana a cikinta, fãce sallama. Kuma sunã da abinci, a cikinta, sãfe da maraice. [19.63] Wancan Aljannar ce wadda Muke gãdar da wanda ya kasance mai aiki da taƙawa daga bãyiNa. [19.64] (Sunã mãsu cħwa) "Kuma bã mu sauka(3) Fãce da umuruin Ubangijinka (Muhammad). Shĩ ne da mulkin abin da ke a gaba gare mu da abin da ke a bãyanmu da abin da ke a tsakãnin wannan." Kuma(4) (Ubangijinka bai kasance wanda ake mantãwa ba. [19.65] Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu. sai ka bauta Masa, kuma ka yi haƙuri ga bautarsa. Shin kã san wani takwara a gare shi? [19.66] Kuma mutum yana cħwa, "Shin idan na mutu lalle ne haƙĩ ƙa da sannu zã a fitar da ni inã mai rai?" [19.67] Shin, kuma mutum bã zai tuna ba cħwa lalle ne Mun halitta shi a gabãni, alhãli kuwa bai kasance kõme ba? [19.68] To, Munã rantsuwa da Ubangijinka, lalle ne, Muna tãyar da su da kuma shaianun sa´an nan, kuma lalle Muna halatar da su da kuma Shaiɗanun sa´an nan, kuma, lalle Muna halatar da su a għfen Jahannama sunã gurfãne. [19.69] Sa´an nan kuma lalle Munã fizge wanda yake mafi tsananin girman kai ga Mai rahama daga kõwace ƙungiya. [19.70] Sa´an nan kuma lalle Mũ ne Mafi sani ga waɗanda suke sũ ne mafiya cancantar ƙõnuwa da ita. [19.71] Kuma bãbu kõwa daga gare ku sai mai tuzga mata.(1) Yã kasance wajibi ga Ubangijinka, hukuntacce. [19.72] Sa´an nan kuma Mu tsħrar da waɗanda suka yi aiki da taƙawa, kuma Mu bar azzãlumai a cikinta gurfãne. [19.73] Kuma idan anã karatun ãyõyinMu, bayyanannu a kansu, sai waɗanda suka kãfirta su ce wa waɗanda suka yi ĩmãni, "Wanne daga ƙungiyõyin biyu ya fi zama mafi alhħri ga matsayi, kuma mafi kyaun majalisa?" [19.74] Kuma da yawa daga mutãnen ƙarni Muka halakar a gabãninsu sũ (waɗandaMuka halakar) in ne mafi kyaun kãyan ãki da magãnã.(2) [19.75] Ka ce: "Wanda ya kasance a cikin ɓata sai Mai rahama Ya yalwata masa yalwatãwa, har idan sun ga abin da ake yi musu wa´adi, imma azãba kõ sã´a, to zã su sani, wane ne yake shĩ ne, mafi sharri ga wuri, kuma mafi rauni ga runduna!" [19.76] Kuma Allah na ƙãra wa wa ɗanda suka nħmi shiryuwa da shiriya. Kuma ayyuka mãsu wanzuwa na ƙwarai ne mafi alhħri awurin Ubangijinka ga lãda, kuma mafi alhħri ga makõma. [19.77] Shin, ka ga wanda ya kãfirta da ayõyinMu, kuma ya ce: "Lalle ne zã a bã ni dũkiya da ɗiya?" [19.78] Shin, yã tsinkãyi gaibi ne, kõ kuwa yã ɗauki wani alkawari daga Mai rahama ne? [19.79] ôaha! zã mu rubũta abin da yake faɗa, kuma Mu yalwata masa, daga azãba, yalwatãwa. [19.80] Kuma Mu gãde shi ga abin da yake faɗa, kuma ya zo Mana yanã shi kɗai. [19.81] Kuma suka riƙi gumãka,(1) baicin Allah, dõmin su kãsance mataimaka a gare su. [19.82] ôaha! Zã su kãfirta da ibãdarsu, kuma su kasance maƙiya a kansu. [19.83] Shin, ba ka gani ba cħwa Mun saki shaiɗanu(2) a kan kãfirai sunã shũshũta su ga zunubi shũshũtãwa? [19.84] Sabõda haka kada ka yi gaggawa a kansu, Munã yi musu ƙidãyar ajali ne kawai, ƙidãyãwa. [19.85] A rãnar da Muka tãra mãsu taƙawa zuwa ga Mai rahama sunã bãƙin girma. [19.86] Kuma Munã kõra mãsu laifi zuwa Jahannama, gargaãwa. [19.87] Ba su mal1akar cħto fãce wanda ya riƙi alkawari a wurin Mai rahama. [19.88] Kuma suka ce: "Mai rahama Yã riƙi ã!" [19.89] Lalle ne haƙĩƙa kun zo da wani abu mai girman mũni. [19.90] Sammai sunã kusa su tsattsage sabõda shi, kuma ƙasa ke kħce kuma duwãtsu su faɗi sunã karyayyu. [19.91] Dõmin sun yi da´awar ɗã ga Mai rahama. [19.92] Alhãli bã ya kamata ga Mai rahama ya riƙi wani ɗã. [19.93] Dukkan wanda yake a cikin sammai da ƙasa bai zama ba fãce mai jħ wa Mai rahama ne yanã bãwã. [19.94] Lalle ne haƙĩƙa Yã lissafe su, kuma ya ƙidãye su, ƙidãya. [19.95] Kuma dukan kõwanensu mai jħ Masa ne a Rãnar Ƙiyãma yanã shi kaɗai. [19.96] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, Mai rahama zai sanya musu so.(1) [19.97] Sa´an nan Ibin sani kawai Mun sauƙaƙar da shi (Alƙur´ãni) a harshenka, dõmin ka yi bushãra da shi ga mãsu aiki da taƙawa kuma ka yi gargaɗi da shi ga mutãne mãsu tsananin husũma. [19.98] Kuma da yawa Muka halakar da mutãnen ƙarnõni a gabãninsu. Shin kanã jin mõtsin wani guda daga gare su, kõ kuwa kanã jin wata ɗuriya tãsu? @THAAHAA Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [20.1] Ɗ. H. [20.2] Ba Mu saukar da Alƙur´ãni a gare ka dõmin ka wahala ba. [20.3] Fãce dõmin tunãtarwa ga wanda ke tsõron Allah. [20.4] (An saukar da shi) saukarwa daga wanda Ya halitta ƙasa da sammai maɗaukaka. [20.5] Mai rahama, Ya daidaita(2) a kan Al´arshi. [20.6] Abin da yake a cikin sammai nãSa ne, da abin da yake a cikin ƙasa da abin da yake a tsakãninsu da abin da ke ƙarƙashin turɓãya. [20.7] Kuma idan ka bayyana da magana, to, lalle Shi, Yanã sanin asĩri da mafi bõyuwa. [20.8] Allah bãbu abin bautãwa fãce Shi. Yanã da sunãye mafiya kyau. [20.9] Kuma shin, lãbarin Mũsã yãje maka? [20.10] A lõkacin da ya ga wata wuta, sai ya ce wa iyãlinsa, "Ku dãkata. Lalle ne nĩ, na tsinkãyi wata wuta tsammãnĩna in zo mukuda makãmashi daga gare ta, kõ kuwa in sãmi wata shiriya a kan wutar." [20.11] Sa´an nan a lõkacin da ya je mata, aka kira shi, "Ya Mũsã!" [20.12] "Lalle ne, Nĩ ne Ubangijnka, sai ka ɗħbe takalmanka(3) Lalle ne kanã a rãfin nan abin tsarkakħwa, Ɗuwa." [20.13] "Kuma Nĩ Nã zãɓe ka. Sai ka saurãra ga abin da ake yin wahayi." [20.14] "Lalle, Nĩ Ni ne Allah. Bãbu abin bautawa fãce Ni. Sai ka bauta Mini, kuma ka tsayar da salla dõmin tuna Ni." [20.15] "Lalle ne Sa´a mai zuwa ce, lnã kusa da In ɓõye ta dõmin a sãka wa dukan rai da abin da yake aikatãwa." [20.16] "Sabõda haka, kada wanda bã ya yin ĩmãni da ita kumaya bi son zuciyarsa, ya taushe ka daga gare ta har ka halaka." [20.17] "Kuma wãce ce waccan ga dãmanka yã Mũsa!" [20.18] Ya ce: "Ita sandãta ce, inã dõgara a kanta, kuma inã kakkaɓar ganye da ita a kan ƙananan bisãshħna kuma inã da waɗansu bukãtõci(1) na dabam a gare ta." [20.19] Ya ce: "Ka yi jĩfa da ĩta, yã Mũsã!" [20.20] Sai ya jħfa ta. Sai gã ta dabbar macĩjiya, tanã tafiya da gaggãwa. [20.21] Ya ce: "Ka kãma ta kuma kada ka ji tsõro. Za Mu mayar da ita ga hãlinta na farko." [20.22] "Kuma ka haɗa hannunka zuwa ga damtsenka, ya fita yanã fari, bãbu sõfane, wata ãyã ta dabam." [20.23] "Dõmin Mu nũna maka daga ãyõyinMu manya." [20.24] "Ka tafi zuwa ga Fĩr´auna. Lalle shĩ ya ƙħtare haddi (da girman kai)." [20.25] Ya ce: "Ya Ubangiji! Ka buɗa(2) mini, ƙirjĩna. [20.26] "Kuma ka sauƙaƙe mini al´amarĩna." [20.27] "Kuma Ka warware mini wani ƙulli daga harshħna." [20.28] "Su fahimci maganãta." [20.29] "Kuma Ka sanya mini wani mataimaki daga mutãnena." [20.30] "Hãrũna ɗan´uwana." [20.31] "Ka ƙarfafa halittata da shi." [20.32] "Kuma Ka shigar da shi a cikin al´amarina." [20.33] "Dõmin mu tsarkake Ka da yawa." [20.34] "Kuma mu tuna Ka da yawa." [20.35] "Lalle Kai, Ka kasance Mai gani gare mu." [20.36] Ya ce: "Lalle ne, an bã ka rõƙonka, yã Mũsã!" [20.37] "Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun yi wata baiwa gare ka a wani lõkacin na dabam." [20.38] "A lõkacin da Muka yi wahayin abin da aka yi wahayi zuwa ga uwarka." [20.39] "cħwa, Ki jħfa shi a cikin akwatin nan, sa´an nan ki jħfa shi a cikin kõgi, sa´an nan kogin ya jefa shi a gãɓa, wani maƙiyi Nãwa kuma maƙiyi nãsa ya ɗauke shi.´ Kuma Na jħfa wani so daga gare Ni a kanka. Kuma dõmin a riƙe ka da kyau a kan ganiNa." [20.40] "A sa´ad da ´yar´uwrka ke tafiya har ta ce, shin, in shiryar da ku ga wanda ke rħnonsa?´ Sai Muka mayar da kai zuwa ga uwarka dõmin idonta ya yi sanyi(1) kuma bã zã ta yi baƙin ciki ba. Kuma kã kashe wani rai, sa´an nan Muka tsħrar da kai daga baƙin ciki, kuma Muka fitine ka da waɗansu fitinõni. Sa´an nan ka zauna shħkaru a cikin mutãnen Madyana. Sa´an nan kuma ka zo a kan wata ƙaddara, yã Mũsã! [20.41] "Kuma Na zãɓe ka dõmin Kaina." [20.42] "Ka tafi kai da ɗan´uwanka game da ãyõyiNa, kuma kada ku yi rauni ga ambatõNa." [20.43] "Ku tafi kũ biyu zuwa ga Fir´auna. Lalle shĩ ya ƙħtare haddi (ga girman kai)." [20.44] "Sai ku gaya masa magana mai laushi,(2) tsammãninsa yanã tunãwa kõ kuwa ya ji tsõro." [20.45] Su biyu suka ce: "Ya Ubangijinmu! Lalle ne munã tsõron ya yi gaggawa a kanmu, kõ ya ƙħtare haddi." [20.46] Ya ce: "Kada ku ji tsõro. Lalle Nĩ, Inã tãre da ku, Inaji, kuma Inã gani." [20.47] "Sai ku jħ masa sa´an nan ku ce, Lalle mũ, Manzanni biyune na Ubangijinka, sai ka saki Banĩ Isrã´ĩla tãre da mu. Kuma kada ka yi musu azãba. Haƙĩƙa mun zomaka da wata ãyã daga, Ubangijinka. Kuma aminci ya tabbata ga wanda ya bi shiriya." [20.48] "Lalle mũ, haƙĩƙa, an yi wahayi zuwa gare mu, cħwaazãba tanã a kan wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya." [20.49] Ya ce: "To, wãne ne Ubangijinku? Ya Mũsã!" [20.50] Ya ce: "Ubangijinmu Shi ne wanda Ya bai wa dukan kõme halittarsa, sa´an nan Ya shiryar." [20.51] Ya ce: "To, mħne hãlin ƙarnõnin farko?" [20.52] Ya ce: "Saninsu yanã a wurin Ubangijĩna, Ubangijĩna bã Ya ɓacħwa kuma bã Ya mantuwa." [20.53] "Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma Ya shigar muku da hanyõyi a cikinta, kuma Ya saukar da ruwa daga sama." Sa´an nan game da shi(1) Muka fitar da nau´i-nau´i daga tsirũruwa dabam-dabam. [20.54] Ku ci kuma ku yi kiwon dabbõbin ni´imarku. Lalle ne, a cikin wannan akwai ãyõyi ga masu hankali. [20.55] Daga gare ta(2) Muka halitta ku, kuma a cikinta Muke mayar da ku, kuma daga gare ta Muke fitar da ku a wani lõkaci na dabam. [20.56] Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun nũna masa ãyõyinMu dukansu sai ya ƙaryata, kuma ya ƙiya! [20.57] Ya ce: "Shin kã zo mana ne dõmin ka fitar da mu daga ƙasarmu game da sihirinka, yã Mũsã?" [20.58] "To, lalle ne munã zo maka da wani sihiri irinsa. Sai ka sanya wani wa´adi a tsakãninmu da tsakãninka bã mu sãɓa masa mũ kai kuma, bã ka sãɓãwa, a wani wuri mai dãcħwa." [20.59] Ya ce: "Wa´adinku shi ne rãnar ƙawa kuma a tãra mutãne da hantsi." [20.60] Sai Fir´auna ya jũya, sa´an nan ya tãra mugunyar dabãrarsa, sa´an nan kuma ya zo. [20.61] Mũsã ya ce musu, "Kaitõnku! Kada ku ƙirƙira ƙarya ga Allah har Ya tumɓuke ku da wata azãba. Kuma wanda ya ƙirƙira ƙarya, yã tãɓe." [20.62] Sai suka yi jãyayya ga al´amarinsu a tsakãninsu kuma suka asirta gãnawa. [20.63] Suka ce: "Lalle ne waɗannan biyun, haƙĩƙa masihirta ne sunã nufin su fitar da ku daga ƙasarku(3) game da sihirinsu kuma su tafi da tabĩ´arku mafĩficiya." [20.64] "Sai ku haɗa dabãrarku sa´an nan kuma ku tafi a sahu guda, kuma haƙĩƙa, wanda ya rinjãya, a yau, ya rabbanta." [20.65] Suka ce: "Ya Mũsã! Imma ka jefa, ko kuma mu kasance farkon mai jħfawa." [20.66] Ya ce: "ôa, ku jħfa." Sai gã igiyoyinsu da sandunansu anã sũranta su a gare shi, daga sihirinsu, lalle sunã tafiya da sauri. [20.67] Sai Mũsã ya ji tsõro a cikin ransa. [20.68] Muka ce: "Kada ka ji tsõro. lalle kai ne mafi ɗaukaka." [20.69] "Kuma ka jħfa abin da ke a cikin hannun dãmanka, ta cafe abin da suka aikata. Lalle ne abin da suka aikata mãkircin masihirci ne kuma masihirci bã ya cin nasara a duk inda ya je." [20.70] Sai aka jħfar da masihirtan sunã mãsu sujada, suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin Hãrũna da Mũsã." [20.71] Ya ce: "Kun yi ĩmãni sabõda shi a gabãnin in yi muku izni? Lalle shĩ, haƙĩƙa, babbanku ne wanda ya sanar da ku sihirin! To, lalle ne zan kakkãtse hannayenku da ƙafãfunku a tarnaƙi kuma lalle zan tsĩre ku a cikin kututturan itãcen dabĩno, kuma lalle zã ku sani wanenmu ne mafi tsananin azãba kuma wãne ne mafi wanzuwar (azãba)." [20.72] Suka ce: "Bã zã mu fĩfĩta ka ba faufau a kan abin da ya zo mana na hujjõji. Munã rantsuwa da wanda Ya ƙãga halittarmu sai ka hukunta abin da kake mai hukuntãwa, ai kanã ƙãre wannan rãyuwar dũniya kawai ne." [20.73] "Lalle mũ, mun yi ĩmãni da Ubangijinmu dõmin Ya gãfarta mana laifuffukanmu da abin da ka tĩlasta mu a kansa na sihiri. Kuma Allah ne Mafi alhħri, kumaMafi wanzuwa." [20.74] Lalle(1) shĩ wanda ya je wa Ubangijinsa yanã mai laifi, to lalle ne yanã da Jahannama, bã ya mutuwa a cikinta kuma bã ya rãyuwa. [20.75] Kuma wanda ya je Masa yanã mai ĩmãni, alhãli kuwaya aikata aikin ƙwarai to waɗannan sunã da darajõji maɗaukaka. [20.76] Gidãjen Aljannar zama kõguna na gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwama a cikinsu. Kuma wannan ne sakamakon wanda ya tsarkaku. [20.77] Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun yi wahayi zuwa ga Mũsã cħwa, "Ka yi tafiyar dare da bãyiNa. Sa´an nan ka dõka musu hanya a cikin tħku tana ƙħƙasasshiya, bã ka tsõron riskuwa, kuma bã ka fargabar nutsħwa." [20.78] Sai Fir´auna ya bi su game da rundunarsa. Sai abin da ya rufe su daga tħku ya rufe su. [20.79] Kuma Fir´auna ya ɓatar da mutãnensa, kuma bai shiryar(dasu) ba. [20.80] Yã Banĩ Isrã´ĩla! Lalle Mun tsħrar da ku daga maƙiyinku, kuma mun yi muku wa´adi a għfen Dũtsen nan na dãma, kuma Mun sassaukar da darɓa da tattabaru dõminku. [20.81] Ku ci daga mãsu dãɗin abin da Muka azurtã ku kuma kada ku ƙħtare haddi a cikinsa har hushĩNa ya sauka a kanku. Kuma wanda hushĩNa ya sauka a kansa, to, lalle ne, ya fãɗi. [20.82] Kuma lalle Nĩ haƙĩƙa Mai gãfara ne ga wanda ya tũba kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aikin ƙwarai, sa´an nan kuma ya nħmi shiryuwa. [20.83] "Kuma mħne ne ya gaggautar(1) da kai ga barin mutãnenka? Yã Mũsã!" [20.84] Ya ce: "Su ne waɗannan a kan sãwũna, kuma na yi gaggãwa zuwa gare Ka, yã Ubangiji! Dõmin Ka yarda." [20.85] Ya ce: "To, lalle ne, haƙĩƙa, Mun fitini, mutãnenka daga bayãnka, kuma sãmiri ya ɓatar da su." [20.86] Sai Mũsã ya kõma zuwa ga mutãnensa yanã mai hushi, mai baƙin ciki, ya ce: "Yã mutãnħna! shin, Ubangijinku bai yi muku wa´adi ba, wa´adi mai kyau? Shin, lõkacin ya yi tsãwo a kanku ne, kõ kun yi nufi ne wani hushi ya sauka a kanku daga Ubangijinku, sabõda haka kuka sãɓã wa alkawarĩna?" [20.87] Suka ce: "Ba mu sãɓa wa alkawarinka(2) ba da ĩkonmu kuma amma an ɗõra mana waɗansu kãya masu nauyi daga abin ƙawar mutãnen ne, sai muka jħfar da su. Sa´an nan kamar haka ne sãmiri ya jħfa." [20.88] "Sai ya fitar musu da wani maraƙi, jikin mutãne, yanã rũri, sa´an nan suka ce: wannan ne gunkinku kuma gunkin Mũsã, sai ya manta." [20.89] Shin, to, bã su ganin cħwabã ya mayar musu da magana, kuma bã ya mallakar wata cũta a gare su, kuma bã ya mallakar amfãni? [20.90] Kuma, haƙĩƙa, Hãrũna yã ce musu daga gabãni, "Yã mutãnħna! Lalle an fitinħ ku da shi ne kawai. Kuma lalle Ubangijinku Mai rahama ne, sai ku bi ni, kuma ku yi ɗã´ã ga umurnĩna." [20.91] Suka ce: "Ba zã mu gushe ba faufau a kansa munã mãsu lazimta,(1) sai Mũsã ya kõmo zuwa gare mu." [20.92] (Mũsã) ya ce: "Yã Hãrũna! Mħ ya hane ka, sa´ad da kagan su sun ɓace." [20.93] "Ba ka bĩ ni ba! Shin, to, ka sãɓã wa umurnina ne?" [20.94] (Hãrũna) ya ce: "Yã ɗãn´uwãna! Kada ka yi kãmu ga għmũna kõ ga kaina. Lalle nĩ, nã ji tsõron ka ce: Ka rarraba a tsakãnin Banĩ Isrã´ĩla kuma ba ka tsare maganata ba." [20.95] (Mũsã) ya ce: "Mħne ne babban al´amarinka? Ya Sãmiri!" [20.96] (Sãmiri) ya ce: "Nã ga abin da ba su gan shi ba shi, sai na yi damƙa, damƙa guda daga kufan sãwun Manzon, sa´an nan na jħfa ta. Kuma haka dai raina ya ƙawãta mini." [20.97] (Mũsã) ya ce: "To, ka tafi, sabõda haka lalle ne kanã da a cikin rãyuwarka, ka ce ´Bãbu shãfa´ kuma kanã da wani ma´alkawarta, bã zã a sãɓa maka gare ta ba. Kuma ka dũba zuwa ga gunkinka wanda ka yini a kansa kanã mai lazimta. Lalle ne muna ƙõne shi,(2) sa´an nan kuma munã shħƙe shi, a cikin tħku, shħƙħwa." [20.98] Abin sani kawai abin bautãwarku Allah kawai ne wanda bãbu wani abin bautãwa, fãce Shi kuma Yã yalwaci(3) dukkan kõme da ilmi. [20.99] Kamar wancan ne Muke lãbartãwa(1) a gare ka, daga lãbãran abin da ya gabãta, alhãli kuwa haƙĩƙa, Mun bã ka zikiri (Alƙur´ãni) daga gunMu. [20.100] Wanda ya kau da kai daga gare shi, to, lalle shĩ, yanãɗaukar wani nauyi a Rãnar Ƙiyãma. [20.101] Sunã madawwama a cikinsa, kuma yã mũnana ya zama abin ɗauka, a Rãnar Ƙiyãma. [20.102] A Rãnar da ake hũrãwa a cikin ƙãho kuma Munã tãra mãsu laifi, a rãnar nan, sunã mãsu shũɗãyen idãnu. [20.103] Suna ɓõye magana a tsakãninsu, (Sunã ce wa jũna) "Ba ku zauna ba (a cikin dũniya) fãce kwãna gõma." [20.104] Mu ne mafi sani ga abin da suke faɗa a sa´ad da mafĩficinsu ga hanya ke cħwa, "Ba ku zauna ba fãce a yini guda." [20.105] Kuma sunã tambayar ka daga duwãtsu(2) sai ka ce: "Ubangijina Yana shħƙe su shħƙħwa, [20.106] Sa´an nan Yanã barin (wurinsu) faƙo mai santsi. [20.107] "Bã ka ganin karkata a cikinsa, kuma bã ka ganin wani tudu." [20.108] A rãnar nan sunã biyar mai kira, bãbu karkata a gare shi, kuma sautuka suka yi kawaici ga Mai rahama, bã ka sauraren kõme fãce sautin tafiya. [20.109] A yinin nan cħto bã ya yin amfãni fãce wanda Mai rahama Ya yi masa izni kuma Ya yarda da shi, da magan(3) [20.110] Yanã sanin(4) abin da ke a gaba gare su da abin da ke bãyansu, kuma bã su kħwayħwa da shi ga sani. [20.111] Kuma fuskõki suka ƙanƙan da kai ga Rãyayye,Tsayayye, alhãli kuwa wanda ya ɗauko wani zãlunci ya tãɓe. [20.112] Kuma wanda ya aikata wani abu daga ayyukan ƙwarai alhãli kuwa yanã mai ĩmãni, to, bã ya tsõron wani zãlunci ko wata naƙasa. [20.113] Kuma haka Muka saukar da shi, Alƙur´ãni, yanã abin karantãwa, da Larabci kuma Muka jujjuya misãlai, a cikinsa, na tsõratarwa, tsammãninsu, sunã yin taƙawa ko ya sabbaba musu wata wa´aztuwa. [20.114] Sa´an nan Allah Mamallaki, Tabbatacce Yã ɗaukaka. Kuma kada ka yi gaggãwa(1) da Alƙur´ãni a gabãnin a ƙãre wahayinsa zuwa gare ka. Kuma ka ce: "Yã Ubangiji! Ka ƙãra mini ilmi." [20.115] Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun yi alkawari zuwa ga Ãdamu a gabãnin wannan, sai ya manta, kuma ba Mu sãmi ƙarfin zũciya a gare shiba. [20.116] Kuma sa´ad da Muka ce wa malã´iku, "Ku yi sujada ga Ãdamu." Sai suka yi sujada, fãce Iblĩsa, yã ƙiya. [20.117] Sai Muka ce: "Ya Ãdamu! Lalle ne wannan maƙiyi(2) ne gare ka da kuma ga mãtarka, sabõda haka kada ya fitar da ku daga Aljanna har ku wahala." [20.118] Lalle ne kã sãmu bã zã ka ji yunwa ba a cikinta, kuma bã zã ka yi tsiraici ba. [20.119] "Lalle kai, bã zã ka ji ƙishirwa ba, kuma bã zã ka shiga hantsi ba." [20.120] Sai shaiɗan ya sanya waswãsi zuwa gare shi, ya ce: "Yã Ãdamu! Shin, in shiryar da kai ga itãciyar dawwama da mulki wanda bã ya ƙãrħwa?" [20.121] Sai suka ci daga gare ta, sabõda haka al´aurunsu suka bayyana, kuma suka shiga sunã lulluɓãwa a kansu daga ganyen Aljanna. Kuma Ãdamu ya sãɓã wa Ubangijinsa, sabõda haka ya ɓace. [20.122] Sa´an nan kuma Ubangjinsa Ya zãɓħ shi, Ya karɓi tũba gare shi, kuma Ya shiryar (da shi). [20.123] Ya ce: "Ku sauka kũ biyu daga gare ta gabã ɗaya, sãshenku yanã maƙiyi ga sãshe. To, imma dai wata shitiya ta jħ muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiryarwãta, to, bã ya ɓacħwa, kuma bã ya wahala." [20.124] "Kuma wanda ya bijire(3) daga ambatõNa (Alƙur´ãni) to, lalle ne rãyuwa mai ƙunci ta tabbata a gare shi, kuma Munã tãyar da shi a Rãnar Ƙiyãma yanã makãho." [20.125] Ya ce: "Ya Ubangiji! Don me Ka tãyar da ni makãho alhãli kuwa nã kasance mai gani?" [20.126] Ya ce: "Kamar wancan ne ãyõyinMu suka jħ maka sai ka mance su, kuma kamar hakar a yau ake mance ka." [20.127] Kuma kamar haka Muke sãka wa wanda ya yawaita,(1) kuma bai yi ĩmãni da ãyõyin Ubangijinsa ba. Kuma lalle ne azãbar Lãhira ce mafi tsanani, kuma mafi wanzuwa [20.128] Shin, to, bai shiryar da su ba cħwa da yawa Muka halakarda (kãfirai) daga ƙarnuka, a gabãninsu, sunã tafiya a cikin masaukansu? Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu hankula. [20.129] Kuma bã dõmin wata kalma ba wadda ta gabãta daga Ubangijinka, da kuma ajali ambatacce haƙĩƙa, dã azãbarta kasance mai lazimta. [20.130] Sai ka yi haƙuri(2) a kan abin da suke cħwa, kuma ka yi tasbĩhi da gõdħ wa Ubangijinka a gabãnin fitõwar rãnã da gabãnin ɓacħwarta, kuma daga sã´õ´in dare sai ka yi tasbĩhi da sãsannin yini, tsammãninka zã ka sãmi yarda. [20.131] Kuma kada ka mĩƙar da idãnunka zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi da shi, nau´i-nau´i daga gare su, kamar huren rãyuwar dũniya yake, dõmin Mu fitine su a cikinsa, alhãli kuwa arzikin Ubangijinka, ne mafi alhħri kuma mafi wanzuwa. [20.132] Kuma ka umurci iyãlanka da salla, kuma ka yi haƙuri a kanta. Bã Mu tambayar ka wani arziki Mu ne Muke azurta ka. Kuma ãƙiba mai kyau tanã ga taƙawa. [20.133] Kuma suka ce: "Don me bã ya zo mana da wata ãyã daga Ubangijinsa?" Shin, kuwa hujjar abin da ke a cikin littattafan farko, ba ta jħ musu ba? [20.134] Kuma dã dai Mun halaka sũ da wata azãba daga gabãninsa, lalle ne dã sun ce: "Yã Ubangijinmu! Dã Kã aiko da wani Manzo zuwa gare mu har mu bibiyi ãyõyinKa daga gabãnin mu ƙasƙanta, kuma mu wulãkantu!" [20.135] Ka ce: "Kõwa mai tsumãye ne. Sai ku yi tsumãye. Sa´an nan zã ku san su wa ne ma´abũta tafarki madaidaici, kuma wane ne ya nħmi shiryuwa." @AL ANBYAA' Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [21.1] Hisãbin mutãne ya kusanta gare su, ahãli kuwa sunã a cikin gafala, sunã mãsu bijirħwa. [21.2] Wani ambatõ daga Ubangijinsu sãbo, bã ya zuwa gare su fãce sun saurãre shi, alhãli kuwa sunã mãsu yin wãsa. [21.3] Sanã mãsu shagaltacin zukãtansu, kuma su asirta gãnãwa: Waɗanda suka yi zãlunce (sunã cħwa) "Wannan bã Kõwa ba ne fãce mutum misãlinku. Shin, to, kunã jħ wa sihiri, ahãli kuwa kũ, kunã fahimta?" [21.4] Ya ce: "Ubangijina Yanã sanin magana a cikin sama da ƙasa kuma Shi ne Mai ji, Masani." [21.5] ôa, suka ce: "Yãye-yãyen mafarki ne. ôa, yã ƙirƙira shi ne. ôa, shi mawãƙi ne. Sai ya zo mana da wata ãyã kamar yadda aka aiko manzanni na farko." [21.6] Wata alƙarya da Muka halaka ta a gabãninsu, ba ta yi ĩmãni ba. Shin, to, sũ, sunã yin ĩmãni? [21.7] Kuma ba Mu aika ba a gabãninka fãce mazãje, Munã yin wahayi zuwa gare su. Ku tambayi ma´abũta ambato(1) idan kun kasance ba ku sani ba. [21.8] Kuma ba Mu sanya su jiki, bã su cin abin ci ba, kuma ba su kasance madawwama ba. [21.9] Sa´an nan kuma Muka gaskata musu alkawari; sai Muka tsħrar da su da wanda Muke so, kuma Muka halakar da mãsu yawaitãwa.(2) [21.10] Lalle haƙĩƙa Mun saukar da wani littãfi zuwa gare ku,(3) a cikinsa akwai ambatonku. Shin, to, bã ku hankalta? [21.11] Kuma da yawa Muka karya wata alƙarya tã kasance mai zãlunci, kuma Muka ƙãga halittar waɗansu mutãne na dabam a bãyanta. [21.12] Sai a lõkacin da suka hangi azãbarMu, sai gã su sunã gudu daga gare ta. [21.13] "Kada ku yi gudu. Ku kõmo zuwa ga abin da aka ni´imtar da ku a cikinsa da gidãjenku tsammãninku anã tambayar ku." [21.14] Suka ce: "Kaitonmu! Lalle mũ ne muka kasance mãsu zãlunci." [21.15] Sa´an nan waccan ba ta gushe ba, ita ce da´awarsu har Muka mayar da su girbabbu, bitattu. [21.16] Kuma ba Mu halitta sama da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu Muna Mãsu wãsã ba. [21.17] Da Mun yi nufin Mu riƙi wani abin wãsa dã Mun(1) riƙe shi daga gunMu, idan Mun kasance mãsu aikatãwa. [21.18] ôa, Munã jĩfa da gaskiya a kan ƙarya, sai ta darkãke ta, sai ga tã halakakka. Kuma bone yã tabbata a gare ku sabõda abin da kuke siffantãwa. [21.19] Kuma shĩ ne da mallakar wanda yake a cikin sammai da ƙasa. Kuma waɗanda suke wurinSa (watau malã´iku), bã su yin girman kai ga ibãdarSa. kuma bã su gajiya. [21.20] Sunã tasbĩhi dare da rãnã, bã su yin rauni. [21.21] Kõ (kãfirai) sun riƙi waɗansu abũbuwan bautãwa ne ga ƙasã, su ne mãsu tãyarwa (gare su)? [21.22] Dã waɗansu abũbuwan bautawa sun kasance a cikinsu (sama da ƙasa) fãce Allah, haƙĩƙa dã su biyun sun ɓãci. Sabõda haka tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al´arshi daga abin da suke siffantãwa. [21.23] Bã a tambayar Sa ga abin da Yake aikatãwa, alhãli kuwa sũanã tambayar su. [21.24] Kõ sun riƙi waɗansu abũbuwan bautãwa baicinSa? Ka ce: "Ku kãwo hujjarku, wannan shi ne ambaton wanda yake tãre da ni, kuma shi ne ambaton wanda yake a gabãnĩna. ôa, mafi yawansubã su sanin gaskiya, sabõda haka sũ mãsu bijirħwa ne." [21.25] Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cħwa "Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa fãce Nĩ, sai ku bauta Mini." [21.26] Kuma suka ce: "Mai rahama ya riƙi ɗã." Tsarkinsa, ya tabbata! ôa, (malã´iku) bãyi ne mãsu daraja. [21.27] Bã su gabãtarSa da magana, kuma su da umurninSa suke aiki. [21.28] Yanã sanin abin da yake gaba gare su da abin da yake a bãyansu, kuma bã su yin cħto fãce ga wanda Ya yarda, kuma sũmasu sauna ne sabõda tsõronSa. [21.29] Kuma wanda ya ce daga gare su, "Lalle nĩ abin bautãwa ne baicinSa," to, wannan Munã sãkã masa da, Jahannama. Kamar haka Muke sãkã wa azzãlumai. [21.30] Shin kuma waɗanda suka kãfirta ba, su gani da cħwa lalle sammai da ƙasa sun kasance ɗinke,(1) sai Muka bũɗe su, kuma Muka sanya dukan kome mai rai daga ruwa? Shin, bã zã su yi ĩmãni ba? [21.31] Kuma Mun sanya tabbatattun duwãtsu a cikin ƙasa dõmin kada ta karkata da su kuma Mun sanya ranguna, hanyõyi, a cikinsu (duwãtsun), tsammãninsu sunã shiryuwa. [21.32] Kuma Mun sanya sama rufi tsararre, alhãli kuwa su daga ãyõyinta mãsu bijirħwa ne. [21.33] Kuma shĩ ne wanda Ya halitta dare da yini da rãnã da watã dukansu(2) a cikin wani sarari suKe iyo. [21.34] Kuma ba Mu sanya dawwama ga wani mutum ba, a gabãninka. Shin to idan ka mutu to sũ ne madawwama? [21.35] Kõwane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne. Kuma Munã jarraba ku da sharri da alhħri dõmin fitina. Kuma zuwa gare Mu ake mayar da ku. [21.36] Kuma idan waɗanda suka kãfirta suka gan ka, bã su riƙon ka fãce da izgili (sunã cħwa), "Shin, wannan ne ke ambatar gumãkanku?" Alhãli kuwa sũ, ga ambatar Mai rahama, mãsu kãfirta(1) ne. [21.37] An halitta mutum daga gaggãwa, zan nũna muku ãyõyiNa. Sabõda haka kada ku nħmiyin gaggãwa. [21.38] Kuma sunã cħwa, "A yaushe wannan wa´adi zai tabbata, idan kun kasance mãsu gaskiya?" [21.39] Dã waɗanda suka kãfirta sunã sanin lõkacin da bã su kange wuta daga fuskõkinsu, kuma haka daga bãyayyakinsu, alhãli kuwa ba su zama ana taimakon su ba. [21.40] ôa, tanã jħ musu bisa ga auke sai ta ɗimautar da su, sa´an nan bã su iya mayar da ita, kuma ba su zama anã yi musu jinkiri ba. [21.41] Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili ga waɗansu Manzanni daga gabãninka, sai abin da suka kasance sunã izgili da shi ya auku ga waɗanda suka yi izgilin daga gare su. [21.42] Ka ce: "Wãne ne yake tsare ku a dare da yini daga Mai rahama?" ôa, sũ mãsu bijirħwa ne daga ambaton Ubangijinsu. [21.43] Ko kuwa sunã da waɗansu abũbuwan bautãwa waɗanda ke tsare su, daga gare Mu? Bã su iya taimakon kansu kuma ba su kasance anã abũtar su(2) ba daga gareMu. [21.44] ôa, Mun yalwata wa waɗannan da ubanninsu ni´imarMu, har rãyuwa ta yi tsawo a kansu. Shin, to, bã su ganin cħwa lalle Mũ, Munã je wa ƙasarsu, Munã rage(3) ta daga sãsanninta? Shin, to, su ne marinjaya? [21.45] Ka ce: "Abin sani, inã yi muku gargaɗi kawai da wahayi," kuma kurma ba ya jin kira a lõkacin da ake yi musu gargaɗi. [21.46] Kuma haƙĩƙa idan wata iska daga azãbar Ubangiji ta shãfe su, haƙĩƙa sunã cħwa, "Yã kaitonmu! Lalle mũ ne muka kasance mãsu zãlunci." [21.47] Kuma Munã aza ma´aunan ãdalci ga Rãnar Ƙiyãma, sabõda haka ba a zãluntar rai da kõme. Kuma kõ dã ya kasance nauyin ƙwãya daga kõmayya ne Mun zo da ita. Kuma Mun isa zama Mãsu hisãbi. [21.48] Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun kãwo wa Mũsã da Hãrũna Rarrabewa da haske da ambato ga mãsu aiki da taƙawa. [21.49] Waɗanda suke tsãron Ubangijinsu a fake, alhãli kuwa sũ, mãsu sauna ne daga Sa´a. [21.50] Kuma wannan ambato ne mai albarka Mun saukar da shi. Shin, to, kũ mãsu musu ne gare shi? [21.51] Kuma lalle haƙĩƙa Mun kãwo wa Ibrãhĩm shiryuwarsa daga gabãni, kuma Mun kasance Masana gare shi. [21.52] Ya ce wa ubansa da mutanensa, "Mħne ne waɗannan mutummutumai waɗanda kuke mãsu lazimta a kansu?" [21.53] Suka ce: "Mun sãmi Ubanninmu mãsu lazimta a kansu." [21.54] Ya ce: "Lalle, haƙĩƙa, kun kasance kũ da Ubanninku a cikin ɓata bayyananna." [21.55] Suka ce: "Shin kã zo mana da gaskiya ne, Kõ kuwa kai kanã daga mãSu wãsã ne?" [21.56] Ya ce: "ôa, Ubangijinku Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa, wanda Ya ƙãga halittarsu. Kuma Ni inã daga mãsu shaida a kan haka." [21.57] "Kuma inã rantsuwa da Allah, lalle zan yi wani shiri ga gumãkanku a bãyan kun jũya kunã mãsu bãyar da bãya." [21.58] Sai ya sanya su guntu-guntu fãce wani babba gare su, tsammãninsũ sunã Kõmãwa zuwa gare shi. [21.59] Suka ce: "Wane ne ya aikata wannan ga gumãkanmu? Lalle shĩ, haƙĩƙa, yanã daga azzãlumai." [21.60] Suka ce: "Mun ji wani saurayi yanã ambatar su. Anã ce masa Ibrahĩm." [21.61] Suka ce: "To, ku zo da shi a kan idanun mutãne, tsammãnin su zã su bãyar da shaida." [21.62] Suka ce: "Shin kai ne ka aikata wannan ga gumãkanmu? Yã Ibrahĩm!" [21.63] Ya ce: "ôa, babbansu, wannan, shĩ ya aikata, shi. Sai ku tambaye su idan sun kasance sunã yin magana." [21.64] Sai suka kõma wa jũnansu suka ce: "Lalle ne kũ, kũ ne azzãlumai." [21.65] Sa´an nan kuma aka sunkuyar da su a kan kãwunansu (sukace,) "Lalle, haƙĩƙa, kã sani waɗannan bã su yin magana." [21.66] Ya ce: "Shin to, kunã bautã wa abin da, bã ya, amfãnin ku da Kõme kuma bã ya cũtar da ku baicin Allah?" [21.67] "Tir da ku, kuma da abin da kuke bauta wa, baicin Allah! Shin to, bã ku hankalta?" [21.68] Suka ce: "Ku ƙõne shi kuma ku taimaki gumãkanku, idan kun kasance mãsu aikatãwa." [21.69] Muka ce: "Yã wuta! Ki kasance sanyi da aminci ga Ibrahĩm." [21.70] Kuma suka yi nufin wani mũgun shiri da shi, sai Mukasanya su mafiya hasãra. [21.71] Kuma Muka tsħrar da shi da Lũɗu zuwa ga ƙasar nan wadda Muka sanya albarka a cikinta ga tãlikai. [21.72] Kuma Muka ba shi Is´haka da Ya´aƙuba a kan daɗi alhãli kuwa dukansu Mun sanya su sãlihai. [21.73] Kuma Muka sanya su shugabanni, sunã shiryarwa da umurninMu. Kuma Muka yi wahayi zuwa gare su da ayyukan alhħri da tsayar da salla da bãyar da zakka. Kuma sun kasance mãsu bauta gare Mu. [21.74] Kuma Lũɗu Mun bã shi hukunci da ilmi. Kuma Mun tsĩrar da shi daga alƙaryar nan wadda ke aikata mũnãnan ayyuka. Lallesũ, sun kasance mutãnen mũgun aiki, fãsiƙai. [21.75] Kuma Muka shigar da shi a cikin rahamarMu. Lalle ne shĩ, yanã daga sãlihai. [21.76] Kuma Nũhu, a sa´ad da ya yi kira a gabãni, sai Muka karɓa masa, sa´an nan Muka tsirar da shi da mutãnensa daga baƙin ciki mai girma. [21.77] Kuma Muka taimake shi daga mutãnen nan waɗanda suka ƙaryata da ãyõyinMu. Lalle ne sũ, sun kasance mutãnen mugun aiki. Sai Muka nutsar da su gabã ɗaya. [21.78] Kuma Dãwũda da Sulaimãn sa´ad da suke yin hukunci a cikin sha´anin shũka a lõkacin da tumãkin mutãne suka yi kiĩwon dare a cikinsa. Kuma Mun kasance Mãsu halarta ga hukuncinsu. [21.79] Sai Muka fahimtar da ita (mats´alar)(1) ga Sulaiman. Kuma dukansu Mun bã su hukunci da ilmi kuma Muka hõre duwatsu tãre da Dãwũda, sunã tasbĩhi, da tsuntsãye. Kuma Mun kasance Mãsu aikatãwa. [21.80] Kuma Muka sanar da shi sana´ar(2) wata tufa sabõda ku dõmin ya tsare ku daga makãminku. To, shin, ku mãsu gõdħwa ne? [21.81] Kuma (Muka hõre) wa Sulaimãn iska mai tsananin bugãwa, tanã gudãna da umuruinsa zuwa ga ƙasar nan wadda Muka sanya albarka a cikinta. Kuma Mun kasance Masana ga dukkan Kõme. [21.82] Kuma daga Shaiɗannu (Mun hõre) wanda ke nutso sabõda shi. Kuma sunã yin wani aiki baicin wancan. Kuma Mun kasance Mãsu tsaro a gare su. [21.83] Kuma da Ayyũba a sã´ad da ya yi kiran Ubangijinsa, (ya ce:) "Lalle nĩ, cũta ta shãfe ni, alhãli kuwa Kai ne Mafi rahamar mãsu rahama." [21.84] Sai Muka karɓa masa, sa´an nan Muka kuranye abin da ke a gare shi na cũta, kuma Muka kãwo masa mutãnesa da kwatank wacinsu tãre da su, sabõda rahama daga wurinMu da tunãtarwa(1) ga mãsu ibãda. [21.85] Kuma da Ismãĩla da Idrĩsa da Zulkifli, dukansu sunã daga mãsu haƙuri. [21.86] Kuma Muka shigar da su a cikin rahamarMu. Lalle ne, sunã daga sãlihai. [21.87] Kuma mai kifi(2) a sã´ad da ya tafi yanã mai hushi, sai ya yi zaton cħwa ba zã Mu ƙuƙunta masa ba. Sai ya yi kira a cikin duffai cħwa, "Bãbu abĩn bautãwa fãce Kai. Tsarki ya tabbata a gare Ka. Lalle ne nĩ, na kasance daga azzãlumai." [21.88] Sai Muka karɓa masa kuma Muka tsĩrar da shi daga baƙin ciki. Kamar haka ne Muke tsĩrarda masu ĩmãni. [21.89] Kuma da Zakariyya a sa´ad da ya kirãyi Ubangijinsa cħwa, "Ya Ubangiji! Kada Ka bar ni makaɗaici alhãli kuwa Kai ne Mafi alhħrin mãsu gãdo." [21.90] Sai Muka karɓa masa kuma Muka kyautata(3) masa mãtarsa. Lalle ne sũ, sun kasance sunã gudun tsħre zuwa ga ayyukan alhħri. Kuma sunã kiran Mu a kan kwaɗayi da fargaba. Kuma sun kasance mãsu saunar (aikata sãɓo) gare Mu. [21.91] Kuma da wadda ta tsare farJinta daga alfãsha. Sai Muka hũra a cikinta daga rũhinMu.(1) Kuma Muka sanya ta ita da ɗanta wata ãyã ga dũniya. [21.92] Lalle ne wannan(2) ita ce al´ummarku ta zama al´umma guda, kuma Nĩ ne Ubangijinku. Sai ku bauta Mini. [21.93] Kuma suka kakkãtse al´amarinsu a tsakaninsu. Dukan Kõwanensu mãsu Kõmõwa zuwa gare Ni [21.94] Dõmin wanda ya aikata daga ayyukan kwarai alhãli kuwa yanã mai ĩmãni, to, bãbu musu ga aikinsa, kuma Mu Mãsu rubũtãwa gare shi ne. [21.95] Kuma hananne ne a kan wata alƙarya da Muka halakar cħwa lalle sũ, bã su kõmõwa. [21.96] Har sa´ad da aka bũde Yãjũju da Mãjũju alhãli kuwa sunã gaggãwa daga kõwane tudun ƙasa. [21.97] Kuma wa´adin nan tabbatacce ya kusanto, sai gã ta idãnun waɗanda suka kãfirta sunã bayyanannu, (sunã cħwa), "Yã kaitonmu! Haƙĩƙa mun kasance a cikin gafala daga wannan! ôa, mun kasance dai mãsu zãlunci!" [21.98] (A ce musu) "Lalle ne, kũ da abin(3) da kuke bautãwa, baicin Allah makãmashin Jahannama ne. Kũ mãsu tusgãwa gare ta ne." [21.99] Dã waɗannan (abũbuwanbautãwar) sun kasance abũbuwan bautãwar gaskiya ne, dã ba su tusga mata ba, alhãli kuwa dukansu madawwama a cikinta ne. [21.100] Sunã da wata hargõwa a cikinta, alhãli kuwa sũ, a cikinta, bã su saurãren kõme. [21.101] Lalle ne waɗanda kalmar yabo tã gabãta a garħ su daga garħ Mu, waɗannan waɗanda ake nĩsantarwa daga barinta ne. [21.102] Bã su jin sautin mõtsinta alhãli kuwa sũ madawwamãne a cikin abin da rãyukansu suka yi marmarinsa. [21.103] Firgitar nan mafi girma, bã zã ta baƙantã musu rai ba. Kuma malã´iku na yi musu marãba (sunã cħwa) "Wannan yininku nħ wanda kuka kasance anã yi muku wa´adi da shi." [21.104] A rãnar da Muke naɗe sãma kamar neɗħwar takarda ga abũbuwan rubũtãwa kamar yadda Muka fãra a farKon(1) halitta Muke mãyar da ita. Wa´adi ne a Kanmu. Lalle ne Mun kasance Mãsu aikatãwa. [21.105] Kuma lalle haƙĩƙa Mun rubũta a cikin Littãfi baicin Ambato(2) (Lauhul Mahfũz) cħwa ƙasã, bayĩNa sãlihai, sunã gãdonta. [21.106] Lalle ne a cikin wannan (Alƙur´ãni), haƙĩƙa, akwai iyarwa (ga maganar da ta gabãta(3) ga waɗansu mutãne mãsu ibãda. [21.107] Kuma ba Mu aike ka ba fãce dõmin wata rahama ga talikai. [21.108] Ka ce: "Abin sani kawai, anã yin wahayi zuwa gare ni ne, cħwa, lalle ne, Abin bautãwarku, Abin bautãwa ne Guda. To shin kũ mãsu mĩƙa wuya ne?" [21.109] Sa´an nan idan suka jũya, to, ka ce: "Nã sanar da ku, a kan daidaita, kuma ban sani ba, shin, abin da ake yi muku wa´adi makusanci ne Kõ kuwa manĩsanci?" [21.110] "Lalle ne Shĩ (Allah) Yanã sanin bayyane daga magana, kuma Yanã sanin abin da kuke ɓõyħwa. [21.111] "Kuma ban sani ba, tsammãninsa ya zama fitina a gare ku, kõ kuma don jin dãɗi, zuwa ga wani ɗan lõkaci." [21.112] Ya ce: "Yã Ubangiji! Ka yi hukunci da gaskiya. Kuma Ubangijinmu Mai rahama ne Wanda ake nħman taimakonSa a kan abinda kuke siffantãwa." @AL HAJJ Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. [22.1] Yã ku mutãne! Ku bi Ubangijinku da taƙawa. Lalle ne girgizar(1) ƙasa ta tsayuwar Sa´a wata aba ce mai girma. [22.2] A rãnar da kuke ganin ta dukan mai shãyar da mãma tanã shagala daga abin da ta shãyar, kuma dukan mai ciki tanã haihuwar cikinta, kuma kanã ganin mutãne sunã mãsu mãyħ alhãli kuwa su bã mãsu mãye ba, amma azãbar Allah ce mai tsanani. [22.3] Akwai daga mutãne(2) wanda yake yin musũ ga sha´anin Allah bã da wani ilmi ba, kuma yanã biyar kõwane Shaiɗan mai taurin kai. [22.4] An wajabta masa cħwa wanda ya jiɓince shi, to, lalle ne sai ya ɓatar da shi, kuma ya shiryar da shi zuwa ga azãbar sa´ĩr. [22.5] Ya ku mutãne! Idan kun kasance a cikin shakka a Tãshin Ƙiyãma, to, lalle ne Mũ, Man halittaku daga turɓaya, sa´an nan kuma daga gudãjin jini, sa´an nan kuma daga taõka wadda ake halittãwa da wadda ba a halittawa dõmin, Mu bayyana muku. Kuma Munã tab batar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sa´an nan kuma Munã fitar da ku kunã jãrĩri, sa´an nan kuma dõmin ku kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rãyuwa dõmin kada ya san kõme a bãyan ya sani. Kuma kanã ganin ƙasa shiru, sa´an nan idan Muka saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kõwane nau´i mai ban sha´awa. [22.6] Wancan ne dõmin lalle Allah Shi ne Gaskiya, kuma lalle ne shi Yake rãyar da matattu, kuma lalle Shi Mai ikon yi ne a kan kõme. [22.7] Kuma lalle ne Sa´ar Tãshin Ƙiyãma mai zuwa ce, bãbu shakka a cikinta kuma lalle ne Allah Yanã tãyar da waɗanda suke a cikin ƙaburbura. [22.8] Kuma daga mutãne akwai mai yin musu(1) ga Allah bã da wani ilmi ba kuma bã da wata shiriya ba, kuma bã da wani littãfi mai haskakãwa ba. [22.9] Yanã mai karkatar da sãshensa dõmin ya ɓatar (da wasu) daga tafarkin Allah! Yanã da wani wulãkanci a dũniya, kuma Munã ɗanɗana masa azãbar gõbara a Rãnar Ƙiyãma. [22.10] (A ce masa): "Wancan azaba sabõda abin da hannayenka biyu suka gabatar ne, kuma lalle ne Allah bai zama Mai zãlunci ga bãyinSa ba." [22.11] Kuma daga mutãne akwai mai bauta(2) wa Allah a kan wani gefe. Sa´an nan idan wani alhħri ya sãme shi, sai ya natsu da shi, kuma idan wata fitina ta sãme shi, sai ya jũya bãya a kan fuskarsa. Yã yi hasãrar dũniya da Lãhira. Waccan ita ce hasãra bayyananna. [22.12] Yanã kiran baicin Allah, abin da bã ya cũtarsa da abin da bã ya amfãninsa! waccan ita ce ɓata mai nĩsa. [22.13] Yanã kiran wanda yake lalle cũtarwarsa ce mafi kusa daga amfãninsa! Lalle ne, tir da shi ya zama majiɓinci, kuma tir da ya zama abõkin zama! [22.14] Lalle ne Allah Yanã shigar da waɗanda suka yi ĩmãni(3) kuma suka aikata ayyukan ƙwarai a cikin gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashinsu. Lalle ne Allah Yanã aikata abin da Yake nufi. [22.15] Wanda ya kasance yanã zaton cħwa Allah bã zai taimake shi(4) ba a cikin dũniya da Lãhira to sai ya mĩƙa wata igiya zuwa sama, sa´an nan kuma ya yanke ta, sa´an nan ya dũba. Shin, ko lalle kaidinsa zai gusar da abin da yake ji na takaici? [22.16] Kuma kamar haka Muka saukar da shi (Alƙur´ãni) yanã ãyõyi bayyanannu. Kuma lalle ne Allah Yanã shiryar da wanda Yake nufi. [22.17] Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni da waɗanda suka tũba(1) (Yahũdu) da waɗanda suka karkace (Saba´ãwa) da Nasãra da Majũsãwa da waɗanda suka yi shirka, lalle ne Allah Yanã yin hukunci a tsakãninsu a Ranãr Ƙiyãma.Lalle ne Allah Mahalarci ne a kan dukkan kõme. [22.18] Ashe, ba ka gani ba, lalle Allah, wanda yake a cikin sammai da wanda yake a cikin ƙasa yanã yin sujada a gare shi, da kuma rãna da watã da taurãri da duwãtsu da itãce da dabbõbi, da kuma mãsu yawa daga mutãne? Kuma waɗansu mãsu yawa azãba tã tabbata a kansu. Kuma wanda Allah Ya wulãkantar, to, bã ya da wani mai girmamãwa. Kuma Lalle ne Allah Yanã aikata abin da Yake so. [22.19] waɗannan ƙungiyõyi biyu(2) ne mãsu husũma, sun yi husũma ga sha´anin Ubangijinsu. To, waɗanda suka kãfirta an yanka musu waɗansu tufafi daga wata irin wuta, anã zuba tafasasshen ruwa daga bisa kãwunansu. [22.20] Da shĩ ake narkar da abin da yake a cikin cikunansu da fãtun jikinsu. [22.21] Kuma sunã da waɗansu gwalmõmin dũka na baƙin ƙarfe. [22.22] A kõyaushe suka yi nufin fita daga gare ta, daga baƙin ciki, sai a mayar da su a cikinta, (a ce musu) "Ku ɗanɗani azãbar gõbara." [22.23] Lalle ne, Allah Yana shigar da waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai a cikin gidãjen Aljanna, ƙoramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, anã ƙawãta su, a cikinsu, da waɗansu mundãye na zĩnãri da lu´u-lu´u. Kuma tufãfinsu a cikinsu alharĩni ne.(3) [22.24] Kuma an shiryar da su zuwa ga mai kyau na zance kuma an shiryar da su zuwa ga, hanyar wanda ake gode wa. [22.25] Lalle ne waɗanda suka kãfirta kuma suka taushe (mutãne) daga hanyar Allah da masallaci mai alfarma wanda Muka sanya shi ga mutãne alhãli kuwa mazauni a ciki da baƙauye daidai suke kuma wanda ya yi nufin karkatar(1) da gaskiya a cikinsa da zãlunci zã Mu ɗanɗana masa daga wata azãba mai raɗadi. [2